< 2 Tarihi 36 >

1 Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a Urushalima yă gāji mahaifinsa.
And they took [the] people of the land Jehoahaz [the] son of Josiah and they made king him in place of father his in Jerusalem.
2 Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku.
[was] a son of Three and twenty year[s] Jehoahaz when became king he and three months he reigned in Jerusalem.
3 Sarkin Masar ya tumɓuke shi a Urushalima, ya tilasta Yahuda su biya haraji talenti ɗari na azurfa da kuma talentin zinariya.
And he removed him [the] king of Egypt in Jerusalem and he imposed a fine on the land one hundred talent[s] of silver and a talent of gold.
4 Sarkin Masar ya naɗa Eliyakim, ɗan’uwan Yehoyahaz, sarki a bisa Yahuda da kuma Urushalima, ya kuma canja sunan Eliyakim zuwa Yehohiyakim. Amma Neko ya ɗauki Yehoyahaz ɗan’uwan Eliyakim ya kai Masar.
And he made king [the] king of Egypt Eliakim brother his over Judah and Jerusalem and he changed name his Jehoiakim and Jehoahaz brother his he took Necho and he brought him Egypt towards.
5 Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa.
[was] a son of Twenty and five year[s] Jehoiakim when became king he and one [plus] ten year[s] he reigned in Jerusalem and he did the evil in [the] eyes of Yahweh God his.
6 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya hauro ya kara da shi. Ya kama shi, ya daure da sarƙoƙin tagulla, ya kuma kai shi Babilon.
On him he came up Nebuchadnezzar [the] king of Babylon and he bound him with bronze fetters to take him Babylon towards.
7 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kuma kwaso kayayyaki daga haikalin Ubangiji ya sa su a haikalinsa a can.
And some of [the] articles of [the] house of Yahweh he brought Nebuchadnezzar to Babylon and he put them in palace his in Babylon.
8 Sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim, ayyukan banƙyamar da ya aikata da dukan abubuwan da aka same shi da su, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda. Sai Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
And [the] rest of [the] matters of Jehoiakim and abominations his which he did and [what] was found on him there they [are] written on [the] scroll of [the] kings of Israel and Judah and he became king Jehoiachin son his in place of him.
9 Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku da kwana goma. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji.
[was] a son of Eight years Jehoiachin when became king he and three months and ten days he reigned in Jerusalem and he did the evil in [the] eyes of Yahweh.
10 Da bazara, Sarki Nebukadnezzar ya aika a kawo Yehohiyacin, aka kuma kawo shi Babilon, tare da kayayyaki masu daraja daga haikalin Ubangiji, sai Sarki Nebukadnezzar ya naɗa kawunsa Zedekiya, sarki a bisa Yahuda da Urushalima.
And to [the] return of the year he sent the king Nebuchadnezzar and he brought him Babylon towards with [the] articles of preciousness of [the] house of Yahweh and he made king Zedekiah relative his over Judah and Jerusalem.
11 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya.
[was] a son of Twenty and one year[s] Zedekiah when became king he and one [plus] ten year[s] he reigned in Jerusalem.
12 Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa kuma bai ƙasƙantar da kansa a gaban Irmiya annabi, wanda ya yi magana kalmar Ubangiji ba.
And he did the evil in [the] eyes of Yahweh God his not he humbled himself from to before Jeremiah the prophet from [the] mouth of Yahweh.
13 Ya tayar wa Sarki Nebukadnezzar, wanda ya sa ya yi rantsuwa da sunan Allah. Ya zama mai kunnen ƙashi da kuma taurin zuciya, bai kuwa juye ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ba.
And also against the king Nebuchadnezzar he rebelled who he had made swear an oath him by God and he made stiff neck his and he made hard heart his from turning back to Yahweh [the] God of Israel.
14 Bugu da ƙari, dukan shugabannin firistoci da mutane suka ƙara zama marasa aminci, suna bin dukan abubuwan banƙyama na al’ummai, suka ƙazantar da haikalin Ubangiji, wanda ya tsarkake a Urushalima.
Also all [the] leaders of the priests and the people they increased (to act unfaithfully *Q(K)*) unfaithfulness according to all [the] abominations of the nations and they made unclean [the] house of Yahweh which he had consecrated in Jerusalem.
15 Sai Ubangiji Allah na kakanninsu, ya yi ta aika da magana gare su ta wurin’yan saƙonsa sau da sau, domin ya ji tausayi mutanensa da mazauninsa.
And he sent Yahweh [the] God of ancestors their to them by [the] hand of messengers his rising early and sending for he had compassion on people his and on dwelling place his.
16 Amma suka yi wa’yan saƙon Allah ba’a, suka rena maganarsa, suka yi wa annabawansa dariyar reni, har sai da fushin Ubangiji ya tasar a kan mutanensa babu makawa.
And they were deriding [the] messengers of God and despising words his and mocking at prophets his until came up [the] anger of Yahweh on people his until there not [was] healing.
17 Ya bashe su ga sarkin Babiloniyawa wanda ya karkashe samarinsu da takobi a wuri mai tsarki, bai yi juyayin saurayi, ko budurwa, ko tsoho, ko gajiyayye ba. Allah ya bashe su duka ga Nebukadnezzar.
And he brought up on them [the] king of ([the] Chaldeans *Q(k)*) and he killed young men their with the sword in [the] house of sanctuary their and not he had compassion on young man and young woman [the] old and [the] decrepit everyone he gave in hand his.
18 Nebukadnezzar ya kwashe dukan kayayyaki daga haikalin Allah, babba da ƙarami, da ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin sarki da na fadawansa zuwa Babilon.
And all [the] articles of [the] house of God great and small and [the] treasures of [the] house of Yahweh and [the] treasures of the king and officials his everything he brought Babylon.
19 Suka cinna wa haikalin Allah wuta, suka rurrushe katangar Urushalima; suka ƙone dukan fada, suka kuma lalace kome mai amfani da yake can.
And they burned [the] house of God and they pulled down [the] wall of Jerusalem and all palaces its they burned with fire and all [the] articles of preciousness its to destroy.
20 Waɗanda ba a kashe ba kuwa Nebukadnezzar ya kwashe su, ya kai Babilon, suka zama bayinsa da na’ya’yansa maza har zuwa kahuwar mulkin Farisa.
And he took into exile the remainder from the sword to Babylon and they became for him and for sons his slaves until reigned [the] kingdom of Persia.
21 Ƙasar ta more hutun Asabbacinta; a dukan lokacin zamanta kango ta huta, har sai da shekaru saba’in nan suka cika bisa ga maganar Ubangiji da Irmiya ya faɗi.
To fulfill [the] word of Yahweh by [the] mouth of Jeremiah until it has accepted the land sabbaths its all [the] days of the desolation of it it rested to complete seventy year[s].
22 Don a cika maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya, a shekara farko ta Sairus sarkin Farisa, sai Ubangiji ya motsa zuciyar Sairus na Farisa don yă yi shela a dukan masarautarsa, ya kuma sa shi a rubuce cewa,
And in year one of Cyrus [the] king of Persia to fulfill [the] word of Yahweh by [the] mouth of Jeremiah he stirred up Yahweh [the] spirit of Cyrus [the] king of Persia and he caused to pass a proclamation in all kingdom his and also in writing saying.
23 “Ga abin da Sairus sarkin Farisa ya ce, “‘Ubangiji Allah na sama, ya ba ni dukan mulkokin duniya, ya kuma naɗa ni in gina masa haikali a Urushalima a Yahuda. Duk wani na mutanensa a cikinku, bari yă haura yă tafi, bari kuma Ubangiji Allahnsa yă kasance tare da shi.’”
Thus he says Cyrus - [the] king of Persia all [the] kingdoms of the earth he has given to me Yahweh [the] God of the heavens and he he has appointed me to build for him a house in Jerusalem which [is] in Judah who? [is] among you from all people his Yahweh God his [be] with him and let him go up.

< 2 Tarihi 36 >