< 2 Tarihi 8 >
1 A ƙarshen shekaru ashirin, a lokacin da Solomon ya gina haikalin Ubangiji da nasa fadan,
Or, vingt ans s’étant accomplis après que Salomon eut bâti la maison du Seigneur et sa propre maison,
2 Solomon ya sāke gina ƙauyukan da Hiram ya ba shi, ya kuma zaunar da Isra’ilawa a cikinsu.
Il bâtit les villes qu’Hiram lui avait données, et y fit habiter les enfants d’Israël.
3 Sa’an nan Solomon ya tafi Hamat-Zoba ya ci ta da yaƙi.
Il s’en alla aussi à Emath-Suba, et s’en empara.
4 Ya kuma gina Tadmor a hamada da kuma dukan biranen ajiyar da ya gina a Hamat.
Et il bâtit Palmyre dans le désert, et les autres villes très fortifiées, il les bâtit en Emath.
5 Ya sāke gina Bet-Horon na Bisa da kuma Bet-Horon na Ƙasa a matsayin birane masu katanga, da bangaye da ƙofofi da kuma ƙyamare,
Il construisit aussi Béthoron la haute, et Béthoron la basse, villes murées, ayant des portes, des verrous et des serrures;
6 haka kuma Ba’alat da dukan biranen ajiyarsa, da kuma dukan birane domin keken yaƙinsa da dawakansa, duk abin da ya so yă gina a Urushalima, a Lebanon da kuma dukan yankin da ya yi mulki, ya gina shi.
Et de plus Balaath. toutes les villes très fortes qui étaient à Salomon, toutes les villes des quadriges, et les villes de la cavalerie: tout ce que Salomon voulut et décida, il le bâtit, dans Jérusalem, et sur le Liban, et dans tout le pays de sa domination.
7 Dukan mutanen da suka rage daga Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa (waɗannan mutane ba Isra’ilawa ba ne),
Quant à tout le peuple qui était resté des Héthéens, des Amorrhéens, des Phérézéens, des Hévéens et des Jébuséens, qui n’étaient point de la race d’Israël,
8 wato, zuriyarsu da suka ragu a ƙasar, wadda Isra’ilawa ba su hallaka ba, waɗannan ne Solomon ya mai da su bayinsa na aikin dole, kamar yadda yake har wa yau.
Mais des enfants et des descendants de ceux que les enfants d’Israël n’avaient point tués, Salomon les rendit dépendants et tributaires jusqu’à ce jour.
9 Amma Solomon bai mai da Isra’ilawa bayi don aikinsa ba; su ne mayaƙansa, shugabannin hafsoshinsa, da shugabannin keken yaƙinsa da kuma mahayan keken yaƙinsa.
Pour les enfants d’Israël, il ne les employa pas à travailler aux ouvrages du roi; car c’étaient des hommes de guerre, les premiers chefs et les commandants de ses quadriges et de sa cavalerie.
10 Su ne kuma manyan ma’aikatan Sarki Solomon, manyan mutane ɗari biyu da hamsin masu lura da mutane.
Or tous les princes de l’armée du roi Salomon étaient au nombre de deux cent cinquante, qui instruisaient le peuple.
11 Solomon ya kawo’yar Fir’auna daga Birnin Dawuda zuwa fadan da ya gina mata, gama ya ce, “Matata ba za tă zauna a fadan Dawuda sarkin Isra’ila ba, domin wuraren da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga masu tsarki ne.”
Quant à la fille de Pharaon, il la transporta de la cité de David dans la maison qu’il lui avait bâtie; car le roi dit: Ma femme n’habitera pas dans la maison de David, roi d’Israël, parce quelle a été sanctifiée, du moment que l’arche du Seigneur y est entrée.
12 A kan bagaden Ubangiji da ya gina a gaban shirayi, Solomon ya miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji,
Alors Salomon offrit des holocaustes au Seigneur sur l’autel du Seigneur, qu’il avait construit devant le portique,
13 bisa ga bukace-bukace na kullum don hadayun da Musa ya umarta don Asabbatai, Sabon Wata da kuma bukukkuwa uku na shekara, Bikin Burodi Marar Yisti, Bikin Makoni da Bikin Tabanakul.
Pour qu’on y offrît chaque jour des sacrifices, selon le commandement de Moïse, aux jours du sabbat, aux calendes, et aux jours de fête, trois fois par an, c’est-à-dire à la solennité des azymes, à la solennité des semaines et à la solennité des tabernacles.
14 Bisa ga farillar mahaifinsa Dawuda, ya naɗa ɓangarori na firistoci don ayyukansu da Lawiyawa don su jagoranci yabo su kuma taimaki firistoci bisa ga bukace-bukacen kowace rana. Ya kuma naɗa matsara ƙofofi ɓangarori, ɓangarori don ƙofofi dabam-dabam domin abin da Dawuda mutumin Allah ya umarta ke nan.
Et il établit, selon les prescriptions de David, son père, les devoirs des prêtres dans leur ministère, les Lévites dans leur ordre, pour chanter des louanges et servir devant les prêtres, suivant le rite de chaque jour, et les portiers, d’après la distribution qui en avait été faite pour chaque porte; ainsi, en effet, l’avait ordonné David, l’homme de Dieu.
15 Ba a kuwa yi rashin biyayya ba game da abin da sarki ya umarta game da firistoci ko Lawiyawa a kan kayan haikalin ba.
Touchant les commandements du roi, ni les prêtres ni les Lévites n’omirent rien de tout ce qu’il avait ordonné, et par rapport à la garde des trésors,
16 An yi dukan ayyukan Solomon, daga ranar kafa tushen haikalin Ubangiji har gamawarsa. Ta haka aka gama haikalin Ubangiji.
Salomon eut toutes les dépenses préparées depuis le jour qu’il jeta les fondements de la maison jusqu’au jour où il l’acheva.
17 Sa’an nan Solomon ya tafi Eziyon Geber da Elot a bakin tekun Edom.
Alors Salomon alla à Asiongaber et à Aïlath, sur le bord de la mer Rouge, qui est dans la terre d’Edom.
18 Sai Hiram ya aika masa jiragen ruwan da masu tuƙinsu waɗanda suka san teku sosai. Ma’aikatan Hiram suka tafi da na Solomon zuwa Ofir suka dawo da talentin zinariya ɗari huɗu da hamsin wa Sarki Solomon.
Or Hiram lui envoya, par l’entremise de ses serviteurs, des vaisseaux et des matelots connaissant la mer, et ils allèrent avec les serviteurs de Salomon à Ophir, et ils emportèrent de là quatre cent cinquante talents d’or, et ils les portèrent au roi Salomon.