< 2 Tarihi 7 >
1 Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
Lorsque Salomon eut achevé de se répandre en prières, le feu descendit du ciel, et consuma les holocaustes et les victimes; et la majesté du Seigneur remplit la maison.
2 Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
Et les prêtres mêmes ne pouvaient entrer dans le temple du Seigneur, parce que la majesté du Seigneur avait rempli le temple du Seigneur.
3 Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa, “Ubangiji mai alheri ne, ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
Mais tous les enfants d’Israël aussi virent descendre le feu et la gloire du Seigneur sur la maison; et tombant, inclinés vers la terre, sur le pavé qui était de pierre, ils adorèrent et louèrent le Seigneur: Parce qu’il est bon, parce que sa miséricorde est éternelle.
4 Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
Or le roi et tout le peuple immolaient des victimes devant le Seigneur.
5 Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
Le roi Salomon tua donc vingt-deux mille bœufs et cent vingt mille béliers; et le roi dédia, ainsi que tout le peuple, la maison du Seigneur.
6 Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
Or les prêtres étaient appliqués à leurs fonctions, et les Lévites jouaient des instruments propres aux cantiques du Seigneur qu’a composés le roi David pour louer le Seigneur: Parce que sa miséricorde est éternelle; chantant les hymnes de David sur leurs instruments; mais les prêtres sonnaient des trompettes devant eux, et tout Israël était debout.
7 Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
Salomon consacra aussi le milieu du parvis devant le temple du Seigneur; car il avait offert là les holocaustes et les graisses des hosties pacifiques, parce que l’autel d’airain qu’il avait fait ne pouvait tenir les holocaustes, les sacrifices et les graisses.
8 Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
Salomon fit donc en ce temps-là la solennité pendant sept jours, et tout Israël avec lui: assemblée très grande, venue depuis l’entrée d’Emath jusqu’au torrent d’Égypte.
9 A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
Et au huitième jour, il fit une réunion, parce qu’il avait dédié l’autel durant sept jours, et qu’il avait célébré la solennité durant sept jours.
10 A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
Ainsi, au vingt-troisième jour du septième mois, il renvoya dans leurs tabernacles les peuples se livrant à l’allégresse, et se réjouissant du bien qu’avait fait le Seigneur à David, à Salomon et à Israël son peuple.
11 Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
Salomon acheva donc la maison du Seigneur, la maison du roi, et tout ce qu’il s’était proposé en son cœur de faire dans la maison du Seigneur et dans sa propre maison, et il prospéra.
12 sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce, “Na ji addu’arka na kuma zaɓi wannan wuri don kaina, a matsayin haikali don hadayu.
Or le Seigneur lui apparut pendant la nuit, et dit: J’ai entendu ta prière, et choisi ce lieu pour moi, comme une maison de sacrifice.
13 “Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
Si je ferme le ciel, et qu’il ne tombe point de pluie; si j’ordonne et je commande à la sauterelle de dévorer la terre, et si j’envoie une peste à mon peuple,
14 in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
Mais que, converti, mon peuple, sur qui a été invoqué mon nom. me prie, et qu’il recherche ma face, et qu’il fasse pénitence de ses voies très mauvaises, alors moi je les exaucerai du ciel, et je pardonnerai leurs péchés, et je purifierai leur terre.
15 Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
Mes yeux aussi seront ouverts, et mes oreilles attentives à la prière de celui qui priera en ce lieu;
16 Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
Car j’ai choisi et j’ai sanctifié ce lieu, afin que mon nom y soit à jamais, et que mes yeux et mon cœur y demeurent constamment tous les jours.
17 “Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
Et toi-même, si tu marches devant moi comme a marché David ton père; si tu fais selon tout ce que je t’ai ordonné, et que tu gardes mes lois et mes ordonnances,
18 zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
J’élèverai le trône de ton règne comme je l’ai promis à David, ton père, disant: On n’enlèvera pas à ta race un homme qui doit être prince en Israël.
19 “Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
Mais si vous vous détournez, et que vous abandonniez mes lois et mes préceptes que je vous ai proposés, et que, vous en allant, vous serviez des dieux étrangers et les adoriez,
20 zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
Je vous arracherai de ma terre que je vous ai donnée; et cette maison que j’ai consacrée à mon nom, je la rejetterai de ma face, et je la livrerai en proverbe et en exemple à tous les peuples.
21 Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
Ainsi cette maison sera en dérision à tous ceux qui passeront, et ils diront, frappés d’étonnement: Pourquoi le Seigneur a-t-il fait ainsi à cette terre et à cette maison?
22 Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’”
Et l’on répondra: Parce qu’ils ont abandonné le Seigneur Dieu de leurs pères, qui les retira de la terre d’Égypte, et qu’ils ont pris des dieux étrangers, et qu’ils les ont adorés et servis: c’est pour cela que sont venus sur eux tous ces maux.