< 2 Tarihi 36 >
1 Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a Urushalima yă gāji mahaifinsa.
Le peuple prit Joachaz, fils de Josias, et il le sacra, et il le fit roi de Jérusalem, à la place de son père.
2 Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku.
Joachaz avait vingt-trois ans quand il monta sur le trône, et il régna trois mois à Jérusalem; Sa mère se nommait Amital, fille de Jérémie de Lobna, Et il fit le mal devant le Seigneur; il suivit tous les mauvais exemples de ses pères; Et le Pharaon Néchao le chargea de chaînes à Déblatha, en la terre d'Emath, pour qu'il ne régnât pas à Jérusalem.
3 Sarkin Masar ya tumɓuke shi a Urushalima, ya tilasta Yahuda su biya haraji talenti ɗari na azurfa da kuma talentin zinariya.
Il l'emmena en Égypte, et il frappa la terre d'une contribution de cent talents d'argent et d'un talent d'or.
4 Sarkin Masar ya naɗa Eliyakim, ɗan’uwan Yehoyahaz, sarki a bisa Yahuda da kuma Urushalima, ya kuma canja sunan Eliyakim zuwa Yehohiyakim. Amma Neko ya ɗauki Yehoyahaz ɗan’uwan Eliyakim ya kai Masar.
Et le Pharaon Néchao fit roi de Juda, à la place de Josias son père, Éliacim, fils de Josias, et il changea son nom en celui de Joacim, et il prit son frère Joachaz, et il l'emmena en Égypte, où il mourut. Mais il avait donné l'argent et l'or au Pharaon; en ce temps-là, on commença sur la terre à lever une taxe réglée par le Pharaon; chacun, autant qu'il le put, emprunta l'argent et l'or du peuplade la terre, pour le donner au Pharaon Néchao.
5 Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa.
Joacim avait vingt-cinq ans lorsqu'il monta sur le trône, et il régna onze ans à Jérusalem;
6 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya hauro ya kara da shi. Ya kama shi, ya daure da sarƙoƙin tagulla, ya kuma kai shi Babilon.
Nabuchodonosor marcha donc contre Joacim, le chargea de chaînes d'airain, et l'emmena à Babylone.
7 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kuma kwaso kayayyaki daga haikalin Ubangiji ya sa su a haikalinsa a can.
Alors, il emporta une part des vaisseaux du temple du Seigneur, et il les mit dans le temple de Babylone.
8 Sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim, ayyukan banƙyamar da ya aikata da dukan abubuwan da aka same shi da su, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda. Sai Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Quant au reste des faits et gestes de Joacim, n'est-il pas écrit au livre des Récits des rois de Juda? Et Joacim s'endormit avec ses pères, et on l'ensevelit à Gonaza avec ses pères, et Jéchonias, son fils, fut proclamé roi à sa place.
9 Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku da kwana goma. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji.
Jéchonias avait huit ans lorsqu'il monta sur le trône, et il régna trois mois et dix jours à Jérusalem, et il fit le mal devant le Seigneur.
10 Da bazara, Sarki Nebukadnezzar ya aika a kawo Yehohiyacin, aka kuma kawo shi Babilon, tare da kayayyaki masu daraja daga haikalin Ubangiji, sai Sarki Nebukadnezzar ya naɗa kawunsa Zedekiya, sarki a bisa Yahuda da Urushalima.
Et pendant le cours de l'année, le roi Nabuchodonosor envoya des troupes, et on l'emmena à Babylone avec tous les vases précieux du temple du Seigneur, et l'on proclama roi de Juda et de Jérusalem, Sédécias, frère de son père.
11 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya.
Sédécias avait vingt et un ans lorsqu'il monta sur le trône, et il régna onze ans à Jérusalem.
12 Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa kuma bai ƙasƙantar da kansa a gaban Irmiya annabi, wanda ya yi magana kalmar Ubangiji ba.
Et il fit le mal devant le Seigneur, et il ne rentra en lui-même, ni devant le prophète Jérémie, ni à la parole du Seigneur.
13 Ya tayar wa Sarki Nebukadnezzar, wanda ya sa ya yi rantsuwa da sunan Allah. Ya zama mai kunnen ƙashi da kuma taurin zuciya, bai kuwa juye ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ba.
Il se révolta contre le roi Nabuchodonosor, après qu'au nom du Seigneur, le prophète l'eût adjuré de n'en rien faire; il endurcit son cœur et il se roidit le cou, de sorte qu'il ne retourna pas au Seigneur Dieu d'Israël.
14 Bugu da ƙari, dukan shugabannin firistoci da mutane suka ƙara zama marasa aminci, suna bin dukan abubuwan banƙyama na al’ummai, suka ƙazantar da haikalin Ubangiji, wanda ya tsarkake a Urushalima.
Et les premiers de Juda, et les prêtres et le peuple de la contrée, multiplièrent les offenses en commettant les abominations des peuples étrangers, et ils souillèrent le temple du Seigneur à Jérusalem.
15 Sai Ubangiji Allah na kakanninsu, ya yi ta aika da magana gare su ta wurin’yan saƙonsa sau da sau, domin ya ji tausayi mutanensa da mazauninsa.
Et le Seigneur Dieu de leurs pères les avertit en leur envoyant ses prophètes, eu leur envoyant à chaque aurore des messagers, pour épargner son peuple et le lieu saint.
16 Amma suka yi wa’yan saƙon Allah ba’a, suka rena maganarsa, suka yi wa annabawansa dariyar reni, har sai da fushin Ubangiji ya tasar a kan mutanensa babu makawa.
Mais ils raillaient ses envoyés, ils méprisaient ses discours, ils se moquaient de ses prophètes, jusqu'à ce qu'enfin la colère du Seigneur s'enflammât contre le peuple et fût implacable.
17 Ya bashe su ga sarkin Babiloniyawa wanda ya karkashe samarinsu da takobi a wuri mai tsarki, bai yi juyayin saurayi, ko budurwa, ko tsoho, ko gajiyayye ba. Allah ya bashe su duka ga Nebukadnezzar.
Alors, le Seigneur amena contre eux le roi des Chaldéens, qui tua leurs jeunes fils par le glaive dans le temple et le sanctuaire; il n'épargna pas Sédécias, et n'eut point pitié des vierges de Jérusalem; les vainqueurs enlevèrent les anciens; le Seigneur leur avait livré toutes choses.
18 Nebukadnezzar ya kwashe dukan kayayyaki daga haikalin Allah, babba da ƙarami, da ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin sarki da na fadawansa zuwa Babilon.
Et tous les vaisseaux du temple de Dieu, grands et petits, et tous les trésors, tant du temple que du palais et des maisons des grands, furent transportés à Babylone.
19 Suka cinna wa haikalin Allah wuta, suka rurrushe katangar Urushalima; suka ƙone dukan fada, suka kuma lalace kome mai amfani da yake can.
Et Nabuchodonosor brûla le temple du Seigneur; puis, il démolit les remparts de Jérusalem; il livra aux flammes tous ses palais, il détruisit tous les vases précieux.
20 Waɗanda ba a kashe ba kuwa Nebukadnezzar ya kwashe su, ya kai Babilon, suka zama bayinsa da na’ya’yansa maza har zuwa kahuwar mulkin Farisa.
Et il transporta le reste des habitants à Babylone, où ils furent esclaves du roi ou de ses fils, jusqu'à l'établissement de l'empire des Mèdes;
21 Ƙasar ta more hutun Asabbacinta; a dukan lokacin zamanta kango ta huta, har sai da shekaru saba’in nan suka cika bisa ga maganar Ubangiji da Irmiya ya faɗi.
Afin que la parole du Seigneur qu'avait fait connaître la bouche de Jérémie, le prophète, fût accomplie, et que la terre jouît de ses sabbats, et observât le sabbat tous les jours de sa désolation, jusqu'à l'achèvement des soixante-dix années.
22 Don a cika maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya, a shekara farko ta Sairus sarkin Farisa, sai Ubangiji ya motsa zuciyar Sairus na Farisa don yă yi shela a dukan masarautarsa, ya kuma sa shi a rubuce cewa,
La première année de la domination de Cyrus, roi des Perses, après l'accomplissement de la parole du Seigneur, qu'avait dite la bouche de Jérémie, le Seigneur excita l'esprit de Cyrus, roi des Perses, et il envoya dans tout le royaume une proclamation par écrit, disant:
23 “Ga abin da Sairus sarkin Farisa ya ce, “‘Ubangiji Allah na sama, ya ba ni dukan mulkokin duniya, ya kuma naɗa ni in gina masa haikali a Urushalima a Yahuda. Duk wani na mutanensa a cikinku, bari yă haura yă tafi, bari kuma Ubangiji Allahnsa yă kasance tare da shi.’”
Voici ce que dit, à tous les royaumes de la terre, Cyrus, roi des Perses: Le Seigneur Dieu du ciel m'a donné le pouvoir, et il m'a prescrit de rebâtir son temple à Jérusalem, en Juda. Qui, parmi vous tous, est de son peuple? Qu'il parte; son Dieu sera avec lui.