< 2 Tarihi 9 >

1 Sa’ad da sarauniyar Sheba ta ji shahararr Solomon, sai ta zo Urushalima tă gwada shi da tambayoyi masu wuya. Ta iso tare da ayari mai girma, da raƙuma ɗauke da kayan yaji, zinariya mai yawa, da kuma duwatsu masu daraja, ta zo wurin Solomon ta kuma yi magana da shi game da dukan abin da yake zuciyarta.
Og Dronningen af Seba hørte Salomos Rygte og kom for at prøve Salomo med mørke Taler til Jerusalem med en saare stor Skare af Kameler, som bare vellugtende Urter og Guld i Mangfoldighed og dyrebare Stene; og hun kom til Salomo og talte med ham alt det, som var i hendes Hjerte.
2 Solomon ya amsa dukan tambayoyinta; babu wani abin da ya yi masa wuya yă bayyana mata.
Og Salomo udtydede hende alle hendes Ord, og der var ikke et Ord skjult for Salomo, som han ej udtydede hende.
3 Sa’ad da sarauniyar Sheba ta ga hikimar Solomon da kuma fadan da ya gina,
Da Dronningen af Seba saa Salomos Visdom og det Hus, som han havde bygget,
4 ta ga abincin da yake teburinsa, ta ga zaman fadawansa, bayi masu yin masa hidima cikin rigunansu, ta ga masu riƙe kwaf cikin rigunansu da kuma hadayun ƙonawar da ya yi a haikalin Ubangiji, sai mamaki ya kama ta.
og Maden til hans Bord og hans Tjeneres Bolig, og hvordan de stode, som opvartede ham, og deres Klæder og hans Mundskænke og deres Klæder og hans Opgang, ad hvilken han gik op til Herrens Hus: Da var hun ude af sig selv.
5 Ta ce wa sarki, “Labarin da na ji a ƙasata game da nasarorinka da hikimarka, gaskiya ne.
Og hun sagde til Kongen: Det Ord er sandt, som jeg har hørt i mit Land om dine Sager og om din Visdom;
6 Amma ban gaskata abin da suka faɗa ba sai da na zo na kuma gani da idanuna. Tabbatacce, ko rabin girman hikimarka ba a faɗa mini ba, ka wuce labarin da na ji nesa ba kusa ba.
og jeg vilde ikke tro deres Ord, førend jeg kom, og mine Øjne have set det, og se, ikke Halvdelen er mig forkyndt af din megen Visdom; du har mere end efter Rygtet, som jeg har hørt.
7 Abin farin ciki ne ga mutanenka! Abin farin ciki ne ga fadawanka, waɗanda suke cin gaba da tsayawa a gabanka suna kuma jin hikimarka!
Salige ere dine Mænd, og salige ere disse dine Tjenere, som stedse staa for dit Ansigt, og som høre din Visdom!
8 Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allahnka, wanda ya ji daɗi a cikinka ya sa ka a kan kujerar sarautarsa a matsayin sarki don ka yi mulkin domin Ubangiji Allahnka. Saboda ƙaunar Allahnka wa Isra’ila da kuma sha’awarsa na riƙe su har abada, ya naɗa ka sarki a bisansu, don ka yi adalci da kuma gaskiya.”
Lovet være Herren din Gud, som havde Lyst til dig, at sætte dig paa sin Trone til Konge for Herren, din Gud! Fordi din Gud elsker Israel og vil befæste det evindelig, derfor satte han dig til Konge over dem, til at gøre Ret og Retfærdighed.
9 Sa’an nan ta ba sarki talenti 120 na zinariya, kayan yaji masu yawa, da kuma duwatsu masu daraja. Ba a taɓa kasance da irin kayan yaji mai yawa kamar waɗanda sarauniyar Sheba ta ba wa sarki Solomon ba.
Og hun gav Kongen hundrede og tyve Centner Guld og saare mange vellugtende Urter og dyrebare Stene; der var ikke saadanne Urter som disse, hvilke Dronningen af Seba gav Kong Salomo.
10 (Mutanen Hiram da mutanen Solomon suka kawo zinariya daga Ofir, suka kuma kawo gungumen algum da duwatsu masu daraja.
Dertil med havde Hurams Tjenere og Salomos Tjenere bragt Guld fra Ofir og bragt Hebentræ og dyrebare Stene.
11 Sarki ya yi amfani da gungumen algum don matakalan haikalin Ubangiji da kuma na fadan sarki, ya kuma yi garayu da molaye don mawaƙa. Ba a taɓa gani irinsu a Yahuda ba.)
Og af Hebentræet lod Kongen gøre Gange til Herrens Hus og til Kongens Hus, samt Harper og Psaltre til Sangerne; og der blev ikke tilforn set saadant som dette i Judas Land.
12 Sarki Solomon ya ba sarauniyar Sheba duk abin da take so da kuma ta nema; ya ba ta fiye da abin da ta kawo masa. Sa’an nan ta tashi ta koma ƙasarta tare da masu rufe mata baya.
Og Kong Salomo gav Dronningen af Seba alt det, hun havde Lyst til, som hun begærede, foruden Gaver for det, som hun havde medbragt til Kongen; og hun vendte om og drog til sit Land, hun og hendes Tjenere.
13 Nauyin zinariyar da Solomon yake karɓa shekara-shekara talenti 666 ne,
Og Vægten paa det Guld, som kom til Salomo paa eet Aar, var seks Hundrede og seks og tresindstyve Centner Guld
14 ban da harajin da fatakai da’yan kasuwa suke biya. Haka kuma dukan sarakunan Arabiya da gwamnonin ƙasar suka kawo zinariya da azurfa wa Solomon.
foruden det, som indkom fra Toldbetjentene, og det, som Købmændene bragte; og alle Kongerne af Arabia og Fyrsterne i Landet bragte Guld og Sølv til Salomo.
15 Sarki Solomon ya yi manyan garkuwoyi ɗari biyu da zinariya; an yi kowane garkuwa da bekas ɗari shida na zinariya.
Og Kong Salomo lod gøre to Hundrede Skjolde af drevet Guld; seks Hundrede Sekel drevet Guld lod han gaa paa hvert Skjold;
16 Ya kuma yi ƙanana garkuwoyi zinariya ɗari uku, da bekas ɗari uku na zinariya a kowanne. Sarki ya sa su a cikin Fadan da ake kira Kurmin Lebanon.
og tre Hundrede smaa Skjolde af drevet Guld, tre Hundrede Sekel Guld lod han gaa paa hvert Skjold; og Kongen lagde dem i Libanons Skovhus.
17 Sai sarki ya yi wata kujerar sarauta mai girma da aka shafe ta da hauren giwa, aka kuma dalaye ta da zinariya zalla.
Og Kongen lod gøre en stor Trone af Elfenben og beslog den med purt Guld.
18 Kujerar tana da matakalai shida, da wurin sa ƙafa na zinariya haɗe da ita. A kowane gefen wurin zama, akwai wurin ajiye hannu, da zaki tsaye kusa da kowannensu.
Og Tronen havde seks Trin og en Skammel, som med Guld vare fastgjorte til Tronen, og der var Arme paa begge Sider omkring Sædets Sted, og to Løver stode ved Armene.
19 Zakoki goma sha biyu sun tsaya a kan matakalai shida, ɗaya a ƙarshen matakala guda. Ba a taɓa yin irin wannan abu don wata masarauta ba.
Og der stod tolv Løver paa de seks Trin paa begge Sider; saadant er ikke gjort i noget Rige.
20 Dukan kwaf na Sarki Solomon zinariya ne, kuma dukan kayayyakin gida a Fadan da ake kira Kurmin Lebanon zinariya ne zalla. Ba a yi wani abu da azurfa ba, domin ba a ɗauki azurfa a zamanin Solomon a bakin kome ba.
Og alle Kong Salomos Drikkekar vare af Guld, og alle Karrene i Libanons Skovhus vare af fint Guld; Sølv agtedes ikke for noget i Salomos Dage.
21 Sarki yana da jerin jiragen ruwa na kasuwanci waɗanda mutanen Hiram ne suke kula da su. Sau ɗaya kowace shekara uku sukan dawo ɗauke da zinariya, azurfa, hauren giwa, gogo da kuma birai.
Thi Kongens Skibe fore til Tharsis med Hurams Tjenere; een Gang i tre Aar kom de Tharsis Skibe, som bragte Guld og Sølv, Elfenben, Aber og Paafugle.
22 Sarki Solomon ya fi arziki da hikima in aka kwatanta da dukan sauran sarakunan duniya.
Og Kong Salomo blev større end alle Konger paa Jorden ved Rigdom og Visdom.
23 Dukan sarakunan duniya sun nemi su sadu da Solomon don su ji hikimar da Allah ya sa a zuciyarsa.
Og alle Jordens Konger søgte Salomos Ansigt for at høre hans Visdom, som Gud havde givet i hans Hjerte.
24 Shekara, shekara, duk wanda ya zo wurinsa yakan kawo kyauta, kayayyakin azurfa da na zinariya, da riguna, makamai da kayan yaji, da dawakai da kuma alfadarai.
Og de førte hver sin Skænk: Sølvkar og Guldkar og Klæder, Rustninger og vellugtende Urter, Heste og Muler, hvilket skete aarligt.
25 Solomon ya kasance da wuraren ajiye dawakai dubu huɗu don dawakai da kekunan yaƙi, yana da dawakai dubu goma sha biyu waɗanda ya ajiye a biranen kekunan yaƙi da kuma tare da shi a Urushalima.
Og Salomo havde fire Tusinde Stalde til Heste og Vogne og tolv Tusinde Ryttere, og han lod dem blive i Vognstæderne og hos Kongen i Jerusalem.
26 Ya yi mulki bisa dukan sarakuna daga Kogi Yuferites zuwa ƙasar Filistiyawa, har zuwa iyakar Masar.
Og han herskede over alle Kongerne, fra Floden og indtil Filisternes Land og indtil Ægyptens Landemærke.
27 Sarki ya sa azurfa ta zama barkatai a Urushalima kamar duwatsu, al’ul kuma da yawa kamar itatuwan fir a gindin tsaunuka.
Og Kongen gjorde Sølvet i Jerusalem som Stenene og gjorde Cedertræerne som Morbærtræerne, der ere i Lavlandet i Mangfoldighed.
28 An sayo dawakan Solomon daga Masar da kuma daga dukan sauran ƙasashe.
Og man udførte Heste til Salomo fra Ægypten og fra alle Landene.
29 Game da sauran ayyukan mulkin Solomon, daga farko har zuwa ƙarshe, an rubuta su a cikin tarihin annabi Natan, cikin annabcin Ahiya mutumin Shilo da kuma cikin wahayin Iddo mai gani game da Yerobowam ɗan Nebat.
Men det øvrige af Salomos Handeler, de første og de sidste, ere de Ting ikke skrevne i Profeten Nathans Krønike og i Siloniten Ahias Profeti og i Seeren Jeddis Syn imod Jeroboam, Nebats Søn?
30 Solomon ya yi mulki a Urushalima a bisa dukan Isra’ila shekaru arba’in.
Og Salomo regerede i Jerusalem over al Israel fyrretyve Aar.
31 Sa’an nan ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi cikin birnin Dawuda mahaifinsa. Rehobowam ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Og Salomo laa med sine Fædre, og de begrove ham i Davids, hans Faders, Stad; og Roboam, hans Søn, blev Konge i hans Sted.

< 2 Tarihi 9 >