< 2 Tarihi 9 >
1 Sa’ad da sarauniyar Sheba ta ji shahararr Solomon, sai ta zo Urushalima tă gwada shi da tambayoyi masu wuya. Ta iso tare da ayari mai girma, da raƙuma ɗauke da kayan yaji, zinariya mai yawa, da kuma duwatsu masu daraja, ta zo wurin Solomon ta kuma yi magana da shi game da dukan abin da yake zuciyarta.
And the queen of Sheba heard of the fame of Solomon, and came to Jerusalem to prove Solomon with enigmas; with a very great train, and camels that bore spices and gold in great abundance, and precious stones; and she came to Solomon, and spoke with him of all that was in her heart.
2 Solomon ya amsa dukan tambayoyinta; babu wani abin da ya yi masa wuya yă bayyana mata.
And Solomon explained to her all she spoke of, and there was not a thing hidden from Solomon that he did not explain to her.
3 Sa’ad da sarauniyar Sheba ta ga hikimar Solomon da kuma fadan da ya gina,
And when the queen of Sheba saw the wisdom of Solomon, and the house that he had built,
4 ta ga abincin da yake teburinsa, ta ga zaman fadawansa, bayi masu yin masa hidima cikin rigunansu, ta ga masu riƙe kwaf cikin rigunansu da kuma hadayun ƙonawar da ya yi a haikalin Ubangiji, sai mamaki ya kama ta.
and the food of his table, and the deportment of his servants, and the order of service of his attendants and their apparel, and his cupbearers and their apparel, and his ascent by which he went up to the house of Jehovah, there was no more spirit in her.
5 Ta ce wa sarki, “Labarin da na ji a ƙasata game da nasarorinka da hikimarka, gaskiya ne.
And she said to the king, It was a true report that I heard in mine own land of thine affairs and of thy wisdom;
6 Amma ban gaskata abin da suka faɗa ba sai da na zo na kuma gani da idanuna. Tabbatacce, ko rabin girman hikimarka ba a faɗa mini ba, ka wuce labarin da na ji nesa ba kusa ba.
but I gave no credit to their words, until I came and mine eyes had seen; and behold, the half of the greatness of thy wisdom was not told me: thou exceedest the report that I heard.
7 Abin farin ciki ne ga mutanenka! Abin farin ciki ne ga fadawanka, waɗanda suke cin gaba da tsayawa a gabanka suna kuma jin hikimarka!
Happy are thy men, and happy are these thy servants, who stand continually before thee and hear thy wisdom!
8 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka, wanda ya ji daɗi a cikinka ya sa ka a kan kujerar sarautarsa a matsayin sarki don ka yi mulkin domin Ubangiji Allahnka. Saboda ƙaunar Allahnka wa Isra’ila da kuma sha’awarsa na riƙe su har abada, ya naɗa ka sarki a bisansu, don ka yi adalci da kuma gaskiya.”
Blessed be Jehovah thy God, who delighted in thee, to set thee on his throne, to be king to Jehovah thy God! Because thy God loved Israel, to establish them for ever, therefore did he make thee king over them, to do judgment and justice.
9 Sa’an nan ta ba sarki talenti 120 na zinariya, kayan yaji masu yawa, da kuma duwatsu masu daraja. Ba a taɓa kasance da irin kayan yaji mai yawa kamar waɗanda sarauniyar Sheba ta ba wa sarki Solomon ba.
And she gave the king a hundred and twenty talents of gold, and spices in very great abundance, and precious stones; neither was there any such spice as that which the queen of Sheba gave to king Solomon.
10 (Mutanen Hiram da mutanen Solomon suka kawo zinariya daga Ofir, suka kuma kawo gungumen algum da duwatsu masu daraja.
(And the servants also of Huram, and the servants of Solomon, who brought gold from Ophir, brought sandal-wood and precious stones.
11 Sarki ya yi amfani da gungumen algum don matakalan haikalin Ubangiji da kuma na fadan sarki, ya kuma yi garayu da molaye don mawaƙa. Ba a taɓa gani irinsu a Yahuda ba.)
And the king made of the sandal-wood stairs for the house of Jehovah, and for the king's house, and harps and lutes for the singers. And there were none such seen before in the land of Judah.)
12 Sarki Solomon ya ba sarauniyar Sheba duk abin da take so da kuma ta nema; ya ba ta fiye da abin da ta kawo masa. Sa’an nan ta tashi ta koma ƙasarta tare da masu rufe mata baya.
And king Solomon gave to the queen of Sheba all her desire, whatever she asked, besides what she had brought to the king. And she turned and went to her own land, she and her servants.
13 Nauyin zinariyar da Solomon yake karɓa shekara-shekara talenti 666 ne,
And the weight of gold that came to Solomon in one year was six hundred and sixty-six talents of gold,
14 ban da harajin da fatakai da’yan kasuwa suke biya. Haka kuma dukan sarakunan Arabiya da gwamnonin ƙasar suka kawo zinariya da azurfa wa Solomon.
besides [what] dealers and merchants brought, and [what] all the kings of Arabia and the governors of the country brought of gold and silver to Solomon.
15 Sarki Solomon ya yi manyan garkuwoyi ɗari biyu da zinariya; an yi kowane garkuwa da bekas ɗari shida na zinariya.
And king Solomon made two hundred targets of beaten gold, — he applied six hundred [shekels] of beaten gold to one target;
16 Ya kuma yi ƙanana garkuwoyi zinariya ɗari uku, da bekas ɗari uku na zinariya a kowanne. Sarki ya sa su a cikin Fadan da ake kira Kurmin Lebanon.
and three hundred shields of beaten gold, — he applied three hundred [shekels] of gold to one shield; and the king put them in the house of the forest of Lebanon.
17 Sai sarki ya yi wata kujerar sarauta mai girma da aka shafe ta da hauren giwa, aka kuma dalaye ta da zinariya zalla.
And the king made a great throne of ivory, and overlaid it with pure gold;
18 Kujerar tana da matakalai shida, da wurin sa ƙafa na zinariya haɗe da ita. A kowane gefen wurin zama, akwai wurin ajiye hannu, da zaki tsaye kusa da kowannensu.
and the throne had six steps, with a footstool of gold fastened to the throne; and there were arms on each side at the place of the seat, and two lions stood beside the arms;
19 Zakoki goma sha biyu sun tsaya a kan matakalai shida, ɗaya a ƙarshen matakala guda. Ba a taɓa yin irin wannan abu don wata masarauta ba.
and twelve lions stood there on the one side and on the other upon the six steps: there was not the like made in any kingdom.
20 Dukan kwaf na Sarki Solomon zinariya ne, kuma dukan kayayyakin gida a Fadan da ake kira Kurmin Lebanon zinariya ne zalla. Ba a yi wani abu da azurfa ba, domin ba a ɗauki azurfa a zamanin Solomon a bakin kome ba.
And all king Solomon's drinking vessels were of gold, and all the vessels of the house of the forest of Lebanon were of precious gold: silver was not of the least account in the days of Solomon.
21 Sarki yana da jerin jiragen ruwa na kasuwanci waɗanda mutanen Hiram ne suke kula da su. Sau ɗaya kowace shekara uku sukan dawo ɗauke da zinariya, azurfa, hauren giwa, gogo da kuma birai.
For the king's ships went to Tarshish with the servants of Huram: once in three years came the ships of Tarshish, bringing gold and silver, ivory, and apes, and peacocks.
22 Sarki Solomon ya fi arziki da hikima in aka kwatanta da dukan sauran sarakunan duniya.
And king Solomon was greater than all the kings of the earth in riches and wisdom.
23 Dukan sarakunan duniya sun nemi su sadu da Solomon don su ji hikimar da Allah ya sa a zuciyarsa.
And all the kings of the earth sought the presence of Solomon, to hear his wisdom, which God had put in his heart.
24 Shekara, shekara, duk wanda ya zo wurinsa yakan kawo kyauta, kayayyakin azurfa da na zinariya, da riguna, makamai da kayan yaji, da dawakai da kuma alfadarai.
And they brought every man his present, vessels of silver and vessels of gold, and clothing, armour, and spices, horses and mules, a rate year by year.
25 Solomon ya kasance da wuraren ajiye dawakai dubu huɗu don dawakai da kekunan yaƙi, yana da dawakai dubu goma sha biyu waɗanda ya ajiye a biranen kekunan yaƙi da kuma tare da shi a Urushalima.
And Solomon had four thousand stalls for horses and chariots, and twelve thousand horsemen; and he placed them in the chariot-cities, and with the king at Jerusalem.
26 Ya yi mulki bisa dukan sarakuna daga Kogi Yuferites zuwa ƙasar Filistiyawa, har zuwa iyakar Masar.
And he ruled over all the kings from the river as far as the land of the Philistines, and up to the border of Egypt.
27 Sarki ya sa azurfa ta zama barkatai a Urushalima kamar duwatsu, al’ul kuma da yawa kamar itatuwan fir a gindin tsaunuka.
And the king made silver in Jerusalem as stones, and cedars made he as the sycamores that are in the lowland for abundance.
28 An sayo dawakan Solomon daga Masar da kuma daga dukan sauran ƙasashe.
And they brought to Solomon horses out of Egypt, and out of all lands.
29 Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, daga farko har zuwa ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin annabi Natan, cikin annabcin Ahiya mutumin Shilo da kuma cikin wahayin Iddo mai gani game da Yerobowam ɗan Nebat.
And the rest of the acts of Solomon first and last, are they not written in the words of Nathan the prophet, and in the prophecy of Ahijah the Shilonite, and in the visions of Iddo the seer concerning Jeroboam the son of Nebat?
30 Solomon ya yi mulki a Urushalima a bisa dukan Isra’ila shekaru arba’in.
And Solomon reigned in Jerusalem over all Israel forty years.
31 Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi cikin birnin Dawuda mahaifinsa. Rehobowam ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
And Solomon slept with his fathers, and they buried him in the city of David his father; and Rehoboam his son reigned in his stead.