< 2 Tarihi 35 >
1 Yosiya ya yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji a Urushalima, aka kuma yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a ranar goma sha huɗu ga wata na farko.
Y Josías celebró la Pascua al Señor en Jerusalén; el día catorce del primer mes mataron al cordero para la pascua.
2 Ya zaɓi firistoci su yi aikinsu, sai ya ƙarfafa su su yi aikin da kyau a hidimar haikalin Ubangiji.
Y les dio a los sacerdotes sus lugares, y los animó en el servicio del templo de Dios.
3 Ya ce wa Lawiyawa waɗanda suke koyar da dukan Isra’ila da kuma waɗanda aka tsarkake wa Ubangiji. “Ku sa akwatin alkawari mai tsarki a cikin haikalin da Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila ya gina. Ba za a riƙa ɗaukansa a kafaɗa ba. Yanzu ku bauta wa Ubangiji Allahnku da kuma mutanensa Isra’ila.
Y dijo a los levitas, maestros de todo Israel, que estaban consagrados para el Señor: Mira, el cofre del pacto está en la casa que hizo Salomón, el hijo de David, rey de Israel; ya no tendrá que ser transportado en sus espaldas, ahora sean siervos del Señor su Dios y de su pueblo Israel.
4 Ku shirya kanku iyali-iyali a sassanku, bisa ga umarnan da Dawuda sarkin Isra’ila da kuma ɗansa Solomon suka rubuta.
Y prepárense en sus divisiones, por sus familias, como está ordenado en los escritos de David, rey de Israel, y de su hijo Salomón;
5 “Ku tsaya a tsattsarkan wuri, bisa ga ƙungiyoyin gidajen kakannin’yan’uwanku, waɗanda su ba firistoci ba ne. Kowanne ya sami kashi daga cikin gidan Lawiyawa.
Y tomen sus posiciones en el santuario, un grupo de levitas, agrupados como representantes de los grupos de familias de tus hermanos, y por cada división que haya una parte de una familia de los levitas.
6 Ku yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, ku tsarkake kanku, ku kuma shirya raguna domin’yan’uwanku, kuna yin abin da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.”
Sacrifiquen el cordero de la Pascua, y purifíquense, y prepárense para que sus hermanos, hagan de acuerdo a las órdenes dadas por el Señor a través de Moisés.
7 Yosiya ya tanada wa dukan mutanen da ba firistoci ba ne waɗanda suke a wurin, tumaki da awaki dubu talatin don a yanka saboda hadayun Bikin Ƙetarewa, ya kuma ba su shanu dubu uku. Dukan dabbobin kuwa daga garken sarki ne.
Y Josías dio corderos y cabras del rebaño como ofrendas de la Pascua para todas las personas que estaban presentes, hasta treinta mil y tres mil bueyes; estos eran de la propiedad privada del rey.
8 Fadawansa su ma suka ba da taimako da yardar rai ga mutane da kuma firistoci da Lawiyawa. Hilkiya, Zakariya da Yehiyel masu aiki a haikalin Allah, suka ba firistoci hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyu da ɗari shida da kuma shanu ɗari uku.
Y sus capitanes ofrecieron gratuitamente una ofrenda al pueblo, a los sacerdotes y a los levitas. Hilcías, Zacarías y Jehiel, los gobernantes del templo de Dios, dieron a los sacerdotes para las ofrendas de la Pascua dos mil seiscientos bovinos pequeños y trescientos bueyes.
9 Haka kuma Konaniya tare da Shemahiya da Netanel, ɗan’uwansa, da Hashabiya, Yehiyel da Yozabad, shugabannin Lawiyawa, suka tanadar da hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyar da kuma bijimai ɗari biyar domin Lawiyawa.
Y Conanías y Semaías y Natanael, sus hermanos, Hasabaias, Jehiel y Josabad, los jefes de los levitas, dieron a los levitas para las ofrendas de la Pascua cinco mil ganados y quinientos bueyes.
10 Sa’ad da aka shirya kome don Bikin Ƙetarewar, sai Firistoci tare da Lawiyawa suka tsaya wurin tsayawarsu bisa ga umarnin sarki.
Así que todo estaba listo y los sacerdotes tomaron sus lugares con los levitas en sus divisiones, como había dicho el rey.
11 Aka yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, firistoci kuma suka yayyafa jinin da aka ba su, yayinda Lawiyawa suna fiɗan dabbobi.
Y mataron a los corderos de la Pascua, y los sacerdotes rociaban la sangre cuando les fue dada, y los levitas hicieron el desollado.
12 Suka keɓe hadayun ƙonawa don su ba da su ga ƙungiyoyin iyalan mutane don su miƙa ga Ubangiji, yadda yake a rubuce a Littafin Musa. Suka yi haka da shanun.
Y quitaron las ofrendas quemadas, para que pudieran darlas y ofrecerlas al Señor por las divisiones de las familias del pueblo, como está registrado en el libro de Moisés. E hicieron lo mismo con los bueyes.
13 Suka gasa dabbobin Bikin Ƙetarewa a bisa wuta yadda aka tsara, suka dafa hadayu masu tsarki a tukwane, da manyan tukwane, da kuma kwanoni, suka raba su nan da nan ga dukan mutane.
Y el cordero de la Pascua se aso sobre el fuego, como se dice en la ley; y las ofrendas sagradas fueron cocinadas en ollas, calderos y sartenes, y llevadas rápidamente a todas las personas.
14 Bayan wannan, suka shirya wa kansu da kuma wa firistoci, saboda firistoci, zuriyar Haruna, suna miƙa hadayun ƙonawa da sashen kitse daga safe har dare. Saboda haka Lawiyawa suka shirya wa kansu da kuma wa firistocin daga zuriyar Haruna.
Y después de eso, se prepararon para ellos y para los sacerdotes; porque los sacerdotes, los hijos de Aarón, ofrecían las ofrendas quemadas y la grasa hasta la noche; así los levitas prepararon lo que se necesitaba para ellos y para los sacerdotes, los hijos de Aarón.
15 Mawaƙa zuriyar Asaf, suna a wuraren da Dawuda, Asaf, Heman da Yedutun mai duba na sarki suka tsara. Bai zama lalle matsaran ƙofofi a kowace ƙofa su bar wuraren aikinsu ba, domin’yan’uwansu Lawiyawa sun yi shiri dominsu.
Y los hijos de Asaf, los cantores, estaban en sus lugares, como lo ordenaron David y Asaf, Heman y Jedutún, el vidente del rey; y los encargados de las puertas estaban estacionados en cada puerta: no había necesidad de que se fueran de sus lugares, porque sus hermanos, los levitas, los preparaban.
16 Ta haka fa aka yi dukan hidimar Ubangiji a wannan rana, domin su kiyaye Bikin Ƙetarewa, domin kuma su miƙa hadayu na ƙonawa a bisa bagaden Ubangiji, yadda sarki Yosiya ya umarta.
Así que todo lo necesario para la adoración del Señor se preparó ese mismo día, para la celebración de la Pascua y la ofrenda de las ofrendas quemadas en el altar del Señor, como el Rey Josías había dado órdenes.
17 Isra’ilawan da suka kasance a can suka yi Bikin Ƙetarewa a wannan rana, suka kuma kiyaye Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai.
Y todos los hijos de Israel que estaban presentes guardaron la Pascua y la fiesta del pan sin levadura en ese tiempo por siete días.
18 Ba a taɓa yin Bikin Ƙetarewa haka ba tun zamanin annabi Sama’ila; kuma babu sarkin Isra’ilan da ya taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa kamar yadda Yosiya ya yi, tare da firistoci, Lawiyawa da kuma dukan Yahuda da Isra’ila, waɗanda suke can tare da mutanen Urushalima.
No se celebró ninguna Pascua como esta en Israel desde los días de Samuel el profeta; y ninguno de los reyes de Israel había celebrado una Pascua como la que guardaban Josías, los sacerdotes, los levitas y todos los de Judá e Israel que estaban presentes, y el pueblo de Jerusalén.
19 An yi wannan Bikin Ƙetarewa a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya.
En el decimoctavo año del gobierno de Josías, esta Pascua se llevó a cabo.
20 Bayan wannan duka, sa’ad da Yosiya ya shirya haikali, Neko sarkin Masar ya haura don yă yi yaƙi a Karkemish a Yuferites, sai Yosiya ya fita don yă fafata da shi a yaƙi.
Después de todo esto, y después de que Josías ordenó la casa, Necao, rey de Egipto, subió para hacer la guerra en Carquemis, junto al río Eufrates; Y Josías salió contra él.
21 Amma Neko ya aiki’yan saƙo ga Yosiya, yana cewa, “Me ya gama ni da kai, ya Sarkin Yahuda? Ban zo in yi yaƙi da kai ba. Na zo ne in yi yaƙi da gidan da yake gāba da ni! Ka ƙyale ni! Allah ne ya riga ya faɗa mini in hanzarta. Kada ka yi gāba da Allah, wanda yake tare da ni, don kada yă hallaka ka.”
Pero él le envió representantes, diciendo: ¿Qué tengo que ver contigo, rey de Judá? No he venido contra ti este día, sino contra aquellos con quienes estoy en guerra; y Dios me ha dado órdenes de avanzar rápidamente: mantente fuera del camino de Dios, porque él está conmigo o te enviará la destrucción.
22 Yosiya fa, bai juya daga gare shi ba, amma ya ɓad da kama don yă yi yaƙin. Bai saurari abin da Neko ya faɗa bisa ga umarnin Allah ba, amma ya tafi ya yaƙe shi a filin Megiddo.
Sin embargo, Josías no retrocedió; pero manteniendo su propósito de luchar contra él, y sin prestar atención a las palabras de Necao, que vinieron de Dios, se dirigió a la lucha en el valle de Meguido.
23 Maharba suka harbi Yosiya, sai ya ce wa hafsoshinsa, “Ku ɗauke ni ku fita da ni daga nan; gama an yi mini mummunan rauni.”
Y los arqueros enviaron sus flechas al rey Josías, y el rey dijo a sus criados: Llévame, porque estoy gravemente herido.
24 Saboda haka suka ɗauke shi a keken yaƙin, suka fitar da shi, suka sa shi a wata keken yaƙin da yake da shi, suka kawo shi Urushalima, inda ya mutu. Aka binne shi a makabartar kakanninsa, sai dukan Yahuda da Urushalima suka yi makoki dominsa.
Entonces sus siervos lo sacaron de la línea de los carros de guerra, lo pusieron en su segundo carruaje y lo llevaron a Jerusalén, donde llegó a su fin, y pusieron su cuerpo en el lugar de descanso de De su padre. Y en todo Judá y Jerusalén hubo gran llanto para Josías.
25 Annabin Irmiya ya tsara waƙoƙin makoki domin Yosiya, wanda har wa yau mawaƙa maza da mata suke rera game da Yosiya. Suka sa waɗannan su zama al’ada a Isra’ila, suna kuma a rubuce cikin Littafin Makoki.
E hizo Jeremías una canción de dolor para Josías; y hasta el día de hoy, Josiah es nombrado por todos los creadores de melodías, hombres y mujeres, en sus canciones de dolor; lo hicieron una regla en Israel; y las canciones están grabadas entre las canciones de la pena.
26 Sauran ayyukan mulkin Yosiya da kuma kyawawan abubuwan da ya yi, bisa ga abin da aka rubuta a Dokar Ubangiji,
Los demás hechos de Josías, y el bien que hizo, de acuerdo con lo que está registrado en la ley del Señor,
27 dukan ayyukan, daga farko har zuwa ƙarshe, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda.
Y todos sus actos, desde el principio hasta el fin, están registrados en el libro de los reyes de Israel y Judá.