< 2 Tarihi 34 >
1 Yosiya yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara talatin da ɗaya.
Jošíja je bil star osem let, ko je začel kraljevati in v Jeruzalemu je kraljeval enaintrideset let.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma yi tafiya a hanyoyin kakansa Dawuda, ba tare da juye dama ko hagu ba.
Delal je to, kar je bilo pravilno v Gospodovih očeh in hodil po poteh svojega očeta Davida in se ni nagnil niti k desni roki niti k levi.
3 A shekara ta takwas ta mulkinsa, yayinda yake matashi, sai ya fara neman Allah na kakansa Dawuda. A shekara ta goma sha biyunsa ya fara tsabtacce Yahuda da Urushalima daga masujadan kan tudu, ginshiƙan Ashera, sassaƙaƙƙun gumaka da kuma siffofin da aka yi zubi.
Kajti v osmem letu svojega kraljevanja, ko je bil še mlad, je začel iskati Boga svojega očeta Davida in v dvanajstem letu je začel čistiti Juda in Jeruzalem pred visokimi kraji, ašerami, izrezljanimi podobami in ulitimi podobami.
4 A ƙarƙashin umarninsa aka rurrushe bagadan Ba’al, ya kuma tumɓuke bagadan ƙona turare waɗanda suke a bisansu, ya farfashe ginshiƙan Ashera da kuma sassaƙaƙƙun siffofi. Ya ragargaza waɗannan kucu-kucu, ya barbaɗa su a kan kaburburan waɗanda suka miƙa musu hadayu.
V njegovi prisotnosti so porušili Báalove oltarje in podobe, ki so bile visoko nad njimi, je posekal. Ašere, izrezljane podobe in ulite podobe je zdrobil na koščke in iz njih naredil prah in ga raztresel po grobovih tistih, ki so jim žrtvovali.
5 Ya ƙone ƙasusuwan firistocin gumaka a kan bagaden da a dā suke miƙa hadayunsu, ta haka ya tsabtacce Yahuda da Urushalima.
Kosti duhovnikov je sežgal na njihovih oltarjih ter očistil Juda in Jeruzalem.
6 Ya yi haka cikin garuruwan Manasse, Efraim da Simeyon, har zuwa Naftali, da kuma cikin kangwayen kewayensu,
Tako je storil v mestih Manáseja, Efrájima in Simeona, celo do Neftálija, z njihovimi motikami naokoli.
7 ya farfashe bagadai da ginshiƙan Ashera; ya niƙa gumaka suka zama gari, ya kuma yayyanka dukan bagadan turare kucu-kucu ko’ina a Isra’ila. Sa’an nan ya koma Urushalima.
Ko je porušil oltarje in ašere in je rezane podobe poteptal v prah in posekal vse malike po vsej izraelski deželi, se je vrnil v Jeruzalem.
8 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya, ya tsarkake ƙasar da haikalin, ya aiki Shafan ɗan Azaliya da Ma’asehiya mai mulkin birni, tare da Yowa ɗan Yowahaz, marubuci, su gyara haikalin Ubangiji Allah.
Torej v osemnajstem letu njegovega kraljevanja, ko je očistil deželo in hišo, je poslal Acaljájevega sina Šafána, voditelja mesta Maasejája in Joaházovega sina letopisca Joáha, da popravi hišo Gospoda, svojega Boga.
9 Suka tafi wurin Hilkiya babban firist suka ba shi kuɗin da aka kawo cikin haikalin Allah, wanda Lawiyawa masu tsaron ƙofofi sun tattara daga mutanen Manasse, Efraim da dukan raguwar Isra’ila da kuma daga dukan mutanen Yahuda da Benyamin da kuma mazaunan Urushalima.
Ko so prišli k vélikemu duhovniku Hilkijáju so izročili denar, ki je bil prinesen v Božjo hišo, ki so ga zbrali Lévijevci, ki so varovali vrata, iz roke Manáseja, Efrájima in vsega Izraelovega preostanka in od vsega Juda in Benjamina in se vrnili v Jeruzalem.
10 Sa’an nan suka danƙa su ga mutanen da aka naɗa su lura da aiki a kan haikalin Ubangiji. Waɗannan mutane ne suke biyan ma’aikatan da suka gyara suka kuma mai da haikalin.
Položili so ga v roko delavcev, ki so imeli nadzor nad Gospodovo hišo in ga izročili delavcem, ki so delali v Gospodovi hiši, da hišo popravijo in izboljšajo.
11 Suka kuma ba da kuɗi ga kafintoci da magina don su sayi sassaƙaƙƙun duwatsu, da katakai don yin tsaiko da tankar ginin da sarakunan Yahuda suka bari yă fāɗi ya zama kango.
Izročila sta ga celo rokodelcem in graditeljem, da kupijo klesan kamen, les za vezi in da tlakujejo hiše, ki so jih Judovi kralji uničili.
12 Mutanen fa suka yi aiki da aminci. Shugabanninsu, su ne Yahat da Obadiya, Lawiyawa zuriyar Merari da Zakariya da Meshullam, zuriyar Kohat. Dukan Lawiyawa waɗanda suke gwanaye a kayan kiɗi,
Možje so zvesto opravljali delo in njihovi nadzorniki so bili Jahat in Obadjá, Lévijevca izmed Meraríjevih sinov; Zeharjá in Mešulám izmed Kehátovih sinov, da bi ga nadzirali in drugi izmed Lévijevcev, vsi, ki so vešči glasbenih instrumentov.
13 sun lura da ma’aikata, suka kuma lura da dukan masu aiki daga aiki zuwa aiki. Waɗansu Lawiyawan su ne marubuta, magatakarda da kuma masu tsaron ƙofofi.
Bili so tudi nad nosilci bremen in bili so nadzorniki vseh teh, ki so na kakršen koli način opravljali delo. Izmed Lévijevcev so bili pisarji, častniki in vratarji.
14 Yayinda suke fitar da kuɗin da aka kai cikin haikalin Ubangiji, sai Hilkiya firist ya sami Littafin Dokar Ubangiji da aka bayar ta wurin Musa.
Ko so jemali ven denar, ki je bil prinesen v Gospodovo hišo, je duhovnik Hilkijá našel knjigo Gospodove postave, ki je bila dana po Mojzesu.
15 Hilkiya ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a cikin haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan.
Hilkijá je odgovoril in pisarju Šafánu rekel: »V Gospodovi hiši sem našel knjigo postave.« In Hilkijá je knjigo izročil Šafánu.
16 Sa’an nan Shafan ya ɗauki littafin zuwa wurin sarki, ya faɗa masa, “Manyan ma’aikatanka suna yin kome da aka sa su.
Šafán je knjigo odnesel h kralju in [poleg tega] kralju prinesel besedo, rekoč: »Vse, kar je bilo poverjeno tvojim služabnikom, so to storili.«
17 Mun ɗauke kuɗin da an ajiye a haikalin Ubangiji muka ba wa masu aiki da waɗanda suke lura da su.”
Skupaj so zbrali denar, ki je bil najden v Gospodovi hiši ter ga izročili v roko nadzornikov in delavcev.
18 Sa’an nan Shafan magatakarda ya sanar da sarki ya ce, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta daga cikinsa a gaban sarki.
Potem je pisar Šafán povedal kralju, rekoč: »Duhovnik Hilkijá mi je izročil knjigo.« In Šafán jo je bral pred kraljem.
19 Da sarki ya ji kalmomin Doka, sai ya yage rigunansa.
Zgodilo se je, ko je kralj slišal besede postave, da je pretrgal svoja oblačila.
20 Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya, Ahikam ɗan Shafan, Abdon ɗan Mika, Shafan magatakarda da kuma Asahiya mai hidimar sarki.
Kralj je ukazal Hilkijáju, Šafánovemu sinu Ahikámu, Mihajájevemu sinu Abdónu, pisarju Šafánu in kraljevemu služabniku Asajáju, rekoč:
21 Ya ce, “Ku tafi ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da kuma saboda raguwa a Isra’ila da Yahuda game da abin da aka rubuta a wannan littafin da aka samu. Fushin Ubangiji mai girma ne da aka zuba a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye maganar Ubangiji ba; ba su aikata bisa ga dukan abin da yake a rubuce a wannan littafi ba.”
»Pojdite, vprašajte Gospoda zame in za tiste, ki so preostali v Izraelu in Judu, glede besed knjige, ki se je našla, kajti velik je Gospodov bes, ki je izlit na nas, ker se naši očetje niso držali Gospodove besede, da bi delali po vsem, kar je napisano v tej knjigi.«
22 Hilkiya tare da waɗanda sarki ya aika, suka tafi suka yi magana da annabiya Hulda, wadda take matar Shallum ɗan Tokhat ɗan Hasra, mai tsaron wurin ajiyar riguna. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
Hilkijá in tisti, ki jih je kralj določil, so odšli k prerokinji Huldi, ženi Šalúma, Tikvájevega sina, Hasrájevega sina, varuha garderobe (torej prebivala je v Jeruzalemu, v drugem okraju) in ji prav tako govorili.
23 Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce faɗa wa mutumin da ya aike ku gare ni,
Odgovorila jim je: »Tako govori Gospod, Izraelov Bog: ›Povejte človeku, ki vas je poslal k meni:
24 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce zai kawo masifa a wannan wuri da mutanensa, dukan la’anar da aka rubuta a cikin littafin da aka karanta a gaban sarkin Yahuda.
›Tako govori Gospod: ›Glejte, zlo bom privedel nad ta kraj in nad njegove prebivalce, celó vsa prekletstva, ki so zapisana v knjigi, ki so jo brali pred Judovim kraljem,
25 Domin sun yashe ni suka kuma ƙone turare wa waɗansu alloli, suka tsokane ni in yi fushi ta wurin dukan abin da hannuwansu suka yi, fushina zai zuba a kan wannan wuri, ba kuma za a kwantar da shi ba.’
ker so me zapustili in zažigali kadilo drugim bogovom, da bi me lahko dražili do jeze z vsemi deli svojih rok, zato bo moj bes izlit na ta kraj in ne bo pogašen.
26 Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yake cewa game da kalmomin da ka ji.
Kar se tiče Judovega kralja, ki vas je poslal, da poizveste od Gospoda, mu boste rekli takole: ›Tako govori Gospod, Izraelov Bog, glede besed, ki si jih slišal:
27 Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Allah sa’ad da ka ji abin da ya yi magana a kan wannan wuri da mutanensa, domin kuma ka ƙasƙantar da kanka a gabana, ka yage rigunanka ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
›Ker je bilo tvoje srce nežno in si se ponižal pred Bogom, ko si slišal njegove besede zoper to mesto in zoper njegove prebivalce in se ponižuješ pred menoj in si pretrgal svoja oblačila in jokal pred menoj; celo tudi jaz sem te slišal, ‹ govori Gospod.
28 Yanzu zan tara ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka ba za su ga dukan masifar da zan kawo a kan wannan wuri da kuma a kan waɗanda suke zama a nan ba.’” Sai suka kai amsar wa sarki.
›Glej, zbral te bom k tvojim očetom in v miru boš zbran k svojemu grobu niti tvoje oči ne bodo videle vsega zla, ki ga bom privedel nad ta kraj in nad prebivalce istega.‹« Tako so kralju ponovno prinesli besedo.
29 Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
Potem je kralj poslal in zbral skupaj vse starešine iz Juda in Jeruzalema.
30 Ya haura zuwa haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, mutanen Urushalima, firistoci da Lawiyawa, dukan mutane daga ƙarami zuwa babba. Ya karanta dukan kalmomin Littafin Alkawari wanda aka samu a cikin haikalin Ubangiji a kunnuwansu.
Kraj je odšel gor v Gospodovo hišo in vsi Judovi možje, prebivalci Jeruzalema, duhovniki, Lévijevci in vse ljudstvo, veliki in mali, in na njihova ušesa je bral vse besede knjige zaveze, ki se je našla v Gospodovi hiši.
31 Sai sarkin ya miƙe tsaye a inda yake, ya sabunta alkawari a gaban Ubangiji, don yă bi Ubangiji yă kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa da kuma farillansa da dukan zuciyarsa da kuma dukan ransa, ya kuma yi biyayya da kalmomin alkawarin da aka rubuta a cikin wannan littafi.
Kralj je stal na svojem mestu in sklenil zavezo pred Gospodom, da hodi za Gospodom in da se drži njegovih zapovedi, njegovih pričevanj in njegovih zapovedi z vsem svojim srcem in z vso svojo dušo, da izpolni besede zaveze, ki so zapisane v tej knjigi.
32 Sa’an nan ya sa kowa a Urushalima da Benyamin ya yi alkawari ga wannan; mutanen Urushalima suka aikata wannan bisa ga alkawarin Allah, Allah na kakanninsu.
Vsem, ki so bili prisotni v Jeruzalemu in Benjaminu, je velel, da pristopijo k temu. Prebivalci Jeruzalema so storili glede na zavezo Boga, Boga svojih očetov.
33 Yosiya ya fitar da dukan gumakan banƙyama daga dukan yankunan Isra’ilawa, ya kuma sa dukan waɗanda suke a Isra’ila su bauta wa Ubangiji Allahnsu. Muddin ransa, ba su fasa bin Ubangiji Allah na kakanninsu ba.
Jošíja je odvzel vse ogabnosti iz vseh dežel, ki so pripadale Izraelovim otrokom in pripravil vse, ki so bili prisotni v Izraelu, da služijo, torej da služijo Gospodu, svojemu Bogu. In vse svoje dni se niso odvrnili od sledenja Gospodu, Bogu svojih očetov.