< 2 Tarihi 7 >

1 Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
Et quand Salomon eut achevé de prier, le feu descendit des cieux et consuma l’holocauste et les sacrifices, et la gloire de l’Éternel remplit la maison.
2 Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
Et les sacrificateurs ne pouvaient entrer dans la maison de l’Éternel, car la gloire de l’Éternel remplissait la maison de l’Éternel.
3 Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa, “Ubangiji mai alheri ne, ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
Et tous les fils d’Israël, voyant descendre le feu, et la gloire de l’Éternel sur la maison, s’inclinèrent le visage en terre sur le pavement, et se prosternèrent, et célébrèrent l’Éternel: Car il est bon, car sa bonté [demeure] à toujours!
4 Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
Et le roi et tout le peuple sacrifièrent des sacrifices devant l’Éternel.
5 Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
Et le roi Salomon sacrifia un sacrifice de 22 000 bœufs et de 120 000 moutons. Et le roi et tout le peuple firent la dédicace de la maison de Dieu.
6 Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
Et les sacrificateurs se tinrent à leurs charges, et les lévites avec les instruments de musique de l’Éternel, que le roi David avait faits pour célébrer l’Éternel, parce que sa bonté [demeure] à toujours, – quand David louait par leur moyen. Et les sacrificateurs sonnèrent des trompettes vis-à-vis d’eux, et tout Israël se tenait là.
7 Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
Et Salomon sanctifia le milieu du parvis qui était devant la maison de l’Éternel; car il offrit là les holocaustes et la graisse des sacrifices de prospérités, parce que l’autel d’airain que Salomon avait fait ne pouvait recevoir l’holocauste, et l’offrande de gâteau, et les graisses.
8 Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
Et Salomon célébra la fête en ce temps-là, pendant sept jours, et tout Israël avec lui, depuis l’entrée de Hamath jusqu’au torrent d’Égypte, une très grande congrégation.
9 A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
Et au huitième jour ils célébrèrent une fête solennelle; car ils firent la dédicace de l’autel pendant sept jours, et la fête pendant sept jours.
10 A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
Et le vingt-troisième jour du septième mois, il renvoya le peuple à ses tentes, joyeux et le cœur heureux à cause du bien que l’Éternel avait fait à David, et à Salomon, et à Israël, son peuple.
11 Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
Et Salomon acheva la maison de l’Éternel et la maison du roi; et, en tout ce que Salomon avait eu à cœur de faire dans la maison de l’Éternel et dans sa maison, il réussit.
12 sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce, “Na ji addu’arka na kuma zaɓi wannan wuri don kaina, a matsayin haikali don hadayu.
Et l’Éternel apparut de nuit à Salomon, et lui dit: J’ai entendu ta prière, et je me suis choisi ce lieu-ci pour une maison de sacrifice.
13 “Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
Si je ferme les cieux et qu’il n’y ait pas de pluie, et si je commande à la sauterelle de dévorer la terre, et si j’envoie la peste parmi mon peuple,
14 in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
et que mon peuple, qui est appelé de mon nom, s’humilie, et prie, et cherche ma face, et revienne de ses mauvaises voies, moi aussi j’écouterai des cieux, et je pardonnerai leur péché, et je guérirai leur pays.
15 Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
Maintenant mes yeux seront ouverts et mes oreilles attentives à la prière [qu’on fera] de ce lieu;
16 Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
car maintenant j’ai choisi et sanctifié cette maison, afin que mon nom y soit à jamais; et mes yeux et mon cœur seront toujours là.
17 “Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
Et toi, si tu marches devant moi comme a marché David, ton père, pour faire selon tout ce que je t’ai commandé, et si tu gardes mes statuts et mes ordonnances,
18 zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
j’affermirai le trône de ton royaume, selon que j’ai fait alliance avec David, ton père, disant: Tu ne manqueras pas d’un homme pour gouverner Israël.
19 “Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
Mais si vous vous détournez, et que vous abandonniez mes statuts et mes commandements que j’ai mis devant vous, et que vous alliez et serviez d’autres dieux et vous prosterniez devant eux,
20 zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
je vous arracherai de dessus ma terre que je vous ai donnée; et cette maison que j’ai sanctifiée pour mon nom, je la rejetterai de devant ma face, et j’en ferai un proverbe et un sujet de raillerie parmi tous les peuples.
21 Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
Et cette maison, si haut élevée qu’elle soit, quiconque passera près d’elle sera étonné et dira: Pourquoi l’Éternel a-t-il fait ainsi à ce pays et à cette maison?
22 Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’”
Et on dira: Parce qu’ils ont abandonné l’Éternel, le Dieu de leurs pères, qui les fit sortir du pays d’Égypte, et qu’ils se sont attachés à d’autres dieux, et se sont prosternés devant eux et les ont servis: c’est pourquoi il a fait venir sur eux tout ce mal.

< 2 Tarihi 7 >