< 2 Tarihi 6 >

1 Sa’an nan Solomon ya ce, “Ubangiji ya faɗa cewa zai zauna cikin duhun girgije;
Da sagde Salomo: Herren har sagt, at han vilde bo i Mørket.
2 na gina ƙasaitaccen haikali dominka, wuri domin ka zauna har abada.”
Og jeg har bygget dig en Boligs Hus, ja en fast Bolig, at du skal bo der evindelig.
3 Yayinda dukan taron Isra’ila suke tsaye a can, sai sarki ya juya ya albarkace su.
Og Kongen vendte sig om og velsignede al Israels Menighed; thi al Israels Menighed stod.
4 Sa’an nan ya ce, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda da hannuwansa ya cika abin da ya yi alkawari da bakinsa ga mahaifina Dawuda. Gama ya ce,
Og han sagde: Lovet være Herren, Israels Gud! som talte med sin Mund til David, min Fader, og opfyldte det med sine Hænder og sagde:
5 ‘Tun ranar na da fitar da mutanena daga Masar, ban zaɓi wani birni a wata kabilar Isra’ila don a gina haikali domin Sunana ya kasance a can ba, ba kuwa zaɓi wani yă zama shugaba a bisa jama’ata Isra’ila ba.
Fra den Dag da jeg udførte mit Folk af Ægyptens Land, har jeg ikke udvalgt nogen Stad af alle Israels Stammer, til at man skulde bygge et Hus, at mit Navn skulde være der; ikke heller har jeg udvalgt nogen Mand til at være en Fyrste over mit Folk Israel;
6 Amma yanzu na zaɓi Urushalima domin Sunana yă kasance a can, na kuma zaɓi Dawuda yă yi mulkin mutanena Isra’ila.’
men jeg udvalgte Jerusalem, at mit Navn skal være der, og jeg udvalgte David, at han skulde være over mit Folk Israel.
7 “Mahaifina Dawuda ya yi niyya a zuciyarsa yă gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Og det var i min Fader Davids Hjerte at bygge Herren Israels Guds Navn et Hus.
8 Amma Ubangiji ya ce wa mahaifina Dawuda, ‘Domin yana a zuciyarka ka gina haikali domin Sunana, ka yi daidai da ka kasance da wannan a zuciyarka.
Men Herren sagde til David, min Fader: Fordi det har været i dit Hjerte at bygge mit Navn et Hus, da gjorde du vel deri, at det var i dit Hjerte.
9 Duk da haka, ba kai ba ne za ka gina haikalin, amma ɗanka wanda yake namanka da jininka, shi ne wanda zai gina haikali domin Sunana.’
Dog skal du ikke bygge det Hus; men din Søn, som skal udgaa af dine Lænder, han skal bygge mit Navn et Hus.
10 “Ubangiji ya kiyaye alkawarin da ya yi. Na gāje Dawuda mahaifina yanzu kuwa na zauna a kan kujerar sarautar Isra’ila, kamar dai yadda Ubangiji ya alkawarta, na kuma gina haikali domin Sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Og Herren har stadfæstet sit Ord, som han talte; thi jeg er kommen op i Davids, min Faders, Sted og sidder paa Israels Trone, som Herren talte, og har bygget Herren Israels Guds Navn et Hus.
11 A can na ajiye akwatin alkawari, inda alkawarin Ubangiji da ya yi da mutanen Isra’ila yake.”
Og der har jeg sat Arken, hvori Herrens Pagt er, som han gjorde med Israels Børn.
12 Sa’an nan Solomon ya tsaya a gaban bagaden Ubangiji a gaban dukan taron Isra’ila ya ɗaga hannuwansa sama.
Og han stod foran Herrens Alter, for al Israels Forsamling, og udbredte sine Hænder.
13 Dā ma ya riga ya gina dakalin tagulla, mai tsawo kamu biyar, fāɗi kamu biyar da kuma tsayi kamu uku, ya kuma sa shi a tsakiyar filin waje. Ya tsaya a kan dakalin ya kuma durƙusa a gaban dukan taron Isra’ila ya buɗe hannuwansa sama.
Men Salomo havde gjort en Forhøjning af Kobber og sat den midt i Gaarden, fem Alen var dens Længde, og fem Alen var dens Bredde og tre Alen var dens Højde; og han stod paa den og knælede paa sine Knæ for al Israels Forsamling og udbredte sine Hænder imod Himmelen.
14 Ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, babu Allah kamar ka a sama da kuma ƙasa, kai da kake kiyaye alkawarinka na ƙauna tare da bayinka waɗanda suke cin gaba da zuciya ɗaya a hanyarka.
Og han sagde: Herre, Israels Gud! der er ingen Gud som du, i Himmelen eller paa Jorden, du, som holder Pagten og Miskundheden med dine Tjenere, som vandre for dit Ansigt af deres ganske Hjerte,
15 Ka kiyaye alkawarinka ga bawanka Dawuda mahaifina; da bakinka ka yi alkawari kuma da hannunka ka cika shi, yadda yake a yau.
du, som har holdt din Tjener David, min Fader, det, du talte til ham; thi du har talt med din Mund og fuldkommet med din Haand, som det ses paa denne Dag.
16 “Yanzu fa Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka kiyaye wa bawanka Dawuda mahaifina alkawuran da ka yi masa sa’ad da ka ce, ‘Ba za ka kāsa kasance da mutumin da zai zauna a gabana a kan kujerar sarautar Isra’ila ba, in kawai’ya’yanka maza za su kula cikin dukan abin da suke yi su yi tafiya a gabana bisa ga dokata, kamar yadda ka yi.’
Og nu, Herre, Israels Gud! hold din Tjener David, min Fader, det, som du har tilsagt ham, og sagt: Dig skal ikke fattes en Mand for mit Ansigt, som skal sidde paa Israels Trone, naar ikkun dine Børn bevare deres Vej, at vandre i min Lov, saaledes som du har vandret for mit Ansigt.
17 Yanzu kuwa, ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bari maganarka da ka yi alkawarta wa bawanka Dawuda yă cika.
Og nu, Herre, Israels Gud! lad dit Ord staa fast, som du talede til din Tjener, til David.
18 “Amma tabbatacce Allah zai zauna a duniya tare da mutane? Sammai, har ma da saman sammai, ba za su iya riƙe ka ba. Balle wannan haikalin da na gina!
Thi sandelig, monne Gud skulde bo hos Menneskene paa Jorden? se, Himlene og Himlenes Himle kunne ikke rumme dig, hvor langt mindre dette Hus, som jeg har bygget?
19 Duk da haka ka mai da hankali ga addu’ar bawanka da kuma roƙo don jinƙai, ya Ubangiji, Allahna. Ka ji kuka da addu’ar da bawanka yake yi a gabanka.
Men vend dit Ansigt til din Tjeners Bøn og til hans ydmyge Begæring, Herre, min Gud! at høre paa det Raab og paa den Bøn, som din Tjener beder for dit Ansigt:
20 Bari idanunka su buɗu ta wajen wannan haikali dare da rana, wannan wurin da ka ce za ka sa Sunanka a can. Bari ka ji addu’ar da bawanka ke yi ta wajen wannan wuri.
At dine Øjne maa være aabnede over dette Hus Dag og Nat, over det Sted, som du har sagt om, at du vilde sætte dit Navn der til at høre den Bøn, som din Tjener beder paa dette Sted;
21 Ka ji roƙe-roƙen bawanka da na mutanenka Isra’ila sa’ad da suka yi addu’a suna duban wajen wannan wuri. Ka ji daga sama, mazauninka; kuma sa’ad da ka ji, ka gafarta.
og at du vilde høre paa din Tjeners og dit Folk Israels ydmyge Begæringer, som de skulle bede paa dette Sted; og at du vilde høre det fra det Sted, hvor du bor i Himmelen, ja at du vilde høre og forlade.
22 “Sa’ad da mutum ya yi wa maƙwabcinsa laifi aka kuma bukaci ya yi rantsuwa, ya kuma zo ya rantse a gaban bagadenka a cikin wannan haikali,
Dersom nogen synder imod sin Næste, og man paalægger ham en Ed i at lade ham sværge, og den Ed kommer for dit Alter i dette Hus:
23 sai ka ji daga sama ka kuma yi wani abu. Ka shari’anta tsakanin bayinka, kana sāka wa mai laifi ta wurin kawo a kansa hakkin abin da ya yi. Ka nuna cewa marar laifi ba shi da laifi, ta haka a fiffita rashin laifinsa.
Da ville du høre fra Himmelen af og gøre derefter og dømme dine Tjenere, saa at du betaler den ugudelige og fører hans Vej over hans Hoved og retfærdiggør den retfærdige og giver ham efter hans Retfærdighed.
24 “Sa’ad da an ci mutanenka Isra’ila a yaƙi ta wurin abokin gāba domin sun yi maka zunubi kuma sa’ad da suka juya suka furta sunanka, suna addu’a suka kuma yin roƙe-roƙe a gabanka a wannan haikali,
Og dersom dit Folk Israel bliver slaget for Fjendens Ansigt, naar de have syndet imod dig, og de da omvende sig og bekende dit Navn og bede og bønfalde om Naade for dit Ansigt i dette Hus:
25 sai ka ji daga sama ka kuma gafarta zunubin mutanenka Isra’ila ka kuma dawo da su zuwa ƙasar da ka ba su da kuma kakanninsu.
Da Ville du høre fra Himmelen af og forlade dit Folks, Israels, Synd og føre dem tilbage til det Land, som du har givet dem og deres Fædre.
26 “Sa’ad da sammai suka rufu ba kuwa ruwan sama saboda mutanenka sun yi maka zunubi, sa’ad da kuwa suka yi addu’a suna duban waje wannan wuri suka kuma furta sunanka suka juye daga zunubinsu domin ka azabta su,
Naar Himmelen bliver tillukket, og der ikke vorder Regn, fordi de have syndet imod dig, og de da bede paa dette Sted og bekende dit Navn og omvende sig fra deres Synd, fordi du ydmyger dem:
27 sai ka ji daga sama ka kuma gafarta zunubin bayinka, mutanenka Isra’ila. Ka koya musu hanyar da ta dace da za su yi zama, ka kuma aika ruwan sama a ƙasar da ka ba mutanenka gādo.
Da ville du høre i Himmelen og forlade dine Tjeneres og dit Folks, Israels, Synd, fordi du viser dem den gode Vej, paa hvilken de skulle vandre; og du ville give Regn over dit Land, som du har givet dit Folk til Arv.
28 “Sa’ad da yunwa ko annoba ta fāɗo a ƙasar, ko wahala ko fumfuna, ko fāra ko fāra ɗango, ko sa’ad da abokan gāba sun yi musu ƙawanya a kowane daga biranensu, dukan wata masifa ko cutar da za tă zo,
Naar der vorder Hunger i Landet, naar der vorder Pest, naar der vorder Tørke og Brand i Korn, Græshopper og Kornorme, naar hans Fjender ængste ham i hans Stæders Land, naar der kommer alle Haande Plage og alle Haande Sygdom;
29 sa’ad da kuwa wani cikin mutanenka Isra’ila ya yi wata addu’a ko roƙo, kowa yana sane a azabarsa da kuma zafinsa, yana buɗe hannuwansa yana duban wajen wannan haikali,
al Bøn, al ydmyg Begæring, som sker af hvert Menneske eller af alt dit Folk Israel, som kender hver sin Plage og sin Smerte og udbreder sine Hænder til dette Hus:
30 sai ka ji daga sama, mazauninka. Ka gafarta, ka kuma yi da kowane mutum gwargwadon duk abin da yake yi, da yake ka san zuciyarsa (gama kai kaɗai ka san zukatan mutane),
Den ville du da høre fra Himmelen af, fra den faste Bolig, i hvilken du bor, og forlade og give enhver efter alle hans Veje, ligesom du kender hans Hjerte; thi du alene kender for dig Menneskens Børns Hjerter,
31 don su ji tsoronka su kuma yi tafiya a hanyoyinka a kowane lokacin da suke zama a ƙasar da ka ba wa kakanninsu.
paa det de skulle frygte dig og vandre i dine Veje alle de Dage, hvilke de leve i Landet, som du har givet vore Fædre.
32 “Game da baƙo wanda shi ba na mutanenka Isra’ila ba kuwa amma ya zo daga ƙasa mai nisa saboda sunanka mai girma da kuma hannunka mai iko da hannunka mai ƙarfi, sa’ad da ya zo ya yi addu’a yana duban wannan haikali,
Ja, ogsaa den fremmede, som ikke er af dit Folk Israel, men kommer fra et langt fraliggende Land for dit store Navns og for din stærke Haands og din udrakte Arms Skyld, og de komme og bede imod dette Hus:
33 sai ka ji daga sama, mazauninka, ka kuma yi duk abin da baƙon ya nemi ka yi, saboda dukan mutanen duniya su san sunanka su kuma ji tsoronka, kamar yadda mutanenka Isra’ila suke yi, su kuma san cewa wannan gidan da na gina na Sunanka ne.
Ham ville du da høre fra Himmelen af, fra den faste Bolig, i hvilken du bor, og gøre efter alt det, som den fremmede raaber til dig om; paa det at alle Folk paa Jorden maa kende dit Navn og frygte dig, ligesom dit Folk Israel, og at de maa vide, at dette Hus, som jeg har bygget, er kaldet efter dit Navn.
34 “Sa’ad da mutanenka suka je yaƙi da abokan gābansu, ko’ina ka kai su, kuma sa’ad da suka yi addu’a gare ka suna duban wannan birnin da ka zaɓa da haikalin nan da na gina domin Sunanka,
Naar dit Folk drager ud til Krigen imod sine Fjender, paa den Vej, hvor du sender dem hen, og de bede til dig, vendte imod Vejen til den Stad, som du udvalgte, og imod det Hus, som jeg har bygget til dit Navn:
35 sai ka ji addu’arsu da kuma roƙonsu daga sama, ka kuma biya musu bukatarsu.
Da ville du høre deres Bøn og deres ydmyge Begæring fra Himmelen af og skaffe dem Ret.
36 “Sa’ad da suka yi maka zunubi, gama babu wani wanda ba ya zunubi, ka kuwa yi fushi da su ka miƙa su ga abokin gāba, wanda ya kai su zaman bauta a ƙasa mai nisa ko kuwa kusa;
Naar de synde imod dig (thi der er intet Menneske, som jo synder), og du bliver vred paa dem og giver dem hen for deres Fjenders Ansigt, og de, som have fanget dem, føre dem fangne bort til et Land langt borte eller nær hos,
37 Kuma in suka canja zuciya a cikin ƙasar da suke zaman bauta, suka tuba suka roƙe ka a ƙasar zaman bautarsu suka kuma ce, ‘Mun yi zunubi, mu yi abin da ba daidai ba, mu kuwa yi mugunta’;
og de tage det igen til Hjerte udi Landet, hvori de ere fangne, og omvende sig og bede til dig om Naade i deres Fangenskabs Land, og de sige: Vi have syndet, handlet ilde og været ugudelige;
38 in kuma sun juye gare ka da dukan zuciyarsu da ransu a ƙasar zaman bautarsu inda aka kai su, suka kuma dubi wajen ƙasar da ka ba wa kakanninsu, wajen birnin da ka zaɓa da kuma wajen haikalin da na gina domin Sunanka;
og de omvende sig til dig af deres ganske Hjerte og af deres ganske Sjæl i deres Fangenskabs Land, hvor de holde dem fangne; og de bede, vendte imod Vejen til deres Land, som du har givet deres Fædre, og imod Staden, som du udvalgte, og imod Huset, som jeg har bygget for dit Navn:
39 to, daga sama, mazauninka, sai ka ji addu’arsu da kuma roƙe-roƙensu, ka kuwa biya musu bukatunsu. Ka gafarta wa mutanenka, waɗanda suka yi maka zunubi.
Da ville du høre fra Himmelen af, fra den faste Bolig, som du bor udi, deres Bøn og deres ydmyge Begæringer og skaffe dem Ret og forlade dit Folk det, som de have syndet imod dig.
40 “Yanzu, Allahna, bari idanunka su buɗu kunnuwanka kuma su saurara ga addu’o’in da ake miƙa a wannan wuri.
Nu, min Gud! kære, lad dine Øjne være aabnede, og lad dine Øren give Agt paa den Bøn, som sker paa dette Sted.
41 “Yanzu ka tashi, ya Ubangiji Allah, ka zo wurin hutunka,
Saa staa nu op, Herre, Gud! til din Hvile, du og din Magts Ark: Herre, Gud! lad dine Præster iføres Frelse, og lad dine hellige glæde sig i det gode!
42 Ya Ubangiji Allah, kada ka ƙyale shafaffenka.
Herre, Gud! forskyd ikke din Salvedes Ansigt; kom den Naade, du viste imod din Tjener David, i Hu!

< 2 Tarihi 6 >