< 2 Tarihi 35 >

1 Yosiya ya yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji a Urushalima, aka kuma yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a ranar goma sha huɗu ga wata na farko.
Josias fit ensuite à Jérusalem la Pâque du Seigneur, laquelle fut immolée le quatorzième jour du premier mois;
2 Ya zaɓi firistoci su yi aikinsu, sai ya ƙarfafa su su yi aikin da kyau a hidimar haikalin Ubangiji.
Et il établit les prêtres en leurs fonctions, et les exhorta à servir dans la maison du Seigneur.
3 Ya ce wa Lawiyawa waɗanda suke koyar da dukan Isra’ila da kuma waɗanda aka tsarkake wa Ubangiji. “Ku sa akwatin alkawari mai tsarki a cikin haikalin da Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila ya gina. Ba za a riƙa ɗaukansa a kafaɗa ba. Yanzu ku bauta wa Ubangiji Allahnku da kuma mutanensa Isra’ila.
Aux Lévites aussi, par l’enseignement desquels tout Israël était sanctifié au Seigneur, il dit: Mettez l’arche dans le sanctuaire du temple qu’a bâti Salomon, fils de David, roi d’Israël, car vous ne la porterez plus du tout; mais maintenant, servez le Seigneur votre Dieu et son peuple Israël.
4 Ku shirya kanku iyali-iyali a sassanku, bisa ga umarnan da Dawuda sarkin Isra’ila da kuma ɗansa Solomon suka rubuta.
Préparez-vous donc dans vos maisons et vos familles, selon la distribution de chacun de vous, ainsi que l’a ordonné David, roi d’Israël, et que l’a écrit Salomon, son fils.
5 “Ku tsaya a tsattsarkan wuri, bisa ga ƙungiyoyin gidajen kakannin’yan’uwanku, waɗanda su ba firistoci ba ne. Kowanne ya sami kashi daga cikin gidan Lawiyawa.
Et servez dans le sanctuaire, selon les familles et les classes lévitiques;
6 Ku yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, ku tsarkake kanku, ku kuma shirya raguna domin’yan’uwanku, kuna yin abin da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.”
Et, sanctifiés, immolez la Pâque; et préparez vos frères aussi, afin qu’ils puissent faire selon les paroles qu’a dites le Seigneur par l’entremise de Moïse.
7 Yosiya ya tanada wa dukan mutanen da ba firistoci ba ne waɗanda suke a wurin, tumaki da awaki dubu talatin don a yanka saboda hadayun Bikin Ƙetarewa, ya kuma ba su shanu dubu uku. Dukan dabbobin kuwa daga garken sarki ne.
Outre cela Josias donna à tout le peuple qui s’était trouvé là à la solennité de la Pâque, des agneaux et des chevreaux de ses troupeaux, trente mille têtes du reste de son bétail, et trois mille bœufs: c’était du bien entièrement du roi.
8 Fadawansa su ma suka ba da taimako da yardar rai ga mutane da kuma firistoci da Lawiyawa. Hilkiya, Zakariya da Yehiyel masu aiki a haikalin Allah, suka ba firistoci hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyu da ɗari shida da kuma shanu ɗari uku.
Ses officiers aussi offrirent ce qu’ils avaient spontanément voué, tant au peuple qu’aux prêtres et aux Lévites. Or Helcias, Zacharie et Jahiel, princes de la maison du Seigneur, donnèrent aux prêtres, pour faire la Pâque, deux mille six cents têtes de menu bétail mêlé et trois cents bœufs.
9 Haka kuma Konaniya tare da Shemahiya da Netanel, ɗan’uwansa, da Hashabiya, Yehiyel da Yozabad, shugabannin Lawiyawa, suka tanadar da hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyar da kuma bijimai ɗari biyar domin Lawiyawa.
Mais Chonénias, Séméias, et même Nathanaël, ses frères, de plus Hasabias, Jéhiel et Jozabad, princes des Lévites, donnèrent aux autres Lévites, pour célébrer la Pâque, cinq mille têtes de menu bétail et cinq cents bœufs.
10 Sa’ad da aka shirya kome don Bikin Ƙetarewar, sai Firistoci tare da Lawiyawa suka tsaya wurin tsayawarsu bisa ga umarnin sarki.
Le service fut donc préparé, et les prêtres se tinrent à leurs fonctions, et les Lévites aussi selon leurs classes, d’après l’ordre du roi.
11 Aka yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, firistoci kuma suka yayyafa jinin da aka ba su, yayinda Lawiyawa suna fiɗan dabbobi.
Ainsi la Pâque fut immolée; les prêtres répandirent de leur propre main le sang, et les Lévites écorchèrent les holocaustes.
12 Suka keɓe hadayun ƙonawa don su ba da su ga ƙungiyoyin iyalan mutane don su miƙa ga Ubangiji, yadda yake a rubuce a Littafin Musa. Suka yi haka da shanun.
Et ils les séparèrent pour les donner dans les maisons et dans les familles de chacun, et pour les offrir au Seigneur, comme il est écrit dans le livre de Moïse; des bœufs aussi, ils firent pareillement.
13 Suka gasa dabbobin Bikin Ƙetarewa a bisa wuta yadda aka tsara, suka dafa hadayu masu tsarki a tukwane, da manyan tukwane, da kuma kwanoni, suka raba su nan da nan ga dukan mutane.
Et ils firent rôtir la Pâque sur le feu, d’après ce qui est écrit dans la loi; mais les victimes pacifiques, ils les firent cuire dans les chaudières, dans les pots et dans les marmites, et les distribuèrent en hâte à tout le peuple;
14 Bayan wannan, suka shirya wa kansu da kuma wa firistoci, saboda firistoci, zuriyar Haruna, suna miƙa hadayun ƙonawa da sashen kitse daga safe har dare. Saboda haka Lawiyawa suka shirya wa kansu da kuma wa firistocin daga zuriyar Haruna.
Et ils en préparèrent ensuite pour eux et pour les prêtres: car les prêtres furent occupés jusqu’à la nuit à l’oblation des holocaustes et des graisses; de là, les Lévites n’en préparèrent pour eux, et pour les prêtres, fils d’Aaron, que les derniers.
15 Mawaƙa zuriyar Asaf, suna a wuraren da Dawuda, Asaf, Heman da Yedutun mai duba na sarki suka tsara. Bai zama lalle matsaran ƙofofi a kowace ƙofa su bar wuraren aikinsu ba, domin’yan’uwansu Lawiyawa sun yi shiri dominsu.
Les chantres, fils d’Asaph, se tenaient aussi dans leur rang, d’après le commandement de David, d’Asaph, d’Héman et d’Iditun, prophètes du roi. Les portiers veillaient à chaque porte, de manière qu’ils ne s’écartaient pas un seul moment de leur ministère; c’est pour cela que les Lévites, leurs frères, leur préparèrent des aliments.
16 Ta haka fa aka yi dukan hidimar Ubangiji a wannan rana, domin su kiyaye Bikin Ƙetarewa, domin kuma su miƙa hadayu na ƙonawa a bisa bagaden Ubangiji, yadda sarki Yosiya ya umarta.
Tout le culte du Seigneur fut donc accompli selon les rites en ce jour-là, pour faire la Pâque, et pour offrir des holocaustes sur l’autel du Seigneur, d’après le commandement du roi Josias.
17 Isra’ilawan da suka kasance a can suka yi Bikin Ƙetarewa a wannan rana, suka kuma kiyaye Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai.
Et les enfants d’Israël qui s’étaient trouvés là firent la Pâque en ce temps, et la solennité des azymes durant sept jours.
18 Ba a taɓa yin Bikin Ƙetarewa haka ba tun zamanin annabi Sama’ila; kuma babu sarkin Isra’ilan da ya taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa kamar yadda Yosiya ya yi, tare da firistoci, Lawiyawa da kuma dukan Yahuda da Isra’ila, waɗanda suke can tare da mutanen Urushalima.
Il n’y eut point de Pâque semblable à celle-ci en Israël, depuis les jours de Samuel le prophète; et même aucun de tous les rois d’Israël ne fit la Pâque comme Josias pour les prêtres, les Lévites, tout Juda et Israël qui s’était trouvé là, et pour tous ceux qui habitaient dans Jérusalem.
19 An yi wannan Bikin Ƙetarewa a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya.
C’est à la dix-huitième année du règne de Josias que cette Pâque fut célébrée.
20 Bayan wannan duka, sa’ad da Yosiya ya shirya haikali, Neko sarkin Masar ya haura don yă yi yaƙi a Karkemish a Yuferites, sai Yosiya ya fita don yă fafata da shi a yaƙi.
Après que Josias eut restauré le temple, Néchao, roi d’Égypte, monta pour combattre à Charcamis près de l’Euphrate: et Josias marcha à sa rencontre.
21 Amma Neko ya aiki’yan saƙo ga Yosiya, yana cewa, “Me ya gama ni da kai, ya Sarkin Yahuda? Ban zo in yi yaƙi da kai ba. Na zo ne in yi yaƙi da gidan da yake gāba da ni! Ka ƙyale ni! Allah ne ya riga ya faɗa mini in hanzarta. Kada ka yi gāba da Allah, wanda yake tare da ni, don kada yă hallaka ka.”
Mais celui-ci, lui ayant envoyé des messagers, dit: Qu’importe à moi et à vous, roi de Juda? Ce n’est pas contre vous que je viens aujourd’hui; mais je combats contre une autre maison, vers laquelle Dieu m’a ordonné de marcher en hâte. Cessez d’agir contre Dieu, qui est avec moi, de peur qu’il ne vous tue.
22 Yosiya fa, bai juya daga gare shi ba, amma ya ɓad da kama don yă yi yaƙin. Bai saurari abin da Neko ya faɗa bisa ga umarnin Allah ba, amma ya tafi ya yaƙe shi a filin Megiddo.
Josias ne voulut point retourner; mais il prépara contre lui un combat, et il n’acquiesça pas aux paroles de Néchao, sorties de la bouche de Dieu; mais il s’avança pour combattre dans le champ de Mageddo
23 Maharba suka harbi Yosiya, sai ya ce wa hafsoshinsa, “Ku ɗauke ni ku fita da ni daga nan; gama an yi mini mummunan rauni.”
Et là, blessé par les archers, il dit à ses serviteurs: Tirez-moi de la bataille, parce que je suis grièvement blessé.
24 Saboda haka suka ɗauke shi a keken yaƙin, suka fitar da shi, suka sa shi a wata keken yaƙin da yake da shi, suka kawo shi Urushalima, inda ya mutu. Aka binne shi a makabartar kakanninsa, sai dukan Yahuda da Urushalima suka yi makoki dominsa.
Ils le transportèrent de son char dans un autre char qui le suivait, selon la coutume des rois, et ils le portèrent à Jérusalem, et il mourut, et fut enseveli dans le mausolée de ses pères; et tout Juda et Jérusalem le pleurèrent;
25 Annabin Irmiya ya tsara waƙoƙin makoki domin Yosiya, wanda har wa yau mawaƙa maza da mata suke rera game da Yosiya. Suka sa waɗannan su zama al’ada a Isra’ila, suna kuma a rubuce cikin Littafin Makoki.
Jérémie surtout, dont les chantres et les chanteuses répètent tous jusqu’au présent jour les lamentations sur Josias; et cela a prévalu comme loi en Israël: voilà qu’on le trouve écrit dans les lamentations.
26 Sauran ayyukan mulkin Yosiya da kuma kyawawan abubuwan da ya yi, bisa ga abin da aka rubuta a Dokar Ubangiji,
Mais le reste des actions de Josias, et ses miséricordes qui sont ordonnées par la loi du Seigneur,
27 dukan ayyukan, daga farko har zuwa ƙarshe, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda.
Comme aussi ses œuvres, les premières et les dernières, sont écrites dans le Livre des rois de Juda et d’Israël.

< 2 Tarihi 35 >