< 2 Tarihi 35 >

1 Yosiya ya yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji a Urushalima, aka kuma yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a ranar goma sha huɗu ga wata na farko.
Og Josias holdt Paaske for Herren i Jerusalem, og de slagtede Paaskelam paa den fjortende Dag i den første Maaned.
2 Ya zaɓi firistoci su yi aikinsu, sai ya ƙarfafa su su yi aikin da kyau a hidimar haikalin Ubangiji.
Og han beskikkede Præsterne til det, de skulde varetage, og styrkede dem til deres Tjeneste i Herrens Hus.
3 Ya ce wa Lawiyawa waɗanda suke koyar da dukan Isra’ila da kuma waɗanda aka tsarkake wa Ubangiji. “Ku sa akwatin alkawari mai tsarki a cikin haikalin da Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila ya gina. Ba za a riƙa ɗaukansa a kafaɗa ba. Yanzu ku bauta wa Ubangiji Allahnku da kuma mutanensa Isra’ila.
Og han sagde til Leviterne, som underviste al Israel om de hellige Ting for Herren: Sætter den hellige Ark i Huset, som Salomo, Davids Søn, Israels Konge, har bygget; I have ingen Byrde at bære paa Skuldre, tjener nu Herren eders Gud og hans Folk Israel,
4 Ku shirya kanku iyali-iyali a sassanku, bisa ga umarnan da Dawuda sarkin Isra’ila da kuma ɗansa Solomon suka rubuta.
og bereder eder efter eders Fædrenehuse, efter eders Skifter, som det er foreskrevet af David, Israels Konge, og foreskrevet af Salomo, hans Søn;
5 “Ku tsaya a tsattsarkan wuri, bisa ga ƙungiyoyin gidajen kakannin’yan’uwanku, waɗanda su ba firistoci ba ne. Kowanne ya sami kashi daga cikin gidan Lawiyawa.
og staar i Helligdommen efter Afdelingerne af Fædrenehusene iblandt eders Brødre, Folkets Børn, og efter hver Afdeling af Fædrenes Huse iblandt Leviterne;
6 Ku yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, ku tsarkake kanku, ku kuma shirya raguna domin’yan’uwanku, kuna yin abin da Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.”
og slagter Paaskelam, helliger eder og bereder det for eders Brødre, idet I gøre efter Herrens Ord ved Mose.
7 Yosiya ya tanada wa dukan mutanen da ba firistoci ba ne waɗanda suke a wurin, tumaki da awaki dubu talatin don a yanka saboda hadayun Bikin Ƙetarewa, ya kuma ba su shanu dubu uku. Dukan dabbobin kuwa daga garken sarki ne.
Og Josias gav Folkets Børn smaat Kvæg, Lam og Kid, alt sammen til Paaske for alle dem, som vare til Stede, efter Tallet tredive Tusinde, og tre Tusinde Øksne; disse bleve givne af Kongens Gods.
8 Fadawansa su ma suka ba da taimako da yardar rai ga mutane da kuma firistoci da Lawiyawa. Hilkiya, Zakariya da Yehiyel masu aiki a haikalin Allah, suka ba firistoci hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyu da ɗari shida da kuma shanu ɗari uku.
Ogsaa gave hans Fyrster en frivillig Gave til Folket, til Præsterne og til Leviterne, nemlig Hilkia og Sakaria og Jehiel, Øverster i Guds Hus, gave Præsterne to Tusinde og seks Hundrede Stykker smaat Kvæg til Paaske og tre Hundrede Øksne.
9 Haka kuma Konaniya tare da Shemahiya da Netanel, ɗan’uwansa, da Hashabiya, Yehiyel da Yozabad, shugabannin Lawiyawa, suka tanadar da hadayun Bikin Ƙetarewa dubu biyar da kuma bijimai ɗari biyar domin Lawiyawa.
Men Kanania og Semaja og Nethaneel, hans Brødre, ligeledes Hasabia og Jehiel og Josabad, Leviternes Øverster, gave fem Tusinde Stykker smaat Kvæg til Paaske og fem Hundrede Øksne.
10 Sa’ad da aka shirya kome don Bikin Ƙetarewar, sai Firistoci tare da Lawiyawa suka tsaya wurin tsayawarsu bisa ga umarnin sarki.
Saa blev Tjenesten beredet; og Præsterne stode paa deres Sted, og Leviterne efter deres Skifter ifølge Kongens Befaling,
11 Aka yanka ragunan Bikin Ƙetarewa, firistoci kuma suka yayyafa jinin da aka ba su, yayinda Lawiyawa suna fiɗan dabbobi.
og disse slagtede Paaskelammene, og Præsterne stænkede med Blodet, som de modtoge af deres Hænder, og Leviterne flaaede Lammene.
12 Suka keɓe hadayun ƙonawa don su ba da su ga ƙungiyoyin iyalan mutane don su miƙa ga Ubangiji, yadda yake a rubuce a Littafin Musa. Suka yi haka da shanun.
Og de skilte Brændofferet derfra, at de kunde give det til Afdelingerne af Fædrenehusene iblandt Folkets Børn for at ofre det til Herren, som der er skrevet i Mose Bog; og ligervis med Øksnene.
13 Suka gasa dabbobin Bikin Ƙetarewa a bisa wuta yadda aka tsara, suka dafa hadayu masu tsarki a tukwane, da manyan tukwane, da kuma kwanoni, suka raba su nan da nan ga dukan mutane.
Og de stegte Paaskelammet ved Ilden paa sædvanlig Vis, men det, som var helliget, kogte de i Gryder og i Kedler og i Pander, og de sendte det i Hast til alle Folkets Børn.
14 Bayan wannan, suka shirya wa kansu da kuma wa firistoci, saboda firistoci, zuriyar Haruna, suna miƙa hadayun ƙonawa da sashen kitse daga safe har dare. Saboda haka Lawiyawa suka shirya wa kansu da kuma wa firistocin daga zuriyar Haruna.
Og derefter tilberedte de for sig og for Præsterne; thi Præsterne, Arons Børn, havde Brændofferet og Fedtstykkerne at ofre indtil Natten; derfor tilberedte Leviterne for sig og for Præsterne, Arons Børn.
15 Mawaƙa zuriyar Asaf, suna a wuraren da Dawuda, Asaf, Heman da Yedutun mai duba na sarki suka tsara. Bai zama lalle matsaran ƙofofi a kowace ƙofa su bar wuraren aikinsu ba, domin’yan’uwansu Lawiyawa sun yi shiri dominsu.
Og Sangerne, Asafs Børn, stode paa deres Sted efter Davids og Asafs og Hemans og Jeduthuns, Kongens Seeres, Bud og Portnerne ved hver Port; de maatte ikke vige fra deres Tjeneste, thi deres Brødre Leviterne tilberedte for dem.
16 Ta haka fa aka yi dukan hidimar Ubangiji a wannan rana, domin su kiyaye Bikin Ƙetarewa, domin kuma su miƙa hadayu na ƙonawa a bisa bagaden Ubangiji, yadda sarki Yosiya ya umarta.
Saa blev al Herrens Tjeneste beskikket paa samme Dag med at holde Paaske og at ofre Brændofre paa Herrens Alter efter Kong Josias Befaling.
17 Isra’ilawan da suka kasance a can suka yi Bikin Ƙetarewa a wannan rana, suka kuma kiyaye Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai.
Saa holdt Israels Børn, som vare til Stede, Paasken paa den samme Tid og de usyrede Brøds Højtid syv Dage.
18 Ba a taɓa yin Bikin Ƙetarewa haka ba tun zamanin annabi Sama’ila; kuma babu sarkin Isra’ilan da ya taɓa yin irin Bikin Ƙetarewa kamar yadda Yosiya ya yi, tare da firistoci, Lawiyawa da kuma dukan Yahuda da Isra’ila, waɗanda suke can tare da mutanen Urushalima.
Og der var ikke holdt Paaske som denne i Israel fra Profeten Samuels Dage af, og ingen Konge i Israel havde holdt saadan Paaske, som Josias holdt med Præsterne og Leviterne og hele Juda og Israel, som vare til Stede, og Indbyggerne i Jerusalem.
19 An yi wannan Bikin Ƙetarewa a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya.
I det attende Josias's Regerings Aar blev denne Paaske holdt.
20 Bayan wannan duka, sa’ad da Yosiya ya shirya haikali, Neko sarkin Masar ya haura don yă yi yaƙi a Karkemish a Yuferites, sai Yosiya ya fita don yă fafata da shi a yaƙi.
Efter alt dette, da Josias havde istandsat Huset, drog Neko, Kongen af Ægypten, op at stride ved Karkemis ved Frat, og Josias drog ud imod ham.
21 Amma Neko ya aiki’yan saƙo ga Yosiya, yana cewa, “Me ya gama ni da kai, ya Sarkin Yahuda? Ban zo in yi yaƙi da kai ba. Na zo ne in yi yaƙi da gidan da yake gāba da ni! Ka ƙyale ni! Allah ne ya riga ya faɗa mini in hanzarta. Kada ka yi gāba da Allah, wanda yake tare da ni, don kada yă hallaka ka.”
Da sendte han Bud til ham og lod sige: Hvad har jeg at gøre med dig, Judas Konge? imod dig kommer jeg ikke paa denne Dag, men imod det Hus, som har Krig med mig, og Gud har sagt, at jeg skulde haste; hold op med at være imod Gud, som er med mig, at han ikke lægger dig øde!
22 Yosiya fa, bai juya daga gare shi ba, amma ya ɓad da kama don yă yi yaƙin. Bai saurari abin da Neko ya faɗa bisa ga umarnin Allah ba, amma ya tafi ya yaƙe shi a filin Megiddo.
Dog vendte Josias ikke sit Ansigt bort fra ham, men forklædte sig for at stride imod ham og lød ikke Nekos Ord, som vare fra Guds Mund, men han kom at stride i Megiddo Dal.
23 Maharba suka harbi Yosiya, sai ya ce wa hafsoshinsa, “Ku ɗauke ni ku fita da ni daga nan; gama an yi mini mummunan rauni.”
Og Skytterne skøde paa Kong Josias; da sagde Kongen til sine Tjenere: Fører mig bort, thi jeg er svarlig saaret.
24 Saboda haka suka ɗauke shi a keken yaƙin, suka fitar da shi, suka sa shi a wata keken yaƙin da yake da shi, suka kawo shi Urushalima, inda ya mutu. Aka binne shi a makabartar kakanninsa, sai dukan Yahuda da Urushalima suka yi makoki dominsa.
Og hans Tjenere førte ham bort fra Vognen og lode ham køre bort paa den anden Vogn, som han havde, og førte ham til Jerusalem, og han døde og blev begraven i sine Fædres Grave; og hele Juda og Jerusalem sørgede over Josias.
25 Annabin Irmiya ya tsara waƙoƙin makoki domin Yosiya, wanda har wa yau mawaƙa maza da mata suke rera game da Yosiya. Suka sa waɗannan su zama al’ada a Isra’ila, suna kuma a rubuce cikin Littafin Makoki.
Og Jeremias sang en Klagesang over Josias, i lige Maade talte alle Sangerne og Sangerskerne i deres Klagesange om Josias indtil denne Dag, og de gjorde en Skik deraf i Israel; og se, de ere opskrevne iblandt Klagesangene.
26 Sauran ayyukan mulkin Yosiya da kuma kyawawan abubuwan da ya yi, bisa ga abin da aka rubuta a Dokar Ubangiji,
Men det øvrige at Josias's Handeler, og hans fromme Gerninger, eftersom skrevet er i Herrens Lov,
27 dukan ayyukan, daga farko har zuwa ƙarshe, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda.
ja hans Handeler, de første og de sidste, se, de ere skrevne i Israels og Judas Kongers Bog.

< 2 Tarihi 35 >