< 2 Tarihi 6 >
1 Sa’an nan Solomon ya ce, “Ubangiji ya faɗa cewa zai zauna cikin duhun girgije;
Le hoe t’i Selomò: Fa nafè’ Iehovà t’ie ho nimoneñe añ’ ieñe mingeo ao.
2 na gina ƙasaitaccen haikali dominka, wuri domin ka zauna har abada.”
Fe nandranjieko anjombam-pimoneñan-dRehe, toetse hitobea’o nainai’e.
3 Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
Nampitoli-daharañe amy zao i mpanjakay naho nitata i valobohò’ Israele iabiy, ie fonga nijohañe eo i fivoribei’ Israeley.
4 Sa’an nan ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannuwansa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
Le hoe re: Andriañeñe t’Iehovà, Andrianañahare’ Israele nitsara am-palie amy Davide raeko vaho nihenefem-pità’e, ami’ty hoe:
5 ‘Tun ranar na da fitar da mutanena daga Masar, ban zaɓi wani birni a wata kabilar Isra’ila don a gina haikali domin Sunana ya kasance a can ba, ba kuwa zaɓi wani yă zama shugaba a bisa jama’ata Isra’ila ba.
Sikal’ amy andro nampiavotako an-tane Mitsraime añe ondatikooy, tsy eo ty rova jinoboko amo fifokoa’ Israeleo hañamboarako anjomba, te ho ao ty añarako; vaho tsy ia t’indaty jinoboko ho mpifehe’ ondatiko Israeleo
6 Amma yanzu na zaɓi Urushalima domin Sunana yă kasance a can, na kuma zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
naho tsy e Ierosalaime ao ty jinoboko hanoako ty añarako naho tsy i Davide ty jinoboko hifelek’ ondatiko Israeleo.
7 “Mahaifina Dawuda ya yi niyya a zuciyarsa yă gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Ie amy zao tañ’ arofo’ i Davide raeko t’ie hamboatse anjomba ho amy tahina’ Iehovà Andrianañahare’ Israeley.
8 Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Domin yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka kasance da wannan a zuciyarka.
Fe hoe t’Iehovà aman-Davide raeko: Ndra te añ’ arofo’o ty handranjy anjomba ho ami’ty añarako toe nanoe’o soa t’ie tami’ty tañ’ arofo’o;
9 Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikalin, amma ɗanka wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
tsy ihe ty hamboatse i anjombay, fa hamboare’ i ana’o hiboak’ am-bania’oy, ty akiba ho ami’ty añarako.
10 “Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina yanzu kuwa na zauna a kan kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya alkawarta, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Aa le najado’ Iehovà i tsara’ tsinara’ey; izaho ty nitroatse amy toe’ i Davide raekoy, le fa mitobok’ am-piambesa’ Israele, ty amy tsara’ Iehovày vaho fa nandranjiako anjomba ho ami’ty tahina’ Iehovà Andrianañahare’ Israele.
11 A can na ajiye akwatin alkawari, inda alkawarin Ubangiji da ya yi da mutanen Isra’ila yake.”
Le fa napoko ao i vata amam-pañina nifanoa’ Iehovà amo ana’ Israeleoy.
12 Sa’an nan Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji a gaban dukan taron Isra’ila ya ɗaga hannuwansa sama.
Aa le nijohañe aolo’ i kitreli’ Iehovà añatrefa’ i valobohò’ Israele iabiy re namelatse o fità’eo—
13 Dā ma ya riga ya gina dakalin tagulla, mai tsawo kamu biyar, fāɗi kamu biyar da kuma tsayi kamu uku, ya kuma sa shi a tsakiyar filin waje. Ya tsaya a kan dakalin ya kuma durƙusa a gaban dukan taron Isra’ila ya buɗe hannuwansa sama.
Toe fa nandranjy rairay torisike t’i Selomò, kiho lime ty andava’e, kiho lime ty ampohe’e naho kiho telo ty haabo’e vaho napo’e añivo’ i kiririsay; eo ty nijohaña’e naho nitongalefa’e añ’ ongotse añatrefa’ i valobohò’ Israeley namela-pitàñe mb’ andikerañe ey,
14 Ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama da kuma ƙasa, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna tare da bayinka waɗanda suke cin gaba da zuciya ɗaya a hanyarka.
vaho nanao ty hoe, Ry Iehovà Andrianañahare’ Israeleo, tsy aman’ Añahare manahak’ azo ty andindiñe ao ndra an-tane atoy, ty mahatam-pañina vaho manolotse fiferenaiñañe amo mpitoro’o mañavelo añatrefa’o an-kaliforan’arofoo;
15 Ka kiyaye alkawarinka ga bawanka Dawuda mahaifina; da bakinka ka yi alkawari kuma da hannunka ka cika shi, yadda yake a yau.
ie fa nifahara’o aman-draeko Davide mpitoro’o i nampitama’o azey, Eka toe tsinara’o am-palie vaho nihenefa’o am-pitàñe, le ie henanekeo.
16 “Yanzu fa Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka kiyaye wa bawanka Dawuda mahaifina alkawuran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka kāsa kasance da mutumin da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza za su kula cikin dukan abin da suke yi su yi tafiya a gabana bisa ga dokata, kamar yadda ka yi.’
Ie amy zao ry Iehovà, Andrianañahare’ Israele, tambozoro i nitsarae’o amy mpitoro’o Davide raekoy, ty hoe: Tsy ho po-ondaty am-pahaisahako eo ty hiambesatse amy fiambesa’ Israeley naho songa hañambeñe ty lala’e o ana’oo hañavelo amy Hake natolokoy manahake i nañaveloa’o aolokoy.
17 Yanzu kuwa, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi alkawarta wa bawanka Dawuda yă cika.
Aa le venteo i tsara’oy henaneo ry Iehovà Andrianañahare’ Israele, i tsinara’o amy mpitoro’o Davideiy.
18 “Amma tabbatacce Allah zai zauna a duniya tare da mutane? Sammai, har ma da saman sammai, ba za su iya riƙe ka ba. Balle wannan haikalin da na gina!
Aa vaho toe himoneñe am’ondaty an-tane atoio hao t’i Andrianañahare, ie tsy tsahats’ Azo o andindin-dikerañeo, àntsake o anjomba rinanjikoo?
19 Duk da haka ka mai da hankali ga addu’ar bawanka da kuma roƙo don jinƙai, ya Ubangiji, Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka.
Fe mb’e haoñe’o ty filolofam-pitoro’o naho i fihalalia’ey, ry Iehovà Andrianañahareko, hahajanjiñe ty toreo naho soloho isolohoa’ ty mpitoro’o añatrefa’o etoy;
20 Bari idanunka su buɗu ta wajen wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce za ka sa Sunanka a can. Bari ka ji addu’ar da bawanka ke yi ta wajen wannan wuri.
te hisokake mb’ami’ty anjomba toy handro an-kaleñe o fihaino’oo, mb’amy toetse nanoe’o ty hoe te hapo’o ao i tahina’oiy, hijanjiña’o o halaly ihalalia’ o mpitoro’oo mb’ amy toetse toio;
21 Ka ji roƙe-roƙen bawanka da na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a suna duban wajen wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka; kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
naho ho haoñe’o o solohom-pitoro’oo naho ondati’o Israeleo, ie hihalaly mb’ ami’ty toetse toy; eka, mijanjiña am-pimoneña’o andikerañ’ ao; le ie mijanjin-dRehe, afaho.
22 “Sa’ad da mutum ya yi wa maƙwabcinsa laifi aka kuma bukaci ya yi rantsuwa, ya kuma zo ya rantse a gaban bagadenka a cikin wannan haikali,
Aa naho manao hakeo ama’ ondaty t’indaty naho ampititiheñe am-panta naho miheo mb’ añ’ anjomba’o mb’etoa vaho mifanta añ’ atrefa’ i kitreliy;
23 sai ka ji daga sama ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, kana sāka wa mai laifi ta wurin kawo a kansa hakkin abin da ya yi. Ka nuna cewa marar laifi ba shi da laifi, ta haka a fiffita rashin laifinsa.
le mijanjiña andindiñe ao naho ano vaho zakao an-katò o mpitoro’oo, le ondroho an-doha’ i tsivokatsey i sata’ey vaho hahao ty vantañe, le anoloro ty amy havantaña’ey.
24 “Sa’ad da an ci mutanenka Isra’ila a yaƙi ta wurin abokin gāba domin sun yi maka zunubi kuma sa’ad da suka juya suka furta sunanka, suna addu’a suka kuma yin roƙe-roƙe a gabanka a wannan haikali,
Aa naho linafa ambane aolo’ o rafelahi’eo ondati’o Israeleo, ie anaña’o hakeo vaho mitolike mamela-pitàn-droe, miantoke ty tahina’o, mihalaly naho misoloho ama’o mbañ’ anjomba’o atoy;
25 sai ka ji daga sama ka kuma gafarta zunubin mutanenka Isra’ila ka kuma dawo da su zuwa ƙasar da ka ba su da kuma kakanninsu.
le mijanjiña an-dindiñ’ao naho apoho ty tahi’ ondati’o Israeleo vaho ampolio mb’ an-tane natolo’o iareo naho aman-droae’ iareo.
26 “Sa’ad da sammai suka rufu ba kuwa ruwan sama saboda mutanenka sun yi maka zunubi, sa’ad da kuwa suka yi addu’a suna duban waje wannan wuri suka kuma furta sunanka suka juye daga zunubinsu domin ka azabta su,
Aa naho mirindriñe i likerañey naho tsy avy i orañey, amy te nanao tahiñe ama’o iereo, le ie mihalaly mb’ami’ty toetse toy naho mamela-pitàñe miantoke i tahina’o naho mitolik’ amy hakeo’ iareoy, ie fa nilafae’o,
27 sai ka ji daga sama ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace da za su yi zama, ka kuma aika ruwan sama a ƙasar da ka ba mutanenka gādo.
le mijanjiña an-dindiñe ao vaho apoho ty hakeo’ o mpitoro’oo naho ondati’o Israeleo, le tehafo mb’an-dalan-tsoa fañaveloañe; le mampahavia orañe an-tane’o nampandovae’o ondati’oo.
28 “Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko wahala ko fumfuna, ko fāra ko fāra ɗango, ko sa’ad da abokan gāba sun yi musu ƙawanya a kowane daga biranensu, dukan wata masifa ko cutar da za tă zo,
Aa naho mametsa-kasalikoañe i taney, he te voa ty angorosy, ke ty pozy ndra tromambo, ke ty valala ndra ty oletse; hera arikatoha’ o rafelahi’eo an-tane ndra an-drova’ iareo ao; ndra kiria inoñe ndra hatindriañ’ inoñe;
29 sa’ad da kuwa wani cikin mutanenka Isra’ila ya yi wata addu’a ko roƙo, kowa yana sane a azabarsa da kuma zafinsa, yana buɗe hannuwansa yana duban wajen wannan haikali,
le ze halaly naho soloho anoa’ t’indaty, ndra ondati’o Israele iabio, ie songa mahafohiñe i arete’ey naho i fangirifiri’ey vaho mamela-pitàñe mb’ ami’ty anjomba toy;
30 sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi da kowane mutum gwargwadon duk abin da yake yi, da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan mutane),
le mijanjiña boak’ am-pimoneña’o andikerañe añe, le songa anoloro ty amo hene sata’eo, ie arofoana’o ty arofo’e —amy te Ihe avao ro maharofoanañe o arofon’ ana’ ondatio—
31 don su ji tsoronka su kuma yi tafiya a hanyoyinka a kowane lokacin da suke zama a ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
soa te hañeveña’e, hañavelo amo lala’oo amy ze hene andro iveloma’e amy tane natolo’o aman-droae’aiy.
32 “Game da baƙo wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba kuwa amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka mai girma da kuma hannunka mai iko da hannunka mai ƙarfi, sa’ad da ya zo ya yi addu’a yana duban wannan haikali,
Le o renetane tsy am’ ondati’o Israeleoo, ie pok’eo boak’ an-tsietoitane añe ty amy tahina’o ra’elahiy naho ty fità’o maozatse vaho ty fità’o natorakitsy le ie mb’ etoa hihalaly mb’ ami’ty anjomba toy;
33 sai ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi duk abin da baƙon ya nemi ka yi, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, su kuma san cewa wannan gidan da na gina na Sunanka ne.
le mijanjiña am-pimoneña’o an-dikerañe añe, le ano ze hene ikanjia’ i renetaney; soa te fonga hahafohiñe ty tahina’o ondati’ ty tane toio naho hañeveñe manahake ondati’o Israeleo vaho ho fohi’ iereo te kanjiañe ami’ty anjomba namboareko toy i tahina’oy.
34 “Sa’ad da mutanenka suka je yaƙi da abokan gābansu, ko’ina ka kai su, kuma sa’ad da suka yi addu’a gare ka suna duban wannan birnin da ka zaɓa da haikalin nan da na gina domin Sunanka,
Aa ie mionjomb’ an-kotakotak’ amo rafelahi’eo ondati’oo, mb’amy ze lalañe añiraha’o iareo naho mihalaly ama’o mb’ami’ty rova jinobo’o toy naho mb’ ami’ ty anjomba niranjieko ho amy tahina’o toy;
35 sai ka ji addu’arsu da kuma roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatarsu.
le janjiño i halali’ iareoy naho o soloho’ iareoo vaho henefo ty fitsakorean-tro’ iareo.
36 “Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wani wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su ka miƙa su ga abokin gāba, wanda ya kai su zaman bauta a ƙasa mai nisa ko kuwa kusa;
Aa ie anaña’o tahiñe (toe tsy eo t’indaty tsy mandilatse) naho iviñera’o naho atolo’o amo rafelahi’ iareoo vaho asese an-drohy mb’an-tane lavits’ añe ndra marine eo;
37 Kuma in suka canja zuciya a cikin ƙasar da suke zaman bauta, suka tuba suka roƙe ka a ƙasar zaman bautarsu suka kuma ce, ‘Mun yi zunubi, mu yi abin da ba daidai ba, mu kuwa yi mugunta’;
f’ie mitsakore an-trok’ao an-tane naneseañe iareo an-drohy añe naho mitolike, misoloho ama’o an-tanem-pandrohiza’ iareo ao, manao ty hoe: Nandilatse zahay, nitoloñ’ an-tahiñe, nanao hakeo;
38 in kuma sun juye gare ka da dukan zuciyarsu da ransu a ƙasar zaman bautarsu inda aka kai su, suka kuma dubi wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, wajen birnin da ka zaɓa da kuma wajen haikalin da na gina domin Sunanka;
le ie mimpoly ama’o an-kaampon’arofo naho an-kaliforam-pañova, an-tanem-pandrohizañ’ ao, amy naneseañe iareo an-drohiy vaho mihalaly mb’ amy tane natolo’o aman-droae’ iareoy naho mb’amy rova jinobo’oy, mb’amo anjomba niranjieko amy tahina’oio,
39 to, daga sama, mazauninka, sai ka ji addu’arsu da kuma roƙe-roƙensu, ka kuwa biya musu bukatunsu. Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi.
le mijanjiña an-dindiñey, am-pimoneña’o ao, o halali’ iareoo naho o soloho’ iareoo, le añomezo to ty amo enta’ iareoo; vaho apoho ty hakeo’ ondati’o nandilatse ama’oo.
40 “Yanzu, Allahna, bari idanunka su buɗu kunnuwanka kuma su saurara ga addu’o’in da ake miƙa a wannan wuri.
Ie henane zao, ry Andrianañahareko, ehe te hisokake o fihaino’oo naho ho janjiñen-dravembia’o ty halaly taroñeñe ami’ty toetse toy.
41 “Yanzu ka tashi, ya Ubangiji Allah, ka zo wurin hutunka,
Aa le miongaha mb’an-toem-pitofà’o eo ry Iehovà Andrianañahare, Ihe naho ty vatan-kaozara’o; Ee te hisarom-pandrombahañe abey ry Iehovà Andrianañahare, o mpisoro’oo, le hirebek’ ami’ty hasoa o noro’oo.
42 Ya Ubangiji Allah, kada ka ƙyale shafaffenka.
O ry Iehovà Andrianañahare, ko ampiolire’o ty lahara’ i noriza’oy; tiahio o fiferenaiña i Davide mpitoro’oo.