< 2 Tarihi 6 >
1 Sa’an nan Solomon ya ce, “Ubangiji ya faɗa cewa zai zauna cikin duhun girgije;
Alors Salomon dit: « Yahvé a dit qu'il habiterait dans les ténèbres épaisses.
2 na gina ƙasaitaccen haikali dominka, wuri domin ka zauna har abada.”
Mais moi, je t'ai construit une maison et un foyer, un lieu où tu pourras habiter à jamais. »
3 Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
Le roi tourna son visage, et il bénit toute l'assemblée d'Israël; et toute l'assemblée d'Israël se tint debout.
4 Sa’an nan ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannuwansa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
Il dit: Béni soit Yahvé, le Dieu d'Israël, qui a parlé de sa bouche à David, mon père, et qui l'a accompli de ses mains, en disant:
5 ‘Tun ranar na da fitar da mutanena daga Masar, ban zaɓi wani birni a wata kabilar Isra’ila don a gina haikali domin Sunana ya kasance a can ba, ba kuwa zaɓi wani yă zama shugaba a bisa jama’ata Isra’ila ba.
Depuis le jour où j'ai fait sortir mon peuple du pays d'Égypte, je n'ai choisi dans toutes les tribus d'Israël aucune ville pour y bâtir une maison, afin que mon nom y fût établi, et je n'ai choisi aucun homme pour être prince sur mon peuple d'Israël.
6 Amma yanzu na zaɓi Urushalima domin Sunana yă kasance a can, na kuma zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
Mais maintenant, j'ai choisi Jérusalem, afin que mon nom y soit établi, et j'ai choisi David pour être prince sur mon peuple d'Israël.
7 “Mahaifina Dawuda ya yi niyya a zuciyarsa yă gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Or, le cœur de David, mon père, était de bâtir une maison au nom de l'Éternel, le Dieu d'Israël.
8 Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Domin yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka kasance da wannan a zuciyarka.
Mais l'Éternel dit à David, mon père: « Tu as bien fait de bâtir une maison pour mon nom, puisque c'était dans ton cœur;
9 Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikalin, amma ɗanka wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
mais ce n'est pas toi qui bâtiras la maison, c'est ton fils, qui sortira de ton corps, qui bâtira la maison pour mon nom ».
10 “Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina yanzu kuwa na zauna a kan kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya alkawarta, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
« Yahvé a accompli la parole qu'il avait prononcée, car je me suis levé à la place de David, mon père, et je me suis assis sur le trône d'Israël, comme Yahvé l'avait promis, et j'ai bâti la maison au nom de Yahvé, le Dieu d'Israël.
11 A can na ajiye akwatin alkawari, inda alkawarin Ubangiji da ya yi da mutanen Isra’ila yake.”
J'y ai placé l'arche, dans laquelle se trouve l'alliance de Yahvé, qu'il a conclue avec les enfants d'Israël. »
12 Sa’an nan Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji a gaban dukan taron Isra’ila ya ɗaga hannuwansa sama.
Il se tint devant l'autel de Yahvé, en présence de toute l'assemblée d'Israël, et il étendit les mains
13 Dā ma ya riga ya gina dakalin tagulla, mai tsawo kamu biyar, fāɗi kamu biyar da kuma tsayi kamu uku, ya kuma sa shi a tsakiyar filin waje. Ya tsaya a kan dakalin ya kuma durƙusa a gaban dukan taron Isra’ila ya buɗe hannuwansa sama.
(car Salomon avait fait une plate-forme d'airain, longue de cinq coudées, large de cinq coudées et haute de trois coudées, et il l'avait placée au milieu du parvis; il s'y tint debout, se mit à genoux devant toute l'assemblée d'Israël, et étendit les mains vers le ciel).
14 Ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama da kuma ƙasa, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna tare da bayinka waɗanda suke cin gaba da zuciya ɗaya a hanyarka.
Il dit alors: « Yahvé, Dieu d'Israël, il n'y a pas de Dieu comme toi, ni dans les cieux ni sur la terre, toi qui gardes l'alliance et la bonté envers tes serviteurs qui marchent devant toi de tout leur cœur,
15 Ka kiyaye alkawarinka ga bawanka Dawuda mahaifina; da bakinka ka yi alkawari kuma da hannunka ka cika shi, yadda yake a yau.
toi qui as gardé envers ton serviteur David, mon père, ce que tu lui avais promis. Oui, tu as parlé de ta bouche, et tu l'as accompli de ta main, comme il en est aujourd'hui.
16 “Yanzu fa Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka kiyaye wa bawanka Dawuda mahaifina alkawuran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka kāsa kasance da mutumin da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza za su kula cikin dukan abin da suke yi su yi tafiya a gabana bisa ga dokata, kamar yadda ka yi.’
Maintenant, Yahvé, le Dieu d'Israël, garde pour ton serviteur David, mon père, ce que tu lui as promis, en disant: Tu ne manqueras pas d'un homme à mes yeux pour s'asseoir sur le trône d'Israël, si seulement tes enfants prennent garde à leur voie, pour marcher dans ma loi comme tu as marché devant moi.
17 Yanzu kuwa, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi alkawarta wa bawanka Dawuda yă cika.
Maintenant, Yahvé, le Dieu d'Israël, que s'accomplisse ta parole, celle que tu as dite à ton serviteur David.
18 “Amma tabbatacce Allah zai zauna a duniya tare da mutane? Sammai, har ma da saman sammai, ba za su iya riƙe ka ba. Balle wannan haikalin da na gina!
« Mais Dieu habitera-t-il vraiment avec les hommes sur la terre? Voici que le ciel et le ciel des cieux ne peuvent te contenir; combien moins cette maison que j'ai bâtie!
19 Duk da haka ka mai da hankali ga addu’ar bawanka da kuma roƙo don jinƙai, ya Ubangiji, Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka.
Mais écoute la prière de ton serviteur et sa supplique, Yahvé mon Dieu, pour écouter le cri et la prière que ton serviteur adresse devant toi;
20 Bari idanunka su buɗu ta wajen wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce za ka sa Sunanka a can. Bari ka ji addu’ar da bawanka ke yi ta wajen wannan wuri.
afin que tes yeux soient ouverts jour et nuit vers cette maison, vers le lieu où tu as dit que tu mettrais ton nom, pour écouter la prière que ton serviteur adressera à ce lieu.
21 Ka ji roƙe-roƙen bawanka da na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a suna duban wajen wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka; kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
Écoute les prières de ton serviteur et de ton peuple d'Israël, quand ils prieront vers ce lieu. Oui, écoute de ta demeure, du ciel, et quand tu auras entendu, pardonne.
22 “Sa’ad da mutum ya yi wa maƙwabcinsa laifi aka kuma bukaci ya yi rantsuwa, ya kuma zo ya rantse a gaban bagadenka a cikin wannan haikali,
« Si un homme pèche contre son prochain, et qu'on lui fasse prêter serment pour qu'il jure, et qu'il vienne jurer devant ton autel dans cette maison,
23 sai ka ji daga sama ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, kana sāka wa mai laifi ta wurin kawo a kansa hakkin abin da ya yi. Ka nuna cewa marar laifi ba shi da laifi, ta haka a fiffita rashin laifinsa.
alors écoute du ciel, agis, et juge tes serviteurs, en faisant retomber le méchant sur sa tête, et en justifiant le juste, pour lui rendre selon sa justice.
24 “Sa’ad da an ci mutanenka Isra’ila a yaƙi ta wurin abokin gāba domin sun yi maka zunubi kuma sa’ad da suka juya suka furta sunanka, suna addu’a suka kuma yin roƙe-roƙe a gabanka a wannan haikali,
Si ton peuple d'Israël est battu par l'ennemi parce qu'il a péché contre toi, s'il revient à lui et confesse ton nom, s'il prie et t'adresse des supplications dans cette maison,
25 sai ka ji daga sama ka kuma gafarta zunubin mutanenka Isra’ila ka kuma dawo da su zuwa ƙasar da ka ba su da kuma kakanninsu.
entends des cieux, pardonne le péché de ton peuple d'Israël et fais-le revenir dans le pays que tu lui as donné, à lui et à ses pères.
26 “Sa’ad da sammai suka rufu ba kuwa ruwan sama saboda mutanenka sun yi maka zunubi, sa’ad da kuwa suka yi addu’a suna duban waje wannan wuri suka kuma furta sunanka suka juye daga zunubinsu domin ka azabta su,
« Quand le ciel est fermé et qu'il n'y a pas de pluie parce qu'ils ont péché contre toi, s'ils prient vers ce lieu et confessent ton nom, et s'ils se détournent de leur péché quand tu les affliges,
27 sai ka ji daga sama ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace da za su yi zama, ka kuma aika ruwan sama a ƙasar da ka ba mutanenka gādo.
alors écoute dans les cieux, et pardonne le péché de tes serviteurs, ton peuple d'Israël, quand tu leur enseignes la bonne voie dans laquelle ils doivent marcher, et fais tomber la pluie sur ton pays, que tu as donné en héritage à ton peuple.
28 “Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko wahala ko fumfuna, ko fāra ko fāra ɗango, ko sa’ad da abokan gāba sun yi musu ƙawanya a kowane daga biranensu, dukan wata masifa ko cutar da za tă zo,
« S'il y a de la famine dans le pays, s'il y a de la peste, s'il y a du mildiou ou de la rouille, des sauterelles ou des chenilles, si leurs ennemis les assiègent dans le pays de leurs villes; quelque fléau ou quelque maladie qu'il y ait -
29 sa’ad da kuwa wani cikin mutanenka Isra’ila ya yi wata addu’a ko roƙo, kowa yana sane a azabarsa da kuma zafinsa, yana buɗe hannuwansa yana duban wajen wannan haikali,
quelque prière et quelque supplication que fasse un homme, ou tout ton peuple d'Israël, qui connaisse son propre fléau et sa propre douleur, et qui étende ses mains vers cette maison,
30 sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi da kowane mutum gwargwadon duk abin da yake yi, da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan mutane),
alors écoute du ciel, ta demeure, et pardonne, et rends à chacun selon toutes ses voies, le cœur que tu connais (car toi seul connais le cœur des enfants des hommes),
31 don su ji tsoronka su kuma yi tafiya a hanyoyinka a kowane lokacin da suke zama a ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
afin qu'ils te craignent, pour marcher dans tes voies, tant qu'ils vivront dans le pays que tu as donné à nos pères.
32 “Game da baƙo wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba kuwa amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka mai girma da kuma hannunka mai iko da hannunka mai ƙarfi, sa’ad da ya zo ya yi addu’a yana duban wannan haikali,
« Pour ce qui est de l'étranger qui n'est pas de ton peuple d'Israël, lorsqu'il vient d'un pays lointain, à cause de ton grand nom, de ta main puissante et de ton bras étendu, lorsqu'il vient prier pour cette maison,
33 sai ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi duk abin da baƙon ya nemi ka yi, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, su kuma san cewa wannan gidan da na gina na Sunanka ne.
écoute du ciel, de ta demeure, et fais tout ce pour quoi l'étranger t'appelle, afin que tous les peuples de la terre connaissent ton nom et te craignent, comme ton peuple d'Israël, et qu'ils sachent que cette maison que j'ai bâtie est appelée de ton nom.
34 “Sa’ad da mutanenka suka je yaƙi da abokan gābansu, ko’ina ka kai su, kuma sa’ad da suka yi addu’a gare ka suna duban wannan birnin da ka zaɓa da haikalin nan da na gina domin Sunanka,
« Si ton peuple part en guerre contre ses ennemis, par quelque moyen que tu l'envoies, et qu'il te prie en direction de cette ville que tu as choisie et de la maison que j'ai bâtie pour ton nom,
35 sai ka ji addu’arsu da kuma roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatarsu.
exauce du haut des cieux sa prière et sa supplication, et fais-lui droit.
36 “Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wani wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su ka miƙa su ga abokin gāba, wanda ya kai su zaman bauta a ƙasa mai nisa ko kuwa kusa;
S'ils ont péché contre toi, car il n'y a pas d'homme qui ne pèche pas, si tu t'es mis en colère contre eux et si tu les as livrés à l'ennemi, qui les a emmenés captifs dans un pays lointain ou proche,
37 Kuma in suka canja zuciya a cikin ƙasar da suke zaman bauta, suka tuba suka roƙe ka a ƙasar zaman bautarsu suka kuma ce, ‘Mun yi zunubi, mu yi abin da ba daidai ba, mu kuwa yi mugunta’;
s'ils reviennent à la raison dans le pays où ils ont été emmenés captifs, s'ils reviennent à eux et s'ils t'adressent des supplications dans le pays de leur captivité, en disant: « Nous avons péché, nous avons agi avec perversité et nous avons fait le mal;
38 in kuma sun juye gare ka da dukan zuciyarsu da ransu a ƙasar zaman bautarsu inda aka kai su, suka kuma dubi wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, wajen birnin da ka zaɓa da kuma wajen haikalin da na gina domin Sunanka;
s'ils reviennent à toi de tout leur cœur et de toute leur âme dans le pays de captivité où ils ont été emmenés, et s'ils prient pour le pays que tu as donné à leurs pères, pour la ville que tu as choisie et pour la maison que j'ai bâtie à ton nom,
39 to, daga sama, mazauninka, sai ka ji addu’arsu da kuma roƙe-roƙensu, ka kuwa biya musu bukatunsu. Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi.
alors écoute du ciel, de ta demeure, leur prière et leurs supplications, fais droit à leur cause et pardonne à ton peuple qui a péché contre toi.
40 “Yanzu, Allahna, bari idanunka su buɗu kunnuwanka kuma su saurara ga addu’o’in da ake miƙa a wannan wuri.
« Maintenant, mon Dieu, que tes yeux soient ouverts et que tes oreilles soient attentives à la prière qui est faite en ce lieu.
41 “Yanzu ka tashi, ya Ubangiji Allah, ka zo wurin hutunka,
« Maintenant, lève-toi, Yahvé Dieu, dans ton lieu de repos, toi et l'arche de ta force. Que tes prêtres, Yahvé Dieu, soient revêtus du salut, et que tes saints se réjouissent de la bonté.
42 Ya Ubangiji Allah, kada ka ƙyale shafaffenka.
« Yahvé Dieu, ne détourne pas le visage de ton oint. Souviens-toi de tes bontés envers David, ton serviteur. »