< 2 Tarihi 1 >

1 Solomon ɗan Dawuda ya kafa kansa sosai a bisa masarautarsa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi ya kuma sa ya zama mai girma sosai.
David’s son [King] Solomon was able to gain complete control over his kingdom, because Yahweh his God helped him and enabled him to become very powerful.
2 Sai Solomon ya yi magana ga dukan Isra’ila, ga shugabannin mayaƙa dubu-dubu da shugabannin mayaƙa ɗari-ɗari, ga alƙalai da kuma ga dukan shugabanni a Isra’ila, kawunan iyalai,
[When] David [was king, he had arranged for a new] Sacred Tent [to be] made in Jerusalem. Then David [and the Israeli leaders] had brought God’s Sacred Chest from Kiriath-Jearim [city] to the new Sacred Tent in Jerusalem that he had prepared for it. But [when Solomon became the king, ] the first Sacred Tent was still at Gibeon [city]. That was the tent that Moses, the man who served God [well], had [arranged to be] made in the desert. And the bronze altar that Bezalel, the son of Uri and grandson of Hur, had made was also still in Gibeon, in front of the first Sacred Tent. [One day] Solomon summoned the army commanders of 1,000 soldiers and the commanders of 100 soldiers and the judges and all the other leaders in Israel. He told them to go with him to Gibeon. So they all went to a hill in Gibeon [where the Sacred Tent was], and Solomon and all the others with him worshiped Yahweh there.
3 Solomon tare da dukan taron suka tafi masujadan kan tudu a Gibeyon, gama Tentin Sujadar Allah yana can, wanda Musa bawan Ubangiji ya yi a hamada.
4 Dawuda ya riga ya haura da akwatin alkawarin Allah daga Kiriyat Yeyarim zuwa inda ya shirya dominsa, domin yă kafa masa tenti a Urushalima.
5 Amma bagaden tagullar da Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, ya yi a Gibeyon a gaba tabanakul na Ubangiji; saboda haka Solomon da taron suka neme nufin Ubangiji a can.
6 Solomon ya haura zuwa bagaden tagulla a gaban Ubangiji a cikin Tentin Sujada, ya kuma miƙa hadayu na ƙonawa dubbai a kansa.
Then Solomon went up to the bronze altar in front of the Sacred Tent, and he offered 1,000 animals to be [killed and] completely burned [on the altar].
7 A wannan dare Allah ya bayyana ga Solomon, ya ce masa, “Roƙi duk abin da kake so in ba ka.”
That night God appeared to Solomon [in a dream] and said to him, “Request whatever you want me to give to you.”
8 Solomon ya amsa wa Allah, “Ka nuna alheri mai girma ga Dawuda mahaifina ka kuma naɗa ni sarki a matsayinsa.
Solomon replied, “You were very kind to David my father, and now you have appointed me to be the king to succeed him.
9 To, yanzu, ya Ubangiji Allah, ka cika alkawarin da ka yi ga mahaifina Dawuda yă tabbata, gama ka naɗa ni sarki a bisa mutanen da suka wuce ƙirge kamar ƙurar ƙasa.
So Yahweh my God, you have caused me to become the king to rule people who are as many as the particles of dirt on the earth. So do what you promised my father David.
10 Ka ba ni hikima da sani, don in iya jagorance wannan mutane, gama wa zai iya shugabance wannan jama’arka mai girma?”
Please enable me to be wise and to know [what I should do], in order that I may rule these people [well], because there is no one who can rule all this great nation of yours [without your help].”
11 Allah ya ce wa Solomon, “Da yake wannan ne sha’awar zuciyarka, ba ka kuwa nemi wadata, arziki ko girma ba, ba ka kuma nemi mutuwar abokan gābanka ba, da yake kuma ba ka nemi tsawon rai ba, amma ka nemi hikima da sani don ka shugabanci jama’ata wadda na naɗa ka sarki,
God replied, “[I am pleased with what] you desire; you have not requested a huge amount of money or to be honored or that your enemies be killed. And you have not requested that you live for a long time. Instead, you have requested that [I enable] you [to] be wise and [to] know [what you should do] in order that you may govern [well] my people whom I have appointed you to rule.
12 saboda haka za a ba ka hikima da sani. Zan kuma ba ka wadata, arziki da girma, waɗanda babu wani sarki kafin kai da ya taɓa kasance da su kuma babu wani a bayanka da zai kasance da su.”
Therefore I will enable you to be wise and to know [what you should do to rule my people well]. But I will also enable you to have a huge amount of money and to be honored, more than anyone who was previously a king ever was honored, more than anyone who later becomes king will be honored.”
13 Sa’an nan Solomon ya tafi Urushalima daga masujadar kan tudu a Gibeyon, da kuma daga gaban Tentin Sujada. Ya kuma yi mulki a bisa Isra’ila.
Then Solomon [and the people who were with him all] left from being in front of he Sacred Tent [on the hill in Gibeon], and they returned to Jerusalem. From there he ruled the Israeli people.
14 Solomon ya tara kekunan yaƙi da dawakai, ya kasance da kekunan yaƙi dubu da ɗari huɗu da kuma dawakai dubu goma sha biyu, waɗanda ya ajiye a biranen kekunan yaƙi, da kuma tare da shi a Urushalima.
Solomon acquired 1,400 chariots and 12,000 men who rode [on horses]. He put some of the chariots and horses in Jerusalem, and put some of them in various other cities.
15 Sarki ya sa azurfa da zinariya suka zama barkatai a Urushalima kamar duwatsu, al’ul kuma kamar itatuwan fir a gindin tsaunuka.
During the years that Solomon was king, silver and gold were as common in Jerusalem as stones, and [lumber from] cedar trees were as plentiful as [lumber from] ordinary sycamore trees in the foothills.
16 Aka shigo da dawakan Solomon daga Masar da kuma daga Kuye’yan kasuwan fada suka saye su daga Kuye.
Solomon’s horses were imported/brought from Egypt and from [the] Kue [region in Turkey].
17 Suka shigo da kekunan yaƙi daga Masar a kan shekel ɗari shida-shida na azurfa, doki kuma a kan shekel ɗari da hamsin-hamsin. Suka kuma riƙa fitar da su ƙasashen waje zuwa dukan sarakunan Hittiyawa da na Arameyawa.
In Egypt his men paid 15 pounds of silver for each chariot and 3-3/4 pounds of silver for each horse. They also exported/sold many of them to the kings of the Heth and Aram people-groups.

< 2 Tarihi 1 >