< 2 Tarihi 35 >

1 Yosiya ya yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji a Urushalima, aka kuma yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a ranar goma sha huɗu ga wata na farko.
Or Josias célébra la pâque à l'Éternel, à Jérusalem, et on immola la pâque, le quatorzième jour du premier mois.
2 Ya zaɓi firistoci su yi aikinsu, sai ya ƙarfafa su su yi aikin da kyau a hidimar haikalin Ubangiji.
Et il établit les sacrificateurs dans leurs charges, et les encouragea au service de la maison de l'Éternel.
3 Ya ce wa Lawiyawa waɗanda suke koyar da dukan Isra’ila da kuma waɗanda aka tsarkake wa Ubangiji. “Ku sa akwatin alkawari mai tsarki a cikin haikalin da Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila ya gina. Ba za a riƙa ɗaukansa a kafaɗa ba. Yanzu ku bauta wa Ubangiji Allahnku da kuma mutanensa Isra’ila.
Il dit aussi aux Lévites qui enseignaient tout Israël, et qui étaient consacrés à l'Éternel: Mettez l'arche sainte dans la maison que Salomon, fils de David, roi d'Israël, a bâtie. Vous n'avez plus à la porter sur l'épaule; maintenant, servez l'Éternel, votre Dieu, et son peuple d'Israël.
4 Ku shirya kanku iyali-iyali a sassanku, bisa ga umarnan da Dawuda sarkin Isra’ila da kuma ɗansa Solomon suka rubuta.
Tenez-vous prêts, selon les maisons de vos pères, selon vos divisions, suivant l'écrit de David, roi d'Israël, et suivant l'écrit de Salomon, son fils;
5 “Ku tsaya a tsattsarkan wuri, bisa ga ƙungiyoyin gidajen kakannin’yan’uwanku, waɗanda su ba firistoci ba ne. Kowanne ya sami kashi daga cikin gidan Lawiyawa.
Tenez-vous dans le sanctuaire, selon les classes des maisons des pères, pour vos frères, les enfants du peuple, et selon le partage de la maison des pères des Lévites.
6 Ku yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, ku tsarkake kanku, ku kuma shirya raguna domin’yan’uwanku, kuna yin abin da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.”
Immolez la pâque, sanctifiez-vous, et préparez-la pour vos frères, en faisant selon la parole de l'Éternel prononcée par Moïse.
7 Yosiya ya tanada wa dukan mutanen da ba firistoci ba ne waɗanda suke a wurin, tumaki da awaki dubu talatin don a yanka saboda hadayun Bikin Ƙetarewa, ya kuma ba su shanu dubu uku. Dukan dabbobin kuwa daga garken sarki ne.
Et Josias fit aux gens du peuple, à tous ceux qui se trouvaient là, un présent de menu bétail, en agneaux et en chevreaux, au nombre de trente mille, le tout pour faire la pâque, et de trois mille bœufs; cela fut pris sur les biens du roi.
8 Fadawansa su ma suka ba da taimako da yardar rai ga mutane da kuma firistoci da Lawiyawa. Hilkiya, Zakariya da Yehiyel masu aiki a haikalin Allah, suka ba firistoci hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyu da ɗari shida da kuma shanu ɗari uku.
Et ses chefs firent un présent volontaire au peuple, aux sacrificateurs et aux Lévites. Hilkija, Zacharie et Jéhiel, princes de la maison de Dieu, donnèrent aux sacrificateurs, pour faire la pâque, deux mille six cents agneaux, et trois cents bœufs.
9 Haka kuma Konaniya tare da Shemahiya da Netanel, ɗan’uwansa, da Hashabiya, Yehiyel da Yozabad, shugabannin Lawiyawa, suka tanadar da hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyar da kuma bijimai ɗari biyar domin Lawiyawa.
Conania, Shémaja et Nathanaël, ses frères, et Hashabia, Jéïel et Jozabad, chefs des Lévites, en présentèrent cinq mille aux Lévites pour faire la pâque, et cinq cents bœufs.
10 Sa’ad da aka shirya kome don Bikin Ƙetarewar, sai Firistoci tare da Lawiyawa suka tsaya wurin tsayawarsu bisa ga umarnin sarki.
Le service étant préparé, les sacrificateurs se tinrent à leurs places, ainsi que les Lévites suivant leurs divisions, selon le commandement du roi.
11 Aka yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, firistoci kuma suka yayyafa jinin da aka ba su, yayinda Lawiyawa suna fiɗan dabbobi.
Puis on immola la pâque; et les sacrificateurs répandaient le sang reçu des mains des Lévites, et les Lévites dépouillaient les victimes.
12 Suka keɓe hadayun ƙonawa don su ba da su ga ƙungiyoyin iyalan mutane don su miƙa ga Ubangiji, yadda yake a rubuce a Littafin Musa. Suka yi haka da shanun.
Ils mirent à part les holocaustes, pour les donner aux gens du peuple, suivant les divisions des maisons de leurs pères, afin de les offrir à l'Éternel, selon qu'il est écrit au livre de Moïse; ils firent de même pour les bœufs.
13 Suka gasa dabbobin Bikin Ƙetarewa a bisa wuta yadda aka tsara, suka dafa hadayu masu tsarki a tukwane, da manyan tukwane, da kuma kwanoni, suka raba su nan da nan ga dukan mutane.
Et ils firent cuire la pâque au feu, selon l'ordonnance; et ils firent cuire les choses consacrées, dans des chaudières, des chaudrons et des poêles; et ils s'empressaient de les distribuer à tous les gens du peuple.
14 Bayan wannan, suka shirya wa kansu da kuma wa firistoci, saboda firistoci, zuriyar Haruna, suna miƙa hadayun ƙonawa da sashen kitse daga safe har dare. Saboda haka Lawiyawa suka shirya wa kansu da kuma wa firistocin daga zuriyar Haruna.
Ensuite ils apprêtèrent ce qui était pour eux et pour les sacrificateurs; car les sacrificateurs, enfants d'Aaron, furent occupés jusqu'à la nuit à offrir les holocaustes et les graisses; c'est pourquoi, les Lévites apprêtèrent ce qu'il fallait pour eux et pour les sacrificateurs, enfants d'Aaron.
15 Mawaƙa zuriyar Asaf, suna a wuraren da Dawuda, Asaf, Heman da Yedutun mai duba na sarki suka tsara. Bai zama lalle matsaran ƙofofi a kowace ƙofa su bar wuraren aikinsu ba, domin’yan’uwansu Lawiyawa sun yi shiri dominsu.
Or les chantres, enfants d'Asaph, étaient à leur place, selon le commandement de David, d'Asaph, d'Héman et de Jéduthun, le Voyant du roi; et les portiers étaient à chaque porte. Ils n'eurent pas à interrompre leur service, car les Lévites, leurs frères, apprêtaient ce qui était pour eux.
16 Ta haka fa aka yi dukan hidimar Ubangiji a wannan rana, domin su kiyaye Bikin Ƙetarewa, domin kuma su miƙa hadayu na ƙonawa a bisa bagaden Ubangiji, yadda sarki Yosiya ya umarta.
Ainsi, tout le service de l'Éternel fut organisé en ce jour-là, pour faire la pâque, et pour offrir les holocaustes sur l'autel de l'Éternel, selon le commandement du roi Josias.
17 Isra’ilawan da suka kasance a can suka yi Bikin Ƙetarewa a wannan rana, suka kuma kiyaye Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai.
Les enfants d'Israël qui s'y trouvèrent, célébrèrent donc la pâque, en ce temps-là, et la fête des pains sans levain, pendant sept jours.
18 Ba a taɓa yin Bikin Ƙetarewa haka ba tun zamanin annabi Sama’ila; kuma babu sarkin Isra’ilan da ya taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa kamar yadda Yosiya ya yi, tare da firistoci, Lawiyawa da kuma dukan Yahuda da Isra’ila, waɗanda suke can tare da mutanen Urushalima.
On n'avait point célébré de pâque semblable en Israël, depuis les jours de Samuel, le prophète; et aucun des rois d'Israël n'avait célébré une pâque pareille à celle que célébrèrent Josias, les sacrificateurs et les Lévites, tout Juda et Israël, qui s'y trouvèrent avec les habitants de Jérusalem.
19 An yi wannan Bikin Ƙetarewa a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya.
Cette pâque fut célébrée la dix-huitième année du règne de Josias.
20 Bayan wannan duka, sa’ad da Yosiya ya shirya haikali, Neko sarkin Masar ya haura don yă yi yaƙi a Karkemish a Yuferites, sai Yosiya ya fita don yă fafata da shi a yaƙi.
Après tout cela, quand Josias eut réparé le temple, Néco, roi d'Égypte, monta pour faire la guerre à Carkémish, sur l'Euphrate; et Josias sortit à sa rencontre.
21 Amma Neko ya aiki’yan saƙo ga Yosiya, yana cewa, “Me ya gama ni da kai, ya Sarkin Yahuda? Ban zo in yi yaƙi da kai ba. Na zo ne in yi yaƙi da gidan da yake gāba da ni! Ka ƙyale ni! Allah ne ya riga ya faɗa mini in hanzarta. Kada ka yi gāba da Allah, wanda yake tare da ni, don kada yă hallaka ka.”
Mais Néco lui envoya des messagers, pour lui dire: Qu'y a-t-il entre moi et toi, roi de Juda? Ce n'est pas à toi que j'en veux aujourd'hui, mais à une maison avec laquelle je suis en guerre; et Dieu m'a dit de me hâter. Cesse de t'opposer à Dieu, qui est avec moi, de peur qu'il ne te détruise.
22 Yosiya fa, bai juya daga gare shi ba, amma ya ɓad da kama don yă yi yaƙin. Bai saurari abin da Neko ya faɗa bisa ga umarnin Allah ba, amma ya tafi ya yaƙe shi a filin Megiddo.
Cependant Josias ne voulut point se détourner de lui; il se déguisa pour combattre contre lui; et il n'écouta pas les paroles de Néco, qui procédaient de la bouche de Dieu. Il vint donc pour combattre, dans la plaine de Méguiddo.
23 Maharba suka harbi Yosiya, sai ya ce wa hafsoshinsa, “Ku ɗauke ni ku fita da ni daga nan; gama an yi mini mummunan rauni.”
Et les archers tirèrent sur le roi Josias; et le roi dit à ses serviteurs: Emportez-moi, car je suis fort blessé.
24 Saboda haka suka ɗauke shi a keken yaƙin, suka fitar da shi, suka sa shi a wata keken yaƙin da yake da shi, suka kawo shi Urushalima, inda ya mutu. Aka binne shi a makabartar kakanninsa, sai dukan Yahuda da Urushalima suka yi makoki dominsa.
Et ses serviteurs l'emportèrent du char, le mirent sur un second char qu'il avait, et le menèrent à Jérusalem, et il mourut. Puis il fut enseveli dans les tombeaux de ses pères, et tous ceux de Juda et de Jérusalem pleurèrent Josias.
25 Annabin Irmiya ya tsara waƙoƙin makoki domin Yosiya, wanda har wa yau mawaƙa maza da mata suke rera game da Yosiya. Suka sa waɗannan su zama al’ada a Isra’ila, suna kuma a rubuce cikin Littafin Makoki.
Jérémie fit aussi une complainte sur Josias; et tous les chantres et toutes les chanteuses ont parlé de Josias dans leurs complaintes, jusqu'à ce jour, et on en a fait une coutume en Israël. Voici, ces choses sont écrites dans les complaintes.
26 Sauran ayyukan mulkin Yosiya da kuma kyawawan abubuwan da ya yi, bisa ga abin da aka rubuta a Dokar Ubangiji,
Le reste des actions de Josias, et ses œuvres de piété, conformes à ce qui est écrit dans la loi de l'Éternel,
27 dukan ayyukan, daga farko har zuwa ƙarshe, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda.
Ses premières et ses dernières actions, sont écrites dans le livre des rois d'Israël et de Juda.

< 2 Tarihi 35 >