< 2 Tarihi 7 >
1 Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
Lorsque Salomon eut achevé de prier, le feu descendit du ciel et consuma l’holocauste et les victimes, et la gloire de Yahweh remplit la maison.
2 Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
Les prêtres ne pouvaient entrer dans la maison de Yahweh, car la gloire de Yahweh remplissait sa maison.
3 Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa, “Ubangiji mai alheri ne, ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
Tous les enfants d’Israël virent descendre le feu et la gloire de Yahweh sur la maison et, tombant le visage contre terre sur le pavé, ils se prosternèrent et louèrent Yahweh, en disant: « Car il est bon, car sa miséricorde dure à jamais! »
4 Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
Le roi et tout le peuple offrirent des sacrifices devant Yahweh.
5 Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
Le roi Salomon immola, pour le sacrifice, vingt deux mille bœufs et cent vingt mille brebis. C’est ainsi que le roi et tout le peuple firent la dédicace de la maison de Dieu.
6 Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
Les prêtres se tenaient à leurs postes, et les lévites aussi avec les instruments de musique de Yahweh que le roi David avait faits pour louer Yahweh, « car sa miséricorde dure à jamais! » lorsqu’il célébra Yahweh par leur ministère. Les prêtres sonnaient des trompettes vis-à-vis d’eux, et tout Israël était debout.
7 Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
Salomon consacra le milieu du parvis qui est devant la maison de Yahweh; car il offrit là les holocaustes et les graisses des sacrifices pacifiques, parce que l’autel d’airain qu’il avait fait ne pouvait contenir l’holocauste, l’oblation et les graisses.
8 Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
Salomon célébra la fête en ce temps-là pendant sept jours, et tout Israël avec lui, très grande multitude venue depuis l’entrée d’Emath jusqu’au torrent d’Égypte.
9 A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
Le huitième jour, ils tinrent l’assemblée de clôture; car ils avaient fait la dédicace de l’autel pendant sept jours, et la fête pendant sept jours.
10 A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
Et le vingt troisième jour du septième mois, Salomon renvoya dans ses tentes le peuple joyeux et le cœur content pour le bien que Yahweh avait fait à David, à Salomon et à Israël, son peuple.
11 Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
Salomon acheva la maison de Yahweh et la maison du roi, et il mena à bien tout ce qui lui était venu à l’esprit de faire dans la maison de Yahweh et dans la maison du roi.
12 sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce, “Na ji addu’arka na kuma zaɓi wannan wuri don kaina, a matsayin haikali don hadayu.
Et Yahweh lui apparut pendant la nuit et lui dit: « J’ai exaucé ta prière et j’ai choisi ce lieu comme la maison où l’on m’offrira des sacrifices.
13 “Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
Quand je fermerai le ciel et qu’il n’y aura pas de pluie, quand j’ordonnerai aux sauterelles de dévorer le pays, ou quand j’enverrai la peste dans mon peuple,
14 in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
si mon peuple, sur lequel est invoqué mon nom, s’humilie, prie et cherche ma face, et s’il se détourne de ses mauvaises voies, je l’écouterai du ciel, je lui pardonnerai son péché et je guérirai son pays.
15 Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
Maintenant, mes yeux seront ouverts et mes oreilles attentives à la prière faite en ce lieu.
16 Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
Maintenant je choisis et je sanctifie cette maison, pour que mon nom y réside à jamais, et là seront à jamais mes yeux et mon cœur.
17 “Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
Et toi, si tu marches devant moi comme a marché David, ton père, mettant en pratique tout ce que je t’ai prescrit, et si tu observes mes lois et mes ordonnances,
18 zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
j’affermirai le trône de ta royauté, selon l’alliance que j’ai conclue avec David, ton père, en disant: il ne te manquera jamais un descendant qui règne en Israël.
19 “Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
Mais si vous vous détournez, si vous abandonnez mes lois et mes commandements que j’ai mis devant vous, et si vous allez servir d’autres dieux et vous prosterner devant eux,
20 zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
je les arracherai de mon pays que je leur ai donné; cette maison que j’ai consacrée à mon nom, je la rejetterai de devant ma face, et j’en ferai un sujet de sarcasme et de raillerie parmi tous les peuples.
21 Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
Cette maison qui était si haut placée sera un sujet de stupeur pour quiconque passera près d’elle, et il dira: Pourquoi Yahweh a-t-il ainsi traité ce pays et cette maison?
22 Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’”
Et l’on répondra: Parce qu’ils ont abandonné Yahweh, le Dieu de leurs pères, qui les a fait sortir du pays d’Égypte, et que, s’attachant à d’autres dieux, ils se sont prosternés devant eux et les ont servis; voilà pourquoi il a fait venir sur eux tous ces maux. »