< 2 Tarihi 35 >

1 Yosiya ya yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji a Urushalima, aka kuma yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a ranar goma sha huɗu ga wata na farko.
Et Josias célébra à Jérusalem la Pâque à l’Éternel; et on égorgea la pâque, le quatorzième jour du premier mois.
2 Ya zaɓi firistoci su yi aikinsu, sai ya ƙarfafa su su yi aikin da kyau a hidimar haikalin Ubangiji.
Et il établit les sacrificateurs dans leurs charges, et les encouragea pour le service de la maison de l’Éternel.
3 Ya ce wa Lawiyawa waɗanda suke koyar da dukan Isra’ila da kuma waɗanda aka tsarkake wa Ubangiji. “Ku sa akwatin alkawari mai tsarki a cikin haikalin da Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila ya gina. Ba za a riƙa ɗaukansa a kafaɗa ba. Yanzu ku bauta wa Ubangiji Allahnku da kuma mutanensa Isra’ila.
Et il dit aux lévites qui enseignaient tout Israël, [et] qui étaient saints, [consacrés] à l’Éternel: Mettez l’arche sainte dans la maison que Salomon, fils de David, roi d’Israël, a bâtie: vous n’avez pas à la porter sur l’épaule; servez maintenant l’Éternel, votre Dieu, et son peuple Israël;
4 Ku shirya kanku iyali-iyali a sassanku, bisa ga umarnan da Dawuda sarkin Isra’ila da kuma ɗansa Solomon suka rubuta.
et préparez-vous, selon vos maisons de pères, selon vos divisions, suivant l’écrit de David, roi d’Israël, et suivant l’écrit de Salomon, son fils;
5 “Ku tsaya a tsattsarkan wuri, bisa ga ƙungiyoyin gidajen kakannin’yan’uwanku, waɗanda su ba firistoci ba ne. Kowanne ya sami kashi daga cikin gidan Lawiyawa.
et placez-vous dans le lieu saint pour les sections des maisons de pères de vos frères, les fils du peuple, et selon les divisions des maisons de pères des lévites;
6 Ku yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, ku tsarkake kanku, ku kuma shirya raguna domin’yan’uwanku, kuna yin abin da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.”
et égorgez la pâque, et sanctifiez-vous, et préparez [la pâque] pour vos frères, afin d’agir conformément à la parole de l’Éternel par Moïse.
7 Yosiya ya tanada wa dukan mutanen da ba firistoci ba ne waɗanda suke a wurin, tumaki da awaki dubu talatin don a yanka saboda hadayun Bikin Ƙetarewa, ya kuma ba su shanu dubu uku. Dukan dabbobin kuwa daga garken sarki ne.
Et Josias donna aux fils du peuple du menu bétail, des agneaux et des chevreaux, au nombre de 30 000, le tout pour les pâques, pour tous ceux qui se trouvaient là, et 3 000 bœufs; cela fut [pris] sur les biens du roi.
8 Fadawansa su ma suka ba da taimako da yardar rai ga mutane da kuma firistoci da Lawiyawa. Hilkiya, Zakariya da Yehiyel masu aiki a haikalin Allah, suka ba firistoci hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyu da ɗari shida da kuma shanu ɗari uku.
Et ses chefs donnèrent volontairement pour le peuple, pour les sacrificateurs et pour les lévites. Hilkija, et Zacharie, et Jekhiel, les princes de la maison de Dieu, donnèrent aux sacrificateurs, pour les pâques, 2 600 [têtes de menu bétail] et 300 de gros bétail.
9 Haka kuma Konaniya tare da Shemahiya da Netanel, ɗan’uwansa, da Hashabiya, Yehiyel da Yozabad, shugabannin Lawiyawa, suka tanadar da hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyar da kuma bijimai ɗari biyar domin Lawiyawa.
Et Conania, et Shemahia et Nethaneël, ses frères, et Hashabia, et Jehiel, et Jozabad, chefs des lévites, donnèrent pour les lévites 5 000 [têtes de menu bétail] pour les pâques, et 500 de gros bétail.
10 Sa’ad da aka shirya kome don Bikin Ƙetarewar, sai Firistoci tare da Lawiyawa suka tsaya wurin tsayawarsu bisa ga umarnin sarki.
Et le service fut réglé, et les sacrificateurs se tinrent à leurs places, et les lévites dans leurs divisions, selon le commandement du roi.
11 Aka yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, firistoci kuma suka yayyafa jinin da aka ba su, yayinda Lawiyawa suna fiɗan dabbobi.
Et ils égorgèrent la pâque; et les sacrificateurs firent aspersion [du sang qu’ils recevaient] de leurs mains, et les lévites écorchaient [les victimes].
12 Suka keɓe hadayun ƙonawa don su ba da su ga ƙungiyoyin iyalan mutane don su miƙa ga Ubangiji, yadda yake a rubuce a Littafin Musa. Suka yi haka da shanun.
Et ils mirent à part les holocaustes pour les donner aux sections des maisons de pères des fils du peuple, pour les présenter à l’Éternel, selon qu’il est écrit dans le livre de Moïse; et [ils firent] de même pour le gros bétail.
13 Suka gasa dabbobin Bikin Ƙetarewa a bisa wuta yadda aka tsara, suka dafa hadayu masu tsarki a tukwane, da manyan tukwane, da kuma kwanoni, suka raba su nan da nan ga dukan mutane.
Et ils firent cuire la pâque au feu, selon l’ordonnance; et les choses saintes, ils les firent cuire dans des chaudières, et des chaudrons, et des poêles, et les distribuèrent à la hâte à tous les fils du peuple.
14 Bayan wannan, suka shirya wa kansu da kuma wa firistoci, saboda firistoci, zuriyar Haruna, suna miƙa hadayun ƙonawa da sashen kitse daga safe har dare. Saboda haka Lawiyawa suka shirya wa kansu da kuma wa firistocin daga zuriyar Haruna.
Et ensuite, ils préparèrent [ce qui était] pour eux et pour les sacrificateurs; car les sacrificateurs, fils d’Aaron, [furent occupés] jusqu’à la nuit à offrir les holocaustes et les graisses; et les lévites préparèrent [ce qui était] pour eux-mêmes, et pour les sacrificateurs, fils d’Aaron.
15 Mawaƙa zuriyar Asaf, suna a wuraren da Dawuda, Asaf, Heman da Yedutun mai duba na sarki suka tsara. Bai zama lalle matsaran ƙofofi a kowace ƙofa su bar wuraren aikinsu ba, domin’yan’uwansu Lawiyawa sun yi shiri dominsu.
Et les chantres, fils d’Asaph, étaient à leur place, selon le commandement de David, et d’Asaph, et d’Héman, et de Jeduthun, le voyant du roi; et les portiers étaient à chaque porte: ils n’eurent pas à se retirer de leur service, car leurs frères, les lévites, préparaient [ce qui était] pour eux.
16 Ta haka fa aka yi dukan hidimar Ubangiji a wannan rana, domin su kiyaye Bikin Ƙetarewa, domin kuma su miƙa hadayu na ƙonawa a bisa bagaden Ubangiji, yadda sarki Yosiya ya umarta.
Et tout le service de l’Éternel fut réglé, en ce jour-là, pour faire la Pâque, et pour offrir des holocaustes sur l’autel de l’Éternel, selon le commandement du roi Josias.
17 Isra’ilawan da suka kasance a can suka yi Bikin Ƙetarewa a wannan rana, suka kuma kiyaye Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai.
Et les fils d’Israël présents, firent la Pâque en ce temps-là, et la fête des pains sans levain pendant sept jours.
18 Ba a taɓa yin Bikin Ƙetarewa haka ba tun zamanin annabi Sama’ila; kuma babu sarkin Isra’ilan da ya taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa kamar yadda Yosiya ya yi, tare da firistoci, Lawiyawa da kuma dukan Yahuda da Isra’ila, waɗanda suke can tare da mutanen Urushalima.
Et on n’avait point célébré en Israël de Pâque semblable depuis les jours de Samuel, le prophète; et aucun des rois d’Israël n’avait célébré une Pâque comme celle que firent Josias, et les sacrificateurs et les lévites, et tout Juda et Israël, qui s’y trouvèrent, et les habitants de Jérusalem.
19 An yi wannan Bikin Ƙetarewa a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya.
Cette Pâque fut célébrée la dix-huitième année du règne de Josias.
20 Bayan wannan duka, sa’ad da Yosiya ya shirya haikali, Neko sarkin Masar ya haura don yă yi yaƙi a Karkemish a Yuferites, sai Yosiya ya fita don yă fafata da shi a yaƙi.
Après tout cela, quand Josias eut mis en état la maison, Neco, roi d’Égypte, monta pour faire la guerre à Carkemish sur l’Euphrate; et Josias sortit à sa rencontre.
21 Amma Neko ya aiki’yan saƙo ga Yosiya, yana cewa, “Me ya gama ni da kai, ya Sarkin Yahuda? Ban zo in yi yaƙi da kai ba. Na zo ne in yi yaƙi da gidan da yake gāba da ni! Ka ƙyale ni! Allah ne ya riga ya faɗa mini in hanzarta. Kada ka yi gāba da Allah, wanda yake tare da ni, don kada yă hallaka ka.”
Et [Neco] lui envoya des messagers, disant: Qu’y a-t-il entre moi et toi, roi de Juda? Ce n’est pas contre toi que je viens aujourd’hui, mais contre la maison avec laquelle je suis en guerre, et Dieu m’a dit de me hâter. Désiste-toi de [t’opposer à] Dieu, qui est avec moi, afin qu’il ne te détruise pas.
22 Yosiya fa, bai juya daga gare shi ba, amma ya ɓad da kama don yă yi yaƙin. Bai saurari abin da Neko ya faɗa bisa ga umarnin Allah ba, amma ya tafi ya yaƙe shi a filin Megiddo.
Et Josias ne se détourna pas de lui, mais il se déguisa pour combattre contre lui; et il n’écouta pas les paroles de Neco, [qui venaient] de la bouche de Dieu. Et il vint pour combattre dans la vallée de Meguiddo.
23 Maharba suka harbi Yosiya, sai ya ce wa hafsoshinsa, “Ku ɗauke ni ku fita da ni daga nan; gama an yi mini mummunan rauni.”
Et les archers tirèrent sur le roi Josias; et le roi dit à ses serviteurs: Ôtez-moi d’ici, car je suis grièvement blessé.
24 Saboda haka suka ɗauke shi a keken yaƙin, suka fitar da shi, suka sa shi a wata keken yaƙin da yake da shi, suka kawo shi Urushalima, inda ya mutu. Aka binne shi a makabartar kakanninsa, sai dukan Yahuda da Urushalima suka yi makoki dominsa.
Et ses serviteurs l’ôtèrent du char, et le mirent sur un second char qu’il avait, et le conduisirent à Jérusalem. Et il mourut; et on l’enterra dans les sépulcres de ses pères; et tout Juda et Jérusalem menèrent deuil sur Josias.
25 Annabin Irmiya ya tsara waƙoƙin makoki domin Yosiya, wanda har wa yau mawaƙa maza da mata suke rera game da Yosiya. Suka sa waɗannan su zama al’ada a Isra’ila, suna kuma a rubuce cikin Littafin Makoki.
Et Jérémie fit des lamentations sur Josias; et tous les chanteurs et toutes les chanteuses ont parlé de Josias dans leurs lamentations jusqu’à aujourd’hui; et on l’a établi comme ordonnance pour Israël. Et, voici, cela est écrit dans les Lamentations.
26 Sauran ayyukan mulkin Yosiya da kuma kyawawan abubuwan da ya yi, bisa ga abin da aka rubuta a Dokar Ubangiji,
Et le reste des actes de Josias, et ses actions pieuses, conformément à ce qui est écrit dans la loi de l’Éternel,
27 dukan ayyukan, daga farko har zuwa ƙarshe, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda.
et ses actes, les premiers et les derniers, voici, ils sont écrits dans le livre des rois d’Israël et de Juda.

< 2 Tarihi 35 >