< 2 Tarihi 1 >

1 Solomon ɗan Dawuda ya kafa kansa sosai a bisa masarautarsa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi ya kuma sa ya zama mai girma sosai.
Therfor Salomon, the sone of Dauid, was coumfortid in his rewme, and the Lord was with hym, and magnefiede hym an hiy.
2 Sai Solomon ya yi magana ga dukan Isra’ila, ga shugabannin mayaƙa dubu-dubu da shugabannin mayaƙa ɗari-ɗari, ga alƙalai da kuma ga dukan shugabanni a Isra’ila, kawunan iyalai,
And Salomon comaundide to al Israel, to tribunes, and centuriouns, and to duykis, and domesmen of al Israel, and to the princes of meynees;
3 Solomon tare da dukan taron suka tafi masujadan kan tudu a Gibeyon, gama Tentin Sujadar Allah yana can, wanda Musa bawan Ubangiji ya yi a hamada.
and he yede with al the multitude in to the hiy place of Gabaon, where the tabernacle of boond of pees of the Lord was, which tabernacle Moyses, the seruaunt of the Lord, made in wildirnesse.
4 Dawuda ya riga ya haura da akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim zuwa inda ya shirya dominsa, domin yă kafa masa tenti a Urushalima.
Forsothe Dauid hadde brouyt the arke of God fro Cariathiarym in to the place which he hadde maad redy to it, and where he hadde set a tabernacle to it, that is, in to Jerusalem.
5 Amma bagaden tagullar da Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, ya yi a Gibeyon a gaba tabanakul na Ubangiji; saboda haka Solomon da taron suka neme nufin Ubangiji a can.
And the brasun auter, which Beseleel, the sone of Vri, sone of Vr, hadde maad, was there bifor the tabernacle of the Lord; whiche also Salomon and al the chirche souyte.
6 Solomon ya haura zuwa bagaden tagulla a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada, ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa dubbai a kansa.
And Salomon stiede to the brasun autir, bifor the tabernacle of boond of pees of the Lord, and offride in it a thousynde sacrifices.
7 A wannan dare Allah ya bayyana ga Solomon, ya ce masa, “Roƙi duk abin da kake so in ba ka.”
Lo! `forsothe in that nyyt God apperide to hym, `and seide, Axe that that thou wolt, that Y yyue to thee.
8 Solomon ya amsa wa Allah, “Ka nuna alheri mai girma ga Dawuda mahaifina ka kuma naɗa ni sarki a matsayinsa.
And Salomon seide to God, Thou hast do greet mersi with Dauid, my fadir, and hast ordeyned me kyng for hym.
9 To, yanzu, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi ga mahaifina Dawuda yă tabbata, gama ka naɗa ni sarki a bisa mutanen da suka wuce ƙirge kamar ƙurar ƙasa.
Now therfor, Lord God, thi word be fillid, which thou bihiytist to Dauid, my fadir; for thou hast maad me kyng on thi greet puple, which is so vnnoumbrable as the dust of erthe.
10 Ka ba ni hikima da sani, don in iya jagorance wannan mutane, gama wa zai iya shugabance wannan jama’arka mai girma?”
Yiue thou to me wisdom and vndurstondyng, that Y go in and go out bifor thi puple; for who may deme worthili this thi puple, which is so greet?
11 Allah ya ce wa Solomon, “Da yake wannan ne sha’awar zuciyarka, ba ka kuwa nemi wadata, arziki ko girma ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, da yake kuma ba ka nemi tsawon rai ba, amma ka nemi hikima da sani don ka shugabanci jama’ata wadda na naɗa ka sarki,
Sotheli God seide to Salomon, For this thing pleside more thin herte, and thou axidist not richessis, and catel, and glorie, nether the lyues of them that hatiden thee, but nether ful many daies of lijf; but thou axidist wisdom and kunnyng, that thou maist deme my puple, on which Y ordeynede thee kyng,
12 saboda haka za a ba ka hikima da sani. Zan kuma ba ka wadata, arziki da girma, waɗanda babu wani sarki kafin kai da ya taɓa kasance da su kuma babu wani a bayanka da zai kasance da su.”
wisdom and kunnyng ben youun to thee; forsothe Y schal yyue to thee richessis, and catel, and glorie, so that noon among kyngis, nether bifor thee nethir aftir thee, be lijk thee.
13 Sa’an nan Solomon ya tafi Urushalima daga masujadar kan tudu a Gibeyon, da kuma daga gaban Tentin Sujada. Ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila.
Therfor Salomon cam fro the hiy place of Gabaon in to Jerusalem, bifor the tabernacle of boond of pees, and he regnede on Israel.
14 Solomon ya tara kekunan yaƙi da dawakai, ya kasance da kekunan yaƙi dubu da ɗari huɗu da kuma dawakai dubu goma sha biyu, waɗanda ya ajiye a biranen kekunan yaƙi, da kuma tare da shi a Urushalima.
And he gaderide to hym chaaris and knyytis, and a thousynde and foure hundrid charis weren maad to hym, and twelue thousynde of knyytis; and he made hem to be in the citees of cartis, and with the kyng in Jerusalem.
15 Sarki ya sa azurfa da zinariya suka zama barkatai a Urushalima kamar duwatsu, al’ul kuma kamar itatuwan fir a gindin tsaunuka.
And the kyng yaf in Jerusalem gold and siluer as stoonys, and cedris as sicomoris, that comen forth in feeldi places in greet multitude.
16 Aka shigo da dawakan Solomon daga Masar da kuma daga Kuye’yan kasuwan fada suka saye su daga Kuye.
Forsothe horsis weren brouyt to hym fro Egipt, and fro Choa, bi the marchauntis of the kyng, whiche yeden, and bouyten bi prijs,
17 Suka shigo da kekunan yaƙi daga Masar a kan shekel ɗari shida-shida na azurfa, doki kuma a kan shekel ɗari da hamsin-hamsin. Suka kuma riƙa fitar da su ƙasashen waje zuwa dukan sarakunan Hittiyawa da na Arameyawa.
`a foure `horsid carte for sixe hundrid platis of siluer, and an hors for an hundrid and fifti. In lijk maner biyng was maad of alle the rewmes of citees, and of the kingis of Sirie.

< 2 Tarihi 1 >