< 2 Tarihi 36 >

1 Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a Urushalima yă gāji mahaifinsa.
And the people of the land take Jehoahaz son of Josiah and cause him to reign instead of his father in Jerusalem.
2 Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku.
Jehoahaz [is] a son of twenty-three years in his reigning, and he has reigned three months in Jerusalem,
3 Sarkin Masar ya tumɓuke shi a Urushalima, ya tilasta Yahuda su biya haraji talenti ɗari na azurfa da kuma talentin zinariya.
and the king of Egypt turns him aside in Jerusalem, and fines the land one hundred talents of silver, and a talent of gold;
4 Sarkin Masar ya naɗa Eliyakim, ɗan’uwan Yehoyahaz, sarki a bisa Yahuda da kuma Urushalima, ya kuma canja sunan Eliyakim zuwa Yehohiyakim. Amma Neko ya ɗauki Yehoyahaz ɗan’uwan Eliyakim ya kai Masar.
and the king of Egypt causes his brother Eliakim to reign over Judah and Jerusalem, and turns his name to Jehoiakim; and Necho has taken his brother Jehoahaz and brings him to Egypt.
5 Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa.
Jehoiakim [is] a son of twenty-five years in his reigning, and he has reigned eleven years in Jerusalem, and he does evil in the eyes of his God YHWH;
6 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya hauro ya kara da shi. Ya kama shi, ya daure da sarƙoƙin tagulla, ya kuma kai shi Babilon.
Nebuchadnezzar king of Babylon has come up against him, and binds him in bronze chains to take him away to Babylon.
7 Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kuma kwaso kayayyaki daga haikalin Ubangiji ya sa su a haikalinsa a can.
And Nebuchadnezzar has brought from the vessels of the house of YHWH to Babylon, and puts them in his temple in Babylon.
8 Sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim, ayyukan banƙyamar da ya aikata da dukan abubuwan da aka same shi da su, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda. Sai Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
And the rest of the matters of Jehoiakim, and his abominations that he has done, and that which is found against him, behold, they are written on the scroll of the kings of Israel and Judah, and his son Jehoiachin reigns in his stead.
9 Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku da kwana goma. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji.
Jehoiachin [is] a son of eight years in his reigning, and he has reigned three months and ten days in Jerusalem, and he does evil in the eyes of YHWH;
10 Da bazara, Sarki Nebukadnezzar ya aika a kawo Yehohiyacin, aka kuma kawo shi Babilon, tare da kayayyaki masu daraja daga haikalin Ubangiji, sai Sarki Nebukadnezzar ya naɗa kawunsa Zedekiya, sarki a bisa Yahuda da Urushalima.
and at the turn of the year King Nebuchadnezzar has sent and brings him to Babylon with the desirable vessels of the house of YHWH, and causes his brother Zedekiah to reign over Judah and Jerusalem.
11 Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya.
Zedekiah [is] a son of twenty-one years in his reigning, and he has reigned eleven years in Jerusalem;
12 Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa kuma bai ƙasƙantar da kansa a gaban Irmiya annabi, wanda ya yi magana kalmar Ubangiji ba.
and he does evil in the eyes of his God YHWH, he has not been humbled before Jeremiah the prophet [speaking] from the mouth of YHWH;
13 Ya tayar wa Sarki Nebukadnezzar, wanda ya sa ya yi rantsuwa da sunan Allah. Ya zama mai kunnen ƙashi da kuma taurin zuciya, bai kuwa juye ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ba.
and he has also rebelled against King Nebuchadnezzar who had caused him to swear by God, and he hardens his neck and strengthens his heart against turning back to YHWH, God of Israel.
14 Bugu da ƙari, dukan shugabannin firistoci da mutane suka ƙara zama marasa aminci, suna bin dukan abubuwan banƙyama na al’ummai, suka ƙazantar da haikalin Ubangiji, wanda ya tsarkake a Urushalima.
Also, all the heads of the priests and the people have multiplied to commit a trespass according to all the abominations of the nations, and they defile the house of YHWH that He has sanctified in Jerusalem.
15 Sai Ubangiji Allah na kakanninsu, ya yi ta aika da magana gare su ta wurin’yan saƙonsa sau da sau, domin ya ji tausayi mutanensa da mazauninsa.
And YHWH, God of their fathers, sends to them by the hand of His messengers—rising early and sending—for He has had pity on His people and on His habitation,
16 Amma suka yi wa’yan saƙon Allah ba’a, suka rena maganarsa, suka yi wa annabawansa dariyar reni, har sai da fushin Ubangiji ya tasar a kan mutanensa babu makawa.
but they are mocking at the messengers of God, and despising His words, and acting deceitfully with His prophets, until the going up of the fury of YHWH against His people—until there is no healing.
17 Ya bashe su ga sarkin Babiloniyawa wanda ya karkashe samarinsu da takobi a wuri mai tsarki, bai yi juyayin saurayi, ko budurwa, ko tsoho, ko gajiyayye ba. Allah ya bashe su duka ga Nebukadnezzar.
And He causes the king of the Chaldeans to go up against them, and he slays their chosen ones by the sword in the house of their sanctuary, and has had no pity on young man and virgin, old man and very aged—He has given the whole into his hand.
18 Nebukadnezzar ya kwashe dukan kayayyaki daga haikalin Allah, babba da ƙarami, da ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin sarki da na fadawansa zuwa Babilon.
And all the vessels of the house of God, the great and the small, and the treasures of the house of YHWH, and the treasures of the king and of his princes—he has brought the whole to Babylon.
19 Suka cinna wa haikalin Allah wuta, suka rurrushe katangar Urushalima; suka ƙone dukan fada, suka kuma lalace kome mai amfani da yake can.
And they burn the house of God, and break down the wall of Jerusalem, and they have burned all its palaces with fire, and all its desirable vessels—to destruction.
20 Waɗanda ba a kashe ba kuwa Nebukadnezzar ya kwashe su, ya kai Babilon, suka zama bayinsa da na’ya’yansa maza har zuwa kahuwar mulkin Farisa.
And he removes those left of the sword to Babylon, and they are to him and to his sons for servants, until the reigning of the kingdom of Persia,
21 Ƙasar ta more hutun Asabbacinta; a dukan lokacin zamanta kango ta huta, har sai da shekaru saba’in nan suka cika bisa ga maganar Ubangiji da Irmiya ya faɗi.
to fulfill the word of YHWH in the mouth of Jeremiah, until the land has enjoyed its Sabbaths; all the days of the desolation it kept Sabbath—to the fullness of seventy years.
22 Don a cika maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya, a shekara farko ta Sairus sarkin Farisa, sai Ubangiji ya motsa zuciyar Sairus na Farisa don yă yi shela a dukan masarautarsa, ya kuma sa shi a rubuce cewa,
And in the first year of Cyrus king of Persia, at the completion of the word of YHWH in the mouth of Jeremiah, YHWH has awoken the spirit of Cyrus king of Persia, and he causes an intimation to pass over into all his kingdom, and also in writing, saying,
23 “Ga abin da Sairus sarkin Farisa ya ce, “‘Ubangiji Allah na sama, ya ba ni dukan mulkokin duniya, ya kuma naɗa ni in gina masa haikali a Urushalima a Yahuda. Duk wani na mutanensa a cikinku, bari yă haura yă tafi, bari kuma Ubangiji Allahnsa yă kasance tare da shi.’”
“Thus said Cyrus king of Persia: YHWH, God of the heavens, has given all kingdoms of the earth to me, and He has laid a charge on me to build a house for Him in Jerusalem which [is] in Judah; who is among you of all His people? His God YHWH [is] with him, and he goes up!”

< 2 Tarihi 36 >