< 2 Tarihi 1 >

1 Solomon ɗan Dawuda ya kafa kansa sosai a bisa masarautarsa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi ya kuma sa ya zama mai girma sosai.
Et Salomon, fils de David, s’affermit dans son royaume; et l’Éternel, son Dieu, fut avec lui et l’agrandit extrêmement.
2 Sai Solomon ya yi magana ga dukan Isra’ila, ga shugabannin mayaƙa dubu-dubu da shugabannin mayaƙa ɗari-ɗari, ga alƙalai da kuma ga dukan shugabanni a Isra’ila, kawunan iyalai,
Et Salomon parla à tout Israël, aux chefs de milliers et de centaines, et aux juges, et à tous les princes de tout Israël, chefs des pères;
3 Solomon tare da dukan taron suka tafi masujadan kan tudu a Gibeyon, gama Tentin Sujadar Allah yana can, wanda Musa bawan Ubangiji ya yi a hamada.
et Salomon, et toute la congrégation avec lui, allèrent au haut lieu qui était à Gabaon; car là était la tente d’assignation de Dieu, que Moïse, serviteur de l’Éternel, avait faite dans le désert
4 Dawuda ya riga ya haura da akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim zuwa inda ya shirya dominsa, domin yă kafa masa tenti a Urushalima.
(mais David avait fait monter l’arche de Dieu de Kiriath-Jéarim au [lieu] que David lui avait préparé; car il lui avait tendu une tente à Jérusalem);
5 Amma bagaden tagullar da Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, ya yi a Gibeyon a gaba tabanakul na Ubangiji; saboda haka Solomon da taron suka neme nufin Ubangiji a can.
et l’autel d’airain qu’avait fait Betsaleël, fils d’Uri, fils de Hur, était là, devant le tabernacle de l’Éternel; et Salomon et la congrégation la recherchèrent.
6 Solomon ya haura zuwa bagaden tagulla a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada, ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa dubbai a kansa.
Et Salomon offrit là, devant l’Éternel, sur l’autel d’airain qui était devant la tente d’assignation; il offrit 1 000 holocaustes sur cet [autel].
7 A wannan dare Allah ya bayyana ga Solomon, ya ce masa, “Roƙi duk abin da kake so in ba ka.”
Cette même nuit Dieu apparut à Salomon, et lui dit: Demande ce que tu veux que je te donne.
8 Solomon ya amsa wa Allah, “Ka nuna alheri mai girma ga Dawuda mahaifina ka kuma naɗa ni sarki a matsayinsa.
Et Salomon dit à Dieu: Tu as usé d’une grande bonté envers David, mon père, et tu m’as fait roi à sa place:
9 To, yanzu, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi ga mahaifina Dawuda yă tabbata, gama ka naɗa ni sarki a bisa mutanen da suka wuce ƙirge kamar ƙurar ƙasa.
maintenant, Éternel Dieu, que ta parole à David, mon père, soit ferme; car tu m’as établi roi sur un peuple nombreux comme la poussière de la terre:
10 Ka ba ni hikima da sani, don in iya jagorance wannan mutane, gama wa zai iya shugabance wannan jama’arka mai girma?”
maintenant, donne-moi de la sagesse et de la connaissance, et je sortirai et j’entrerai devant ce peuple; car qui jugera ton peuple qui est si grand?
11 Allah ya ce wa Solomon, “Da yake wannan ne sha’awar zuciyarka, ba ka kuwa nemi wadata, arziki ko girma ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, da yake kuma ba ka nemi tsawon rai ba, amma ka nemi hikima da sani don ka shugabanci jama’ata wadda na naɗa ka sarki,
Et Dieu dit à Salomon: Parce que c’est cela qui était dans ton cœur, et que tu n’as pas demandé des richesses, des biens, et de la gloire, ni la vie de ceux qui te haïssent, et que tu n’as pas non plus demandé de longs jours, mais que tu as demandé pour toi de la sagesse et de la connaissance afin de pouvoir juger mon peuple sur lequel je t’ai établi roi,
12 saboda haka za a ba ka hikima da sani. Zan kuma ba ka wadata, arziki da girma, waɗanda babu wani sarki kafin kai da ya taɓa kasance da su kuma babu wani a bayanka da zai kasance da su.”
la sagesse et la connaissance te sont données; et je te donnerai des richesses, et des biens, et de la gloire, comme n’en ont pas eu les rois qui ont été avant toi, et comme après toi aucun n’en aura.
13 Sa’an nan Solomon ya tafi Urushalima daga masujadar kan tudu a Gibeyon, da kuma daga gaban Tentin Sujada. Ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila.
Et Salomon revint à Jérusalem, du haut lieu qui était à Gabaon, de devant la tente d’assignation, et il régna sur Israël.
14 Solomon ya tara kekunan yaƙi da dawakai, ya kasance da kekunan yaƙi dubu da ɗari huɗu da kuma dawakai dubu goma sha biyu, waɗanda ya ajiye a biranen kekunan yaƙi, da kuma tare da shi a Urushalima.
Et Salomon rassembla des chars et des cavaliers; et il eut 1 400 chars et 12 000 cavaliers; et il les plaça dans les villes à chars, et auprès du roi à Jérusalem.
15 Sarki ya sa azurfa da zinariya suka zama barkatai a Urushalima kamar duwatsu, al’ul kuma kamar itatuwan fir a gindin tsaunuka.
Et le roi fit que l’argent et l’or, dans Jérusalem, étaient comme les pierres, et il fit que les cèdres étaient, en quantité, comme les sycomores qui sont dans le pays plat.
16 Aka shigo da dawakan Solomon daga Masar da kuma daga Kuye’yan kasuwan fada suka saye su daga Kuye.
Et quant aux chevaux de Salomon, il les tirait d’Égypte: une caravane de marchands du roi prenait un convoi [de chevaux] pour un certain prix;
17 Suka shigo da kekunan yaƙi daga Masar a kan shekel ɗari shida-shida na azurfa, doki kuma a kan shekel ɗari da hamsin-hamsin. Suka kuma riƙa fitar da su ƙasashen waje zuwa dukan sarakunan Hittiyawa da na Arameyawa.
et on faisait monter et sortir d’Égypte un char pour 600 [sicles] d’argent, et un cheval pour 150; et on en faisait venir ainsi, par leur main, pour tous les rois des Héthiens et pour les rois de Syrie.

< 2 Tarihi 1 >