< 2 Tarihi 9 >

1 Sa’ad da sarauniyar Sheba ta ji shahararr Solomon, sai ta zo Urushalima tă gwada shi da tambayoyi masu wuya. Ta iso tare da ayari mai girma, da raƙuma ɗauke da kayan yaji, zinariya mai yawa, da kuma duwatsu masu daraja, ta zo wurin Solomon ta kuma yi magana da shi game da dukan abin da yake zuciyarta.
Da dronningen av Saba hørte Salomos ry, kom hun til Jerusalem med et stort følge og med kameler som bar krydderier og gull i mengde og dyre stener; hun vilde sette Salomo på prøve med gåter. Og da hun var kommet til ham, talte hun med ham om alt som lå henne på hjerte.
2 Solomon ya amsa dukan tambayoyinta; babu wani abin da ya yi masa wuya yă bayyana mata.
Men Salomo tydet alle hennes gåter; det var ikke et ord av det hun sa, som var dulgt for Salomo, så han ikke kunde tyde det.
3 Sa’ad da sarauniyar Sheba ta ga hikimar Solomon da kuma fadan da ya gina,
Da dronningen av Saba så Salomos visdom og så det hus han hadde bygget,
4 ta ga abincin da yake teburinsa, ta ga zaman fadawansa, bayi masu yin masa hidima cikin rigunansu, ta ga masu riƙe kwaf cikin rigunansu da kuma hadayun ƙonawar da ya yi a haikalin Ubangiji, sai mamaki ya kama ta.
og rettene på hans bord, og hvorledes hans tjenere satt ved bordet, og bordsvennene stod omkring, og hvorledes de var klædd, og hans munnskjenker og deres drakt og den trapp han gikk op på til Herrens hus, var hun rent ute av sig selv av forundring.
5 Ta ce wa sarki, “Labarin da na ji a ƙasata game da nasarorinka da hikimarka, gaskiya ne.
Og hun sa til kongen: Så var det da sant det jeg hørte hjemme i mitt land om dig og din visdom.
6 Amma ban gaskata abin da suka faɗa ba sai da na zo na kuma gani da idanuna. Tabbatacce, ko rabin girman hikimarka ba a faɗa mini ba, ka wuce labarin da na ji nesa ba kusa ba.
Jeg trodde ikke det de fortalte, før jeg kom og fikk se det med egne øine; men nu ser jeg at de ikke har fortalt mig halvdelen om din store visdom; du overgår det rykte jeg har hørt.
7 Abin farin ciki ne ga mutanenka! Abin farin ciki ne ga fadawanka, waɗanda suke cin gaba da tsayawa a gabanka suna kuma jin hikimarka!
Lykkelige er dine menn og lykkelige disse dine tjenere som alltid står for ditt åsyn og hører din visdom.
8 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka, wanda ya ji daɗi a cikinka ya sa ka a kan kujerar sarautarsa a matsayin sarki don ka yi mulkin domin Ubangiji Allahnka. Saboda ƙaunar Allahnka wa Isra’ila da kuma sha’awarsa na riƙe su har abada, ya naɗa ka sarki a bisansu, don ka yi adalci da kuma gaskiya.”
Lovet være Herren din Gud, som hadde velbehag i dig, så han satte dig på sin trone som konge for Herren din Gud! Fordi din Gud elsker Israel og vil holde det oppe til evig tid, satte han dig til konge over dem for å håndheve rett og rettferdighet.
9 Sa’an nan ta ba sarki talenti 120 na zinariya, kayan yaji masu yawa, da kuma duwatsu masu daraja. Ba a taɓa kasance da irin kayan yaji mai yawa kamar waɗanda sarauniyar Sheba ta ba wa sarki Solomon ba.
Så gav hun kongen hundre og tyve talenter gull og krydderier i stor mengde og dyre stener; aldri har det vært slik mengde krydderier i landet som det dronningen av Saba gav kong Salomo.
10 (Mutanen Hiram da mutanen Solomon suka kawo zinariya daga Ofir, suka kuma kawo gungumen algum da duwatsu masu daraja.
Men også Hirams folk og Salomos folk som hentet gull fra Ofir, hadde ført sandeltre og dyre stener med derfra.
11 Sarki ya yi amfani da gungumen algum don matakalan haikalin Ubangiji da kuma na fadan sarki, ya kuma yi garayu da molaye don mawaƙa. Ba a taɓa gani irinsu a Yahuda ba.)
Av sandeltreet lot kongen gjøre trapper til Herrens hus og til kongens hus og citarer og harper for sangerne; maken til det var aldri før blitt sett i Juda land.
12 Sarki Solomon ya ba sarauniyar Sheba duk abin da take so da kuma ta nema; ya ba ta fiye da abin da ta kawo masa. Sa’an nan ta tashi ta koma ƙasarta tare da masu rufe mata baya.
Og kong Salomo gav dronningen av Saba alt det hun hadde lyst til og bad om, foruten det han gav til gjengjeld for det hun hadde hatt med til kongen. Så tok hun avsted og drog hjem til sitt land med sine tjenere.
13 Nauyin zinariyar da Solomon yake karɓa shekara-shekara talenti 666 ne,
Vekten av det gull som i ett år kom inn til Salomo, var seks hundre og seks og seksti talenter,
14 ban da harajin da fatakai da’yan kasuwa suke biya. Haka kuma dukan sarakunan Arabiya da gwamnonin ƙasar suka kawo zinariya da azurfa wa Solomon.
foruten det som kom inn fra kjøbmennene og kremmerne; også alle kongene i Arabia og stattholderne i landet avgav gull og sølv til Salomo.
15 Sarki Solomon ya yi manyan garkuwoyi ɗari biyu da zinariya; an yi kowane garkuwa da bekas ɗari shida na zinariya.
Og kong Salomo lot gjøre to hundre store skjold av uthamret gull - det gikk seks hundre sekel uthamret gull med til hvert skjold -
16 Ya kuma yi ƙanana garkuwoyi zinariya ɗari uku, da bekas ɗari uku na zinariya a kowanne. Sarki ya sa su a cikin Fadan da ake kira Kurmin Lebanon.
Og tre hundre små skjold av uthamret gull - til hvert av disse skjold gikk det med tre hundre sekel gull - og kongen satte dem i Libanon-skoghuset.
17 Sai sarki ya yi wata kujerar sarauta mai girma da aka shafe ta da hauren giwa, aka kuma dalaye ta da zinariya zalla.
Kongen lot også gjøre en stor elfenbenstrone og klædde den med rent gull.
18 Kujerar tana da matakalai shida, da wurin sa ƙafa na zinariya haɗe da ita. A kowane gefen wurin zama, akwai wurin ajiye hannu, da zaki tsaye kusa da kowannensu.
Tronen hadde seks trin og en fotskammel av gull, som var fastgjort til tronen; på begge sider av setet var det armer, og tett ved armene stod det to løver;
19 Zakoki goma sha biyu sun tsaya a kan matakalai shida, ɗaya a ƙarshen matakala guda. Ba a taɓa yin irin wannan abu don wata masarauta ba.
og på begge sider av de seks trin stod det tolv løver. Noget sådant har aldri vært gjort i noget annet kongerike.
20 Dukan kwaf na Sarki Solomon zinariya ne, kuma dukan kayayyakin gida a Fadan da ake kira Kurmin Lebanon zinariya ne zalla. Ba a yi wani abu da azurfa ba, domin ba a ɗauki azurfa a zamanin Solomon a bakin kome ba.
Alle kong Salomos drikkekar var av gull, og alle karene i Libanonskoghuset var av fint gull; sølv blev ikke regnet for noget i Salomos dager.
21 Sarki yana da jerin jiragen ruwa na kasuwanci waɗanda mutanen Hiram ne suke kula da su. Sau ɗaya kowace shekara uku sukan dawo ɗauke da zinariya, azurfa, hauren giwa, gogo da kuma birai.
For kongen hadde skiber som fór til Tarsis sammen med Hirams folk; en gang hvert tredje år kom Tarsis-skibene hjem og hadde med gull og sølv, elfenben og aper og påfugler.
22 Sarki Solomon ya fi arziki da hikima in aka kwatanta da dukan sauran sarakunan duniya.
Kong Salomo blev større enn alle jordens konger i rikdom og visdom.
23 Dukan sarakunan duniya sun nemi su sadu da Solomon don su ji hikimar da Allah ya sa a zuciyarsa.
Fra alle jordens kanter kom det konger for å se Salomo og høre hans visdom, som Gud hadde lagt i hans hjerte,
24 Shekara, shekara, duk wanda ya zo wurinsa yakan kawo kyauta, kayayyakin azurfa da na zinariya, da riguna, makamai da kayan yaji, da dawakai da kuma alfadarai.
og hver av dem hadde gaver med: sølvkar og gullkar og klær, våben og krydderier, hester og mulesler; så gjorde de år om annet.
25 Solomon ya kasance da wuraren ajiye dawakai dubu huɗu don dawakai da kekunan yaƙi, yana da dawakai dubu goma sha biyu waɗanda ya ajiye a biranen kekunan yaƙi da kuma tare da shi a Urushalima.
Salomo hadde fire tusen stallrum for hester og stridsvogner og tolv tusen hestfolk; dem la han dels i vognbyene, dels hos sig selv i Jerusalem.
26 Ya yi mulki bisa dukan sarakuna daga Kogi Yuferites zuwa ƙasar Filistiyawa, har zuwa iyakar Masar.
Han rådet over alle kongene fra elven til filistrenes land og like til Egyptens landemerke.
27 Sarki ya sa azurfa ta zama barkatai a Urushalima kamar duwatsu, al’ul kuma da yawa kamar itatuwan fir a gindin tsaunuka.
Kongen gjorde sølvet i Jerusalem like så almindelig som sten, og sedertre like så almindelig som morbærtrærne i lavlandet.
28 An sayo dawakan Solomon daga Masar da kuma daga dukan sauran ƙasashe.
Og hester innførtes til Salomo fra Egypten og fra alle andre land.
29 Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, daga farko har zuwa ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin annabi Natan, cikin annabcin Ahiya mutumin Shilo da kuma cikin wahayin Iddo mai gani game da Yerobowam ɗan Nebat.
Hvad som ellers er å fortelle om Salomo, både i hans første og i hans senere dager, er opskrevet i profeten Natans krønike og i Akia fra Silo's spådomsbok og i seeren Jedis syn om Jeroboam, Nebats sønn.
30 Solomon ya yi mulki a Urushalima a bisa dukan Isra’ila shekaru arba’in.
Salomo var konge i Jerusalem over hele Israel i firti år.
31 Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi cikin birnin Dawuda mahaifinsa. Rehobowam ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Så la Salomo sig til hvile hos sine fedre og blev begravet i sin far Davids stad; og hans sønn Rehabeam blev konge i hans sted.

< 2 Tarihi 9 >