< 2 Tarihi 36 >

1 Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a Urushalima yă gāji mahaifinsa.
Le peuple du pays prit donc Joachaz, fils de Josias, et l’établit roi en la place de son père à Jérusalem.
2 Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku.
Joachaz avait vingt-trois ans lorsqu’il commença à régner, et il régna trois mois à Jérusalem.
3 Sarkin Masar ya tumɓuke shi a Urushalima, ya tilasta Yahuda su biya haraji talenti ɗari na azurfa da kuma talentin zinariya.
Mais le roi d’Égypte, étant venu à Jérusalem, le déposa, et condamna le pays à cent talents d’argent et à un talent d’or.
4 Sarkin Masar ya naɗa Eliyakim, ɗan’uwan Yehoyahaz, sarki a bisa Yahuda da kuma Urushalima, ya kuma canja sunan Eliyakim zuwa Yehohiyakim. Amma Neko ya ɗauki Yehoyahaz ɗan’uwan Eliyakim ya kai Masar.
Et il établit Eliakim, son frère, roi en sa place sur Juda et sur Jérusalem, et il changea son nom en Joakim; mais Joachaz lui-même, il le prit avec lui et l’emmena en Égypte.
5 Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa.
Joakim avait vingt-cinq ans lorsqu’il commença à régner, et il régna onze ans à Jérusalem; mais il fit le mal devant le Seigneur son Dieu.
6 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya hauro ya kara da shi. Ya kama shi, ya daure da sarƙoƙin tagulla, ya kuma kai shi Babilon.
Contre lui monta Nabuchodonosor, roi des Chaldéens, et il l’emmena enchaîné à Babylone,
7 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kuma kwaso kayayyaki daga haikalin Ubangiji ya sa su a haikalinsa a can.
Dans laquelle il transporta aussi les vases du Seigneur, et il les mit dans son temple.
8 Sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim, ayyukan banƙyamar da ya aikata da dukan abubuwan da aka same shi da su, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda. Sai Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Mais le reste des actions de Joakim, et de ses abominations qu’il fit, et ce qui fut découvert en lui, est contenu dans le Livre des rois de Juda et d’Israël. Joachin son fils régna en sa place.
9 Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku da kwana goma. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji.
Joachin avait huit ans lorsqu’il commença à régner, et il régna trois mois et dix jours à Jérusalem, et il fit le mal en la présence du Seigneur.
10 Da bazara, Sarki Nebukadnezzar ya aika a kawo Yehohiyacin, aka kuma kawo shi Babilon, tare da kayayyaki masu daraja daga haikalin Ubangiji, sai Sarki Nebukadnezzar ya naɗa kawunsa Zedekiya, sarki a bisa Yahuda da Urushalima.
Et lorsque le cours de l’année fut révolu, le roi Nabuchodonosor envoya des troupes qui l’emmenèrent à Babylone, emportant en même temps les vases les plus précieux de la maison du Seigneur. Or il établit Sédécias, son oncle, roi sur Juda et sur Jérusalem.
11 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya.
Sédécias avait vingt et un ans lorsqu’il commença à régner, et il régna onze ans à Jérusalem.
12 Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa kuma bai ƙasƙantar da kansa a gaban Irmiya annabi, wanda ya yi magana kalmar Ubangiji ba.
Et il fit le mal en la présence du Seigneur son Dieu, et il ne rougit point en face de Jérémie, le prophète, qui lui parlait par l’ordre du Seigneur.
13 Ya tayar wa Sarki Nebukadnezzar, wanda ya sa ya yi rantsuwa da sunan Allah. Ya zama mai kunnen ƙashi da kuma taurin zuciya, bai kuwa juye ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ba.
Il se détacha même du roi Nabuchodonosor, qui l’avait adjuré par Dieu; il endurcit sa tête et son cœur pour ne point retourner au Seigneur Dieu d’Israël.
14 Bugu da ƙari, dukan shugabannin firistoci da mutane suka ƙara zama marasa aminci, suna bin dukan abubuwan banƙyama na al’ummai, suka ƙazantar da haikalin Ubangiji, wanda ya tsarkake a Urushalima.
Et même tous les princes des prêtres, et le peuple, prévariquèrent iniquement suivant toutes les abominations des nations, et profanèrent la maison du Seigneur, qu’il avait sanctifiée pour lui à Jérusalem.
15 Sai Ubangiji Allah na kakanninsu, ya yi ta aika da magana gare su ta wurin’yan saƙonsa sau da sau, domin ya ji tausayi mutanensa da mazauninsa.
Or le Seigneur Dieu de leurs pères s’adressait à eux par l’entremise de ses envoyés, se levant durant la nuit, et les avertissant chaque jour, parce qu’il ménageait son peuple et sa demeure.
16 Amma suka yi wa’yan saƙon Allah ba’a, suka rena maganarsa, suka yi wa annabawansa dariyar reni, har sai da fushin Ubangiji ya tasar a kan mutanensa babu makawa.
Mais eux se moquaient des envoyés de Dieu, faisaient peu de cas de ses paroles, et raillaient les prophètes, jusqu’à ce que la fureur du Seigneur montât contre son peuple, et qu’il n’y eût aucun remède.
17 Ya bashe su ga sarkin Babiloniyawa wanda ya karkashe samarinsu da takobi a wuri mai tsarki, bai yi juyayin saurayi, ko budurwa, ko tsoho, ko gajiyayye ba. Allah ya bashe su duka ga Nebukadnezzar.
Car il amena contre eux le roi des Chaldéens, qui tua leurs jeunes hommes par le glaive dans la maison de son sanctuaire; et il n’eut pitié ni de l’adolescent, ni de la vierge, ni du vieillard, ni même de l’homme décrépit: mais il les livra tous entre ses mains,
18 Nebukadnezzar ya kwashe dukan kayayyaki daga haikalin Allah, babba da ƙarami, da ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin sarki da na fadawansa zuwa Babilon.
Et quant à tous les vases de la maison du Seigneur, tant les grands que les petits, et les trésors du temple, du roi et des princes, il les transporta à Babylone.
19 Suka cinna wa haikalin Allah wuta, suka rurrushe katangar Urushalima; suka ƙone dukan fada, suka kuma lalace kome mai amfani da yake can.
Les ennemis incendièrent la maison de Dieu, détruisirent le mur de Jérusalem; brûlèrent toutes les tours; et tout ce qu’il y avait de précieux, ils le détruisirent.
20 Waɗanda ba a kashe ba kuwa Nebukadnezzar ya kwashe su, ya kai Babilon, suka zama bayinsa da na’ya’yansa maza har zuwa kahuwar mulkin Farisa.
Si quelqu’un avait échappé au glaive, conduit à Babylone, il était esclave du roi et de ses enfants, jusqu’à ce que régnât le roi de Perse,
21 Ƙasar ta more hutun Asabbacinta; a dukan lokacin zamanta kango ta huta, har sai da shekaru saba’in nan suka cika bisa ga maganar Ubangiji da Irmiya ya faɗi.
Et que fût accomplie la parole du Seigneur annoncée par la bouche de Jérémie, et que la terre célébrât ses sabbats; car pendant tous les jours de la désolation, elle fit le sabbat, jusqu’à ce que fussent accomplis les soixante-dix ans.
22 Don a cika maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya, a shekara farko ta Sairus sarkin Farisa, sai Ubangiji ya motsa zuciyar Sairus na Farisa don yă yi shela a dukan masarautarsa, ya kuma sa shi a rubuce cewa,
Mais en la première année de Cyrus, roi des Perses, pour accomplir la parole du Seigneur qu’il avait dite par la bouche de Jérémie, le Seigneur suscita l’esprit de Cyrus, roi des Perses, qui commanda de publier dans tout son royaume un édit, même par écrit, disant:
23 “Ga abin da Sairus sarkin Farisa ya ce, “‘Ubangiji Allah na sama, ya ba ni dukan mulkokin duniya, ya kuma naɗa ni in gina masa haikali a Urushalima a Yahuda. Duk wani na mutanensa a cikinku, bari yă haura yă tafi, bari kuma Ubangiji Allahnsa yă kasance tare da shi.’”
Voici ce que dit Cyrus, roi des Perses: Le Seigneur Dieu du ciel m’a donné tous les royaumes de la terre, et lui-même m’a ordonné de lui bâtir une maison dans Jérusalem, qui est dans la Judée. Qui d’entre vous est de tout son peuple? Que le Seigneur son Dieu soit avec lui, et qu’il monte.

< 2 Tarihi 36 >