< 2 Tarihi 8 >

1 A ƙarshen shekaru ashirin, a lokacin da Solomon ya gina haikalin Ubangiji da nasa fadan,
Or il arriva au bout des vingt ans, pendant lesquels Salomon bâtit la maison de l'Eternel, et sa maison;
2 Solomon ya sāke gina ƙauyukan da Hiram ya ba shi, ya kuma zaunar da Isra’ilawa a cikinsu.
Qu'il bâtit aussi les villes que Hiram lui avait données, et il y fit habiter les enfants d'Israël.
3 Sa’an nan Solomon ya tafi Hamat-Zoba ya ci ta da yaƙi.
Puis Salomon s'en alla à Hamath de Tsoba, et la conquit.
4 Ya kuma gina Tadmor a hamada da kuma dukan biranen ajiyar da ya gina a Hamat.
Salomon bâtit aussi Tadmor au désert, et toutes les villes de munitions qu'il bâtit à Hamath.
5 Ya sāke gina Bet-Horon na Bisa da kuma Bet-Horon na Ƙasa a matsayin birane masu katanga, da bangaye da ƙofofi da kuma ƙyamare,
Et il bâtit aussi Beth-horon la haute, et Beth-horon la basse, villes fortes de murailles, de portes, et de barres.
6 haka kuma Ba’alat da dukan biranen ajiyarsa, da kuma dukan birane domin keken yaƙinsa da dawakansa, duk abin da ya so yă gina a Urushalima, a Lebanon da kuma dukan yankin da ya yi mulki, ya gina shi.
Et Bahalath, et toutes les villes de munitions qu'eut Salomon, et toutes les villes où il tenait ses chariots, et les villes où il tenait ses gens de cheval, et tout ce que Salomon prit plaisir de bâtir à Jérusalem, et au Liban, et dans tout le pays de sa domination.
7 Dukan mutanen da suka rage daga Hittiyawa, Amoriyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa (waɗannan mutane ba Isra’ilawa ba ne),
Et quant à tout le peuple qui était resté des Héthiens, des Amorrhéens, des Phérésiens, des Héviens et des Jébusiens, qui n'étaient point d'Israël;
8 wato, zuriyarsu da suka ragu a ƙasar, wadda Isra’ilawa ba su hallaka ba, waɗannan ne Solomon ya mai da su bayinsa na aikin dole, kamar yadda yake har wa yau.
D'entre les gens qui étaient restés après eux au pays, [et] que les enfants d'Israël n'avaient pas entièrement détruits, Salomon les rendit tributaires jusqu'à aujourd'hui.
9 Amma Solomon bai mai da Isra’ilawa bayi don aikinsa ba; su ne mayaƙansa, shugabannin hafsoshinsa, da shugabannin keken yaƙinsa da kuma mahayan keken yaƙinsa.
Mais Salomon ne souffrit point que les enfants d'Israël fussent asservis à faire son ouvrage, mais ils étaient gens de guerre, et principaux Chefs de ses capitaines, et Chefs de ses chariots, et ses hommes d'armes.
10 Su ne kuma manyan ma’aikatan Sarki Solomon, manyan mutane ɗari biyu da hamsin masu lura da mutane.
Il y en avait aussi deux cent cinquante, qui étaient les principaux Chefs de ceux qui étaient établis [sur les ouvrages] du Roi Salomon, lesquels avaient l'intendance sur le peuple.
11 Solomon ya kawo’yar Fir’auna daga Birnin Dawuda zuwa fadan da ya gina mata, gama ya ce, “Matata ba za tă zauna a fadan Dawuda sarkin Isra’ila ba, domin wuraren da akwatin alkawarin Ubangiji ya shiga masu tsarki ne.”
Or Salomon fit monter la fille de Pharaon de la Cité de David en la maison qu'il lui avait bâtie; car il dit: Ma femme n'habitera point dans la maison de David Roi d'Israël, parce que les lieux auxquels l'Arche de l'Eternel est entrée sont saints.
12 A kan bagaden Ubangiji da ya gina a gaban shirayi, Solomon ya miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji,
Et Salomon offrait des holocaustes à l'Eternel, sur l'autel de l'Eternel, qu'il avait bâti vis-à-vis du porche.
13 bisa ga bukace-bukace na kullum don hadayun da Musa ya umarta don Asabbatai, Sabon Wata da kuma bukukkuwa uku na shekara, Bikin Burodi Marar Yisti, Bikin Makoni da Bikin Tabanakul.
Et même selon qu'il échéait chaque jour, offrant selon le commandement de Moïse aux jours de Sabbat, et aux nouvelles lunes, et aux fêtes solennelles, trois fois l'année, [savoir] en la fête solennelle des pains sans levain, en la fête solennelle des semaines, et en la fête solennelle des Tabernacles.
14 Bisa ga farillar mahaifinsa Dawuda, ya naɗa ɓangarori na firistoci don ayyukansu da Lawiyawa don su jagoranci yabo su kuma taimaki firistoci bisa ga bukace-bukacen kowace rana. Ya kuma naɗa matsara ƙofofi ɓangarori, ɓangarori don ƙofofi dabam-dabam domin abin da Dawuda mutumin Allah ya umarta ke nan.
Et il établit, suivant ce qu'avait ordonné David son père, les départements des Sacrificateurs selon leur ministère, et les Lévites selon leurs charges, afin qu'ils louassent [Dieu], et qu'ils fissent le service, aidant les Sacrificateurs selon l'ordinaire de chaque jour. [Il établit aussi] les portiers en leurs départements à chaque porte; car tel avait été le commandement de David homme de Dieu.
15 Ba a kuwa yi rashin biyayya ba game da abin da sarki ya umarta game da firistoci ko Lawiyawa a kan kayan haikalin ba.
Et on ne s'écarta point du commandement du Roi touchant les Sacrificateurs et les Lévites, en aucun article, ni en ce qui regardait les trésors.
16 An yi dukan ayyukan Solomon, daga ranar kafa tushen haikalin Ubangiji har gamawarsa. Ta haka aka gama haikalin Ubangiji.
Tout l'ouvrage donc de Salomon ayant été bien préparé, jusqu'au jour que la maison de l'Eternel fut fondée, et jusqu'à ce qu'elle fut achevée, la maison de l'Eternel fut ainsi finie.
17 Sa’an nan Solomon ya tafi Eziyon Geber da Elot a bakin tekun Edom.
Alors Salomon s'en alla à Hetsjon-guéber, et à Eloth, sur le rivage de la mer, qui est au pays d'Edom.
18 Sai Hiram ya aika masa jiragen ruwan da masu tuƙinsu waɗanda suka san teku sosai. Ma’aikatan Hiram suka tafi da na Solomon zuwa Ofir suka dawo da talentin zinariya ɗari huɗu da hamsin wa Sarki Solomon.
Et Hiram lui envoya, sous la conduite de ses serviteurs, des navires, et des serviteurs expérimentés dans la marine, qui s'en allèrent avec les serviteurs de Salomon à Ophir; et ils prirent de là quatre cent cinquante talents d'or, et les apportèrent au Roi Salomon.

< 2 Tarihi 8 >