< 2 Tarihi 7 >
1 Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
Da Salomo hadde endt sin bønn, falt det ild ned fra himmelen og fortærte brennofferet og slaktofferne, og Herrens herlighet fylte huset.
2 Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
Og prestene kunde ikke gå inn i Herrens hus; for Herrens herlighet fylte Herrens hus.
3 Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa, “Ubangiji mai alheri ne, ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
Alle Israels barn så hvorledes ilden falt ned, og Herrens herlighet kom over huset; da kastet de sig ned på gulvet med ansiktet mot jorden og tilbad og lovet Herren, fordi han er god, og hans miskunnhet varer evindelig.
4 Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
Og kongen og alt folket ofret slaktoffer for Herrens åsyn.
5 Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
To og tyve tusen stykker storfe og hundre og tyve tusen stykker småfe var det slaktoffer som kong Salomo bar frem. Således var det kongen og alt folket innvidde Guds hus.
6 Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
Og prestene stod på sine poster, og levittene stod med Herrens musikkinstrumenter, som kong David hadde latt gjøre til å prise Herren med, fordi hans miskunnhet varer evindelig; for David lot dem utføre lovsangen. Men prestene stilte sig midt imot dem og blåste i trompeter, mens hele Israel stod.
7 Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
Og Salomo helliget den midterste del av forgården som var foran Herrens hus; for der ofret han brennofferne og fettstykkene av takkofferne, fordi kobberalteret som Salomo hadde gjort, ikke kunde rumme brennofferet og matofferet og fettstykkene.
8 Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
I syv dager feiret Salomo dengang festen, og hele Israel med ham, en stor mengde folk som var kommet sammen like fra Hamatveien og til Egyptens bekk.
9 A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
Og på den åttende dag holdt de en festforsamling; for alterets innvielse feiret de i syv dager og festen i syv dager.
10 A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
På den tre og tyvende dag i den syvende måned lot han folket fare hjem igjen, glade og vel til mote over det gode Herren hadde gjort mot David og Salomo og mot sitt folk Israel.
11 Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
Salomo var nu ferdig med å bygge Herrens hus og kongens hus; og alt det han hadde hatt i sinne å gjøre i Herrens hus og i sitt eget hus, hadde han lykkelig utført.
12 sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce, “Na ji addu’arka na kuma zaɓi wannan wuri don kaina, a matsayin haikali don hadayu.
Da åpenbarte Herren sig for Salomo om natten og sa til ham: Jeg har hørt din bønn og utvalgt dette sted til et offersted for mig.
13 “Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
Når jeg lukker himmelen, så det ikke kommer regn, og når jeg byder gresshopper å fortære landet, og når jeg sender pest iblandt mitt folk,
14 in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
og så mitt folk, som er kalt med mitt navn, ydmyker sig og beder og søker mitt åsyn og vender om fra sine onde veier, så vil jeg høre fra himmelen og forlate deres synd og læge deres land.
15 Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
Nu skal mine øine være oplatt og mine ører merke på den bønn som bedes på dette sted.
16 Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
Og nu har jeg utvalgt og helliget dette hus, forat mitt navn skal bo der til evig tid, og mine øine og mitt hjerte skal være der alle dager.
17 “Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
Hvis du nu vandrer for mitt åsyn, som din far David gjorde, så du gjør alt det jeg har befalt dig, og holder mine bud og mine lover,
18 zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
så vil jeg trygge din kongetrone efter den pakt jeg gjorde med din far David da jeg sa: Det skal aldri fattes en mann av din ætt til å råde over Israel.
19 “Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
Men hvis I vender eder bort og forlater de lover og bud som jeg har forelagt eder, og gir eder til å tjene andre guder og tilbede dem,
20 zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
så vil jeg rykke dem op av mitt land, som jeg har gitt dem, og dette hus som jeg har helliget for mitt navn, vil jeg forkaste fra mitt åsyn og gjøre det til et ordsprog og til en spott blandt alle folk.
21 Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
Og hver den som går forbi dette hus, som har vært så ophøiet, skal forferdes, og når nogen da spør: Hvorfor har Herren gjort således mot dette land og dette hus?
22 Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’”
da skal de svare: Fordi de forlot Herren, sine fedres Gud, som førte dem ut av Egyptens land, og holdt sig til andre guder og tilbad dem og dyrket dem; derfor har han ført all denne ulykke over dem.