< 2 Tarihi 7 >
1 Sa’ad da Solomon ya gama yin addu’a, sai wuta ya sauko daga sama ya cinye hadaya ta ƙonawa da kuma sadakokin, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
[祝聖聖殿]撒羅滿祈禱完了,有火從天上降下,焚燒了全燔祭和其他的犧牲;上主的榮耀充滿了聖殿。
2 Firistoci ba su iya shiga haikalin Ubangiji ba domin ɗaukakar Ubangiji ta cika shi.
由於上主的榮耀充滿了上主的殿,司祭不能進入上主的殿。
3 Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ga wutar na saukowa, ɗaukakar Ubangiji kuma tana a bisa haikalin, sai suka durƙusa a dakali da fuskokinsu a ƙasa, suka yi sujada suka kuma yi godiya ga Ubangiji suna cewa, “Ubangiji mai alheri ne, ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.”
所有的以色列子民看見有火降下,上主的榮耀充滿了聖殿,便俯伏在石鋪的地上,叩拜稱頌上主說:「因為他是聖善的,因為他的仁慈永遠常存。」
4 Sai sarki da dukan mutanen suka miƙa hadayu a gaban Ubangiji.
君王和眾百姓在上主面前祭殺了犧牲。
5 Sarki Solomon kuwa ya miƙa hadayar bijimai dubu ashirin da biyu da kuma tumaki da awaki dubu ɗari da dubu ashirin. Ta haka sarki da dukan mutane suka keɓe haikalin Allah.
撒羅滿王那時祭殺了二萬二千頭牛,十二萬隻羊;這樣君王和全百姓為上主的聖殿行了奉獻禮。
6 Firistoci suka ɗauki matsayinsu, haka kuma Lawiyawa suka tsaya a matsayinsu riƙe da kayansu na bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe na Ubangiji, waɗanda Sarki Dawuda ya yi domin yabon Ubangiji. An yi amfani da su sa’ad da ake godiya, ana kuma cewa, “Ƙaunarsa dawwammamiya ce har abada.” Kurkusa da Lawiyawa, firistoci suka busa ƙahoninsu, dukan Isra’ila kuwa suna a tsaye.
司祭各站在自己的岡位上,肋未人拿著達味王所製的上主的樂器,奏「因為他的仁慈永遠常存」稱頌上主的歌;這讚美歌是達味令他們唱的;司祭們面對著他們吹號筒,同時全以色列人都站立不動。
7 Solomon ya tsarkake sashen tsakiya na filin da yake gaban haikalin Ubangiji, a can ya miƙa hadayun ƙonawa da kitsen hadayun salama domin bagaden tagullar da ya yi ba zai iya ɗaukan hadayun ƙonawa, hadayun hatsi da kuma ɓangarori na kitsen ba.
撒羅滿祝聖了上主殿前的內院,在那裏,獻了全燔祭與和平祭的脂油,因為他製造的銅壇容不下那麼多全燔祭、素祭和脂油。
8 Ta haka Solomon ya kiyaye bikin a wannan lokaci har kwana bakwai, dukan Isra’ila kuwa tare da shi, babban taro, mutane daga Lebo Hamat har zuwa Rafin Masar.
那時,撒羅滿舉行慶節七天之久,所有的哈瑪特渡口到埃及小河的以色列百姓,都與他在一起,實是一大集會。
9 A rana ta takwas sai suka yi taro, gama sun yi bikin keɓewar bagade na kwana bakwai da kuma biki na ƙarin kwana bakwai.
第八天又舉行了盛大的集會,如此舉行獻壇七天,過節七天。
10 A rana ta ashirin da uku na watan bakwai sai ya sallami mutane su tafi gidajensu da farin ciki da kuma murna a zuciya saboda abubuwa masu kyau da Ubangiji ya yi domin Dawuda da Solomon da kuma domin mutanensa Isra’ila.
七月二十三日,君王遣散了民眾。他們因上主對達味、撒羅滿和他的百姓以色列所施的恩惠,都滿懷歡樂,回了自己的帳幕。[上主的俯允與警告]
11 Sa’ad da Solomon ya gama haikalin Ubangiji da kuma fadan sarki ya kuma yi nasara a yin dukan abin da yake a zuciyarsa da zai yi a haikalin Ubangiji da kuma a fadarsa,
撒羅滿完成了上主的殿和王宮,凡撒羅滿心中要在上主的殿和自己的宮內所作的,都順利完成了。
12 sai Ubangiji ya bayyana gare shi a daren ya ce, “Na ji addu’arka na kuma zaɓi wannan wuri don kaina, a matsayin haikali don hadayu.
夜間上主顯示給撒羅滿,對他說:「我已聽了你的祈禱,我也為我揀選了這地方作為祭祀的大殿。
13 “Sa’ad da na kulle sammai don kada a yi ruwan sama ko na umarci fāri su cinye amfanin ƙasar ko kuwa na aika da annoba a cikin mutanena,
我如果使天閉塞不雨,使蝗蟲吞吃這地,或使瘟疫在我百姓中間流行,
14 in mutanena, waɗanda ake kira da sunana, sun ƙasƙantar da kansu, suka kuma yi addu’a, suka nemi fuskata, suka kuma juye daga mugayen hanyoyinsu, zan ji daga sama in kuma gafarta zunubinsu in kuwa warkar da ƙasarsu.
這稱為我名下的百姓,如果謙遜祈禱,尋求我的面,遠離自己的惡行,我必從天上俯聽,寬恕他們的罪過,使他們的土地生產。
15 Yanzu, idanuna za su buɗu, kunnuwata kuma za su saurara ga addu’o’in da aka miƙa a wannan wuri.
自今以後,我必睜眼垂顧,側耳諦聽在此處發出的祈禱。
16 Na zaɓi na kuma tsarkake wannan haikali saboda Sunana yă kasance a can har abada. Idanuna da kuma zuciyata kullum za su kasance a can.
現今我已選擇這殿,予以祝聖,使我的名永遠在這殿中;我的眼和我的心,也時時留在那裏。
17 “Game da kai kuwa, in ka yi tafiya a gabana kamar yadda Dawuda mahaifinka ya yi, ka kuma yi dukan abin da na umarta, ka kiyaye ƙa’idodina da dokokina,
至於你,如果你在我面前行走,像你父親達味那樣行走,遵行我吩咐你的一切,恪守我的法律和典章,
18 zan kafa kujerar sarautarka, yadda na alkawarta wa Dawuda mahaifinka sa’ad da na ce, ‘Ba za ka taɓa rasa wani mutumin da zai yi mulki a bisa Isra’ila ba.’
我必鞏固你的王位,一如我應許你父親達味所說:你的子孫中,決斷不了有人作以色列的統治者。
19 “Amma in ka juya daga gare ni ka yashe ƙa’idodi da umarnan da na ba ka, ka yi gaban kanka don ka bauta wa waɗansu alloli ka kuma yi musu sujada,
但是,如果你們遠離我,離棄我在你們前所頒布的法律和誡命,而去服侍敬拜別的神,
20 zan tumɓuke Isra’ila daga ƙasata, wadda na ba su, zan kuma ƙi wannan haikalin da na tsarkake domin Sunana. Zan mai da shi abin karin magana da abin ba’a cikin dukan mutane.
我必將你們從我賜予你們的地上根除,且要拋棄這座為我名而祝聖的殿,毫不顧惜,使它成為萬民的笑話和話柄。
21 Ko da yake wannan haikali yanzu mai girma ne, dukan wanda ya wuce zai kaɗa kai yă ce, ‘Me ya sa Ubangiji ya yi irin wannan abu ga wannan ƙasa da kuma ga wannan haikali?’
這殿雖然宏大,凡經過的人必將驚愕說:上主為什麼這樣對待了這地方和這座殿﹖
22 Mutane za su amsa, ‘Domin sun yashe Ubangiji Allah na kakanninsu, wanda ya fitar da su daga Masar, suka rungumi waɗansu alloli, suna musu sujada, suna bauta musu, shi ya sa ya kawo dukan wannan masifa a kansu.’”
人必回答說:是因為他們離棄了領他們出離埃及地的上主,他們祖先的天主,而歸依、崇拜、服侍了別的神;為此,上主使這一切災禍臨到他們身上。」