< 2 Tarihi 7 >

1 Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
And when Solomon had made an end of praying, a fire came down from heaven, and consumed the burnt-offering and the sacrifices; and the glory of the Lord filled the house.
2 Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
And the priests were not able to enter into the house of the Lord; because the glory of the Lord had filled the Lord's house.
3 Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa, “Ubangiji mai alheri ne, ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
And all the children of Israel were looking on as the fire came down, and the glory of the Lord [was resting] upon the house; and they kneeled down with their faces to the ground upon the pavement, and prostrated themselves, and gave thanks unto the Lord, for he is good; because unto everlasting endureth his kindness.
4 Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
And the king and all the people offered sacrifices before the Lord.
5 Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
And king Solomon offered a sacrifice of twenty and two thousand oxen, and a hundred and twenty thousand sheep: and so they dedicated the house of God, the king and all the people.
6 Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
And the priests were standing on their stations, and the Levites with the instruments of the music of the Lord, which king David had made to give thanks unto the Lord, because unto everlasting endureth his kindness, with the song of praise of David in their hand; and the priests blew the trumpets opposite to them, and all Israel were standing.
7 Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
And Solomon hallowed the interior of the court that was before the house of the Lord; for he prepared there the burnt-offerings, and the fat of the peace-offerings; because the copper altar which Solomon had made was not able to contain the burnt-offerings, and the meat-offerings, and the fat.
8 Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
And Solomon held the feast at that time seven days, and all Israel with him, a very great assembly, from the entrance of Chamath unto the river of Egypt.
9 A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
And they held on the eighth day a solemn assembly; for the dedication of the altar they held seven days, and the feast seven days.
10 A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
And on the three-and-twentieth day of the seventh month he dismissed the people unto their tents, joyful and glad of heart because of the good that the Lord had done for David, and for Solomon, and for Israel his people.
11 Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
Thus did Solomon complete the house of the Lord, and the king's house; and [in] all that came into Solomon's heart to make in the house of the Lord, and in his own house, he prospered.
12 sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce, “Na ji addu’arka na kuma zaɓi wannan wuri don kaina, a matsayin haikali don hadayu.
Then appeared the Lord to Solomon during the night, and said unto him, I have heard thy prayer, and I have made choice of this place for myself as a house of sacrifice.
13 “Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
If I shut up the heavens that there be no rain, or if I give a charge to the locusts to devour off the land, or if I send a pestilence among my people:
14 in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
And if my people, over whom my name is called, do then humble themselves, and pray, and seek my presence, and turn away from their evil ways: then will I also hear from heaven, and I will forgive their sin, and will heal their land.
15 Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
Now, my eyes shall be open, and my ears attentive unto the prayer on this place.
16 Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
And now I have chosen and hallowed this house, that my name may be there for ever; and my eyes and my heart shall be there at all times.
17 “Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
And as for thee, if thou wilt walk before me, as David thy father hath walked, so as to do in accordance with all that I have commanded thee, and wilt keep my statutes and my ordinances:
18 zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
Then will I establish the throne of thy kingdom, just as I have covenanted with David thy father, saying, There shall never fail thee a man to be ruler in Israel.
19 “Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
But if ye will indeed turn away, and forsake my statutes and my commandments, which I have set before you, and will go and serve other gods, and bow down to them:
20 zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
Then will I pluck them up out of my land which I have given unto them; and this house, which I have hallowed for my name, will I cast away from my sight, and I will render it to be for a proverb and for a by-word among all the people.
21 Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
And this house, which hath been so exalted, shall become an astonishment to every one that passeth by it: so that he will say, Why hath the Lord done thus unto this land, and unto this house?
22 Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’”
And men shall then say, For the cause that they forsook the Lord the God of their fathers, who had brought them forth out of the land of Egypt, and they took hold of other gods, and bowed down to them, and served them: therefore hath he brought upon them all this evil.

< 2 Tarihi 7 >