< 2 Tarihi 6 >

1 Sa’an nan Solomon ya ce, “Ubangiji ya faɗa cewa zai zauna cikin duhun girgije;
Potem je Salomon rekel: » Gospod je rekel, da bo prebival v gosti temi.
2 na gina ƙasaitaccen haikali dominka, wuri domin ka zauna har abada.”
Toda jaz sem zate zgradil hišo prebivališča in prostor za tvoje prebivanje na veke.«
3 Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
Kralj je obrnil svoj obraz in blagoslovil celotno Izraelovo skupnost in celotna Izraelova skupnost je stala.
4 Sa’an nan ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannuwansa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
Rekel je: »Blagoslovljen bodi Gospod, Izraelov Bog, ki je s svojimi rokami izpolnil to, kar je s svojimi usti govoril mojemu očetu Davidu, rekoč:
5 ‘Tun ranar na da fitar da mutanena daga Masar, ban zaɓi wani birni a wata kabilar Isra’ila don a gina haikali domin Sunana ya kasance a can ba, ba kuwa zaɓi wani yă zama shugaba a bisa jama’ata Isra’ila ba.
›Od dneva, ko sem svoje ljudstvo privedel iz egiptovske dežele, nisem izbral nobenega mesta med vsemi Izraelovimi rodovi, da bi v njem zgradil hišo, da bi bilo tam lahko moje ime niti nisem izbral nobenega človeka, da bi bil vladar nad mojim ljudstvom Izraelom,
6 Amma yanzu na zaɓi Urushalima domin Sunana yă kasance a can, na kuma zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
toda izbral sem Jeruzalem, da bo tam lahko moje ime in izbral sem Davida, da bo nad mojim ljudstvom Izraelom.‹
7 “Mahaifina Dawuda ya yi niyya a zuciyarsa yă gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Torej, to je bilo na srcu mojega očeta Davida, da zgradi hišo za ime Gospoda, Izraelovega Boga.
8 Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Domin yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka kasance da wannan a zuciyarka.
Toda Gospod je mojemu očetu Davidu rekel: ›Ker je bilo to na tvojem srcu, da zgradiš hišo za moje ime, si storil dobro v tem, da je bilo to na tvojem srcu,
9 Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikalin, amma ɗanka wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
vendar hiše ne boš gradil ti, temveč tvoj sin, ki bo izšel iz tvojih ledij, on bo zgradil hišo za moje ime.‹
10 “Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina yanzu kuwa na zauna a kan kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya alkawarta, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Gospod je torej izpolnil svojo besedo, ki jo je govoril, kajti vzdignjen sem na mesto svojega očeta Davida in postavljen sem na Izraelov prestol, kakor je obljubil Gospod in zgradil sem hišo za ime Gospoda, Izraelovega Boga.
11 A can na ajiye akwatin alkawari, inda alkawarin Ubangiji da ya yi da mutanen Isra’ila yake.”
Vanjo sem položil skrinjo, v kateri je Gospodova zaveza, ki jo je sklenil z Izraelovimi otroki.«
12 Sa’an nan Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji a gaban dukan taron Isra’ila ya ɗaga hannuwansa sama.
Stal je pred Gospodovim oltarjem v prisotnosti vse Izraelove skupnosti in razprostrl svoji roki,
13 Dā ma ya riga ya gina dakalin tagulla, mai tsawo kamu biyar, fāɗi kamu biyar da kuma tsayi kamu uku, ya kuma sa shi a tsakiyar filin waje. Ya tsaya a kan dakalin ya kuma durƙusa a gaban dukan taron Isra’ila ya buɗe hannuwansa sama.
kajti Salomon je naredil bronast oder, pet komolcev dolg, pet komolcev širok in tri komolce visok ter ga postavil v sredo dvora. Na njem je stal in pokleknil na svoja kolena pred vso Izraelovo skupnostjo in svoji roki razprostrl proti nebu
14 Ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama da kuma ƙasa, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna tare da bayinka waɗanda suke cin gaba da zuciya ɗaya a hanyarka.
in rekel: »Oh Gospod, Izraelov Bog, tebi ni podobnega Boga ne v nebesih, ne na zemlji, ki se držiš zaveze in izkazuješ usmiljenje svojim služabnikom, ki z vsemi svojimi srci hodijo pred teboj.
15 Ka kiyaye alkawarinka ga bawanka Dawuda mahaifina; da bakinka ka yi alkawari kuma da hannunka ka cika shi, yadda yake a yau.
Ti, ki si ohranil svojemu služabniku Davidu, mojemu očetu, to, kar si mu obljubil in govoriš s svojimi usti in si to izpolnil s svojo roko, kakor je to danes.
16 “Yanzu fa Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka kiyaye wa bawanka Dawuda mahaifina alkawuran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka kāsa kasance da mutumin da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza za su kula cikin dukan abin da suke yi su yi tafiya a gabana bisa ga dokata, kamar yadda ka yi.’
Zdaj torej, oh Gospod, Izraelov Bog, ohrani svojemu služabniku Davidu, mojemu očetu, to, kar si mu obljubil, rekoč: ›Ne bo ti zmanjkalo moža v mojem pogledu, da sedi na Izraelovem prestolu, vendar tako, da bodo tvoji otroci pazili na svojo pot, da hodijo po moji postavi, kakor si ti hodil pred menoj.
17 Yanzu kuwa, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi alkawarta wa bawanka Dawuda yă cika.
Sedaj torej, oh Gospod, Izraelov Bog, naj bo tvoja beseda, ki si jo govoril svojemu služabniku Davidu, podprta.
18 “Amma tabbatacce Allah zai zauna a duniya tare da mutane? Sammai, har ma da saman sammai, ba za su iya riƙe ka ba. Balle wannan haikalin da na gina!
Toda mar bo Bog zagotovo prebival z ljudmi na zemlji? Glej, nebo in nebesa nebes te ne morejo vsebovati, kako veliko manj ta hiša, ki sem jo zgradil!
19 Duk da haka ka mai da hankali ga addu’ar bawanka da kuma roƙo don jinƙai, ya Ubangiji, Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka.
Ozri se na molitev svojega služabnika in k njegovi ponižni prošnji, oh Gospod, moj Bog, da prisluhneš joku in molitvi, ki jo tvoj služabnik moli pred teboj,
20 Bari idanunka su buɗu ta wajen wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce za ka sa Sunanka a can. Bari ka ji addu’ar da bawanka ke yi ta wajen wannan wuri.
da bodo tvoje oči lahko odprte nad to hišo podnevi in ponoči, na kraju, o katerem si rekel, da boš tam položil svoje ime, da prisluhneš molitvi, ki jo tvoj služabnik moli proti temu kraju.
21 Ka ji roƙe-roƙen bawanka da na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a suna duban wajen wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka; kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
Prisluhni torej ponižnim prošnjam svojega služabnika in svojega ljudstva Izraela, ki jih bodo naredili proti temu kraju. Poslušaj iz svojega prebivališča, celó iz nebes in ko slišiš, odpusti.
22 “Sa’ad da mutum ya yi wa maƙwabcinsa laifi aka kuma bukaci ya yi rantsuwa, ya kuma zo ya rantse a gaban bagadenka a cikin wannan haikali,
Če človek greši zoper svojega bližnjega in je prisega položena nanj, ki ga primora priseči in prisega pride pred tvoj oltar v tej hiši,
23 sai ka ji daga sama ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, kana sāka wa mai laifi ta wurin kawo a kansa hakkin abin da ya yi. Ka nuna cewa marar laifi ba shi da laifi, ta haka a fiffita rashin laifinsa.
potem poslušaj iz nebes, stori in sodi [med] svojima služabnikoma s povračilom zlobnemu, tako da položiš njegovo pot na njegovo lastno glavo in opravičiš pravičnega, tako da mu daš glede na njegovo pravičnost.
24 “Sa’ad da an ci mutanenka Isra’ila a yaƙi ta wurin abokin gāba domin sun yi maka zunubi kuma sa’ad da suka juya suka furta sunanka, suna addu’a suka kuma yin roƙe-roƙe a gabanka a wannan haikali,
Če bo tvoje ljudstvo Izrael poraženo pred sovražnikom, ker so grešili zoper tebe in se bo vrnilo ter priznalo tvoje ime in molilo in naredilo ponižno prošnjo pred teboj v tej hiši,
25 sai ka ji daga sama ka kuma gafarta zunubin mutanenka Isra’ila ka kuma dawo da su zuwa ƙasar da ka ba su da kuma kakanninsu.
tedaj prisluhni iz nebes in odpusti greh svojega ljudstva Izraela ter jih ponovno privedi v deželo, ki si jo dal njim in njihovim očetom.
26 “Sa’ad da sammai suka rufu ba kuwa ruwan sama saboda mutanenka sun yi maka zunubi, sa’ad da kuwa suka yi addu’a suna duban waje wannan wuri suka kuma furta sunanka suka juye daga zunubinsu domin ka azabta su,
Ko je nebo zaprto in ni dežja, ker so grešili zoper tebe; vendar če molijo proti temu kraju in priznajo tvoje ime in se odvrnejo od svojega greha, ko si jih prizadel,
27 sai ka ji daga sama ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace da za su yi zama, ka kuma aika ruwan sama a ƙasar da ka ba mutanenka gādo.
potem poslušaj iz nebes in odpusti greh svojih služabnikov in svojega ljudstva Izraela, ko si jih učil dobre poti, po kateri naj bi hodili in pošlji dež na svojo deželo, ki si jo dal svojemu ljudstvu za dediščino.
28 “Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko wahala ko fumfuna, ko fāra ko fāra ɗango, ko sa’ad da abokan gāba sun yi musu ƙawanya a kowane daga biranensu, dukan wata masifa ko cutar da za tă zo,
Če bo v deželi pomanjkanje, kužna bolezen, če bo kvarjenje ali plesen, leteče kobilice ali gosenice, če jih njihovi sovražniki oblegajo v mestih njihove dežele, kakršenkoli udarec ali kakršnakoli bolezen bo tam,
29 sa’ad da kuwa wani cikin mutanenka Isra’ila ya yi wata addu’a ko roƙo, kowa yana sane a azabarsa da kuma zafinsa, yana buɗe hannuwansa yana duban wajen wannan haikali,
potem kakršnakoli molitev ali kakršnakoli ponižna prošnja bo narejena od kateregakoli človeka ali od vsega tvojega ljudstva Izraela, ko bo vsak spoznal svoj lastni udarec in svojo lastno bolečino in bo razprostrl svoji roki v tej hiši,
30 sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi da kowane mutum gwargwadon duk abin da yake yi, da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan mutane),
tedaj prisluhni iz nebes, svojega prebivališča, odpusti in povrni vsakemu človeku glede na njegove lastne poti, katerega srce ti poznaš (kajti samo ti poznaš srca človeških otrok),
31 don su ji tsoronka su kuma yi tafiya a hanyoyinka a kowane lokacin da suke zama a ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
da se te bodo lahko bali, da hodijo po tvojih poteh tako dolgo, dokler živijo v deželi, ki si jo dal našim očetom.
32 “Game da baƙo wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba kuwa amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka mai girma da kuma hannunka mai iko da hannunka mai ƙarfi, sa’ad da ya zo ya yi addu’a yana duban wannan haikali,
Poleg tega glede tujca, ki ni iz tvojega ljudstva Izraela, temveč je prišel iz daljne dežele zaradi tvojega velikega imena, tvoje mogočne roke in tvojega iztegnjenega lakta; če pridejo in molijo v tej hiši,
33 sai ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi duk abin da baƙon ya nemi ka yi, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, su kuma san cewa wannan gidan da na gina na Sunanka ne.
tedaj prisluhni iz nebes, celó iz svojega prebivališča in stôri glede na vse, za kar tujec kliče k tebi, da bo vse ljudstvo zemlje poznalo tvoje ime in se te balo kakor tvoje ljudstvo Izrael in bo lahko vedelo, da je ta hiša, ki sem jo zgradil, imenovana po tvojem imenu.
34 “Sa’ad da mutanenka suka je yaƙi da abokan gābansu, ko’ina ka kai su, kuma sa’ad da suka yi addu’a gare ka suna duban wannan birnin da ka zaɓa da haikalin nan da na gina domin Sunanka,
Če gre tvoje ljudstvo na vojno zoper svoje sovražnike po poti, po kateri jih boš poslal in molijo k tebi obrnjeni k temu mestu, ki si ga izbral in k hiši, ki sem jo zgradil za tvoje ime,
35 sai ka ji addu’arsu da kuma roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatarsu.
tedaj prisluhni iz nebes njihovi molitvi in njihovim ponižnim prošnjam ter obravnavaj njihov primer.
36 “Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wani wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su ka miƙa su ga abokin gāba, wanda ya kai su zaman bauta a ƙasa mai nisa ko kuwa kusa;
Če grešijo zoper tebe (kajti nobenega človeka ni, ki ne greši) in si jezen nad njimi in jih izročiš pred njihove sovražnike in jih oni ujete odvedejo v deželo daleč proč ali blizu,
37 Kuma in suka canja zuciya a cikin ƙasar da suke zaman bauta, suka tuba suka roƙe ka a ƙasar zaman bautarsu suka kuma ce, ‘Mun yi zunubi, mu yi abin da ba daidai ba, mu kuwa yi mugunta’;
vendar če si premislijo v deželi, kamor so odvedeni ujetniki in se obrnejo in molijo k tebi v deželi svojega ujetništva, rekoč: ›Grešili smo, napačno smo storili in počeli zlobno; ‹
38 in kuma sun juye gare ka da dukan zuciyarsu da ransu a ƙasar zaman bautarsu inda aka kai su, suka kuma dubi wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, wajen birnin da ka zaɓa da kuma wajen haikalin da na gina domin Sunanka;
če se vrnejo k tebi z vsem svojim srcem in z vso svojo dušo, v deželi svojega ujetništva, kamor so jih odvedli ujete in molijo k njihovi deželi, ki si jo dal njihovim očetom in k mestu, ki si ga izbral in k hiši, ki sem jo zgradil za tvoje ime,
39 to, daga sama, mazauninka, sai ka ji addu’arsu da kuma roƙe-roƙensu, ka kuwa biya musu bukatunsu. Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi.
tedaj prisluhni iz nebes, celó iz svojega prebivališča, njihovi molitvi in njihovim ponižnim prošnjam in obravnavaj njihov primer in odpusti svojemu ljudstvu, ki je grešilo zoper tebe.
40 “Yanzu, Allahna, bari idanunka su buɗu kunnuwanka kuma su saurara ga addu’o’in da ake miƙa a wannan wuri.
Sedaj, moj Bog, naj bodo, rotim te, tvoje oči odprte in naj bodo tvoja ušesa pozorna na molitev, ki je narejena na tem kraju.
41 “Yanzu ka tashi, ya Ubangiji Allah, ka zo wurin hutunka,
Sedaj torej vzdigni se, oh Gospod Bog, v svoje počivališče, ti in skrinja tvoje moči. Naj bodo tvoji duhovniki, oh Gospod Bog, oblečeni z rešitvijo duš in naj se tvoji sveti veselijo v dobroti.
42 Ya Ubangiji Allah, kada ka ƙyale shafaffenka.
Oh Gospod Bog, svojega obraza ne obrni od svojega maziljenca. Spomni se usmiljenj svojega služabnika Davida.‹«

< 2 Tarihi 6 >