< 2 Tarihi 34 >

1 Yosiya yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara talatin da ɗaya.
Josias var otte Aar gammel, der han blev Konge, og regerede et og tredive Aar i Jerusalem.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma yi tafiya a hanyoyin kakansa Dawuda, ba tare da juye dama ko hagu ba.
Og han gjorde det, som var ret for Herrens Øjne, og vandrede i Davids, sin Faders, Veje og veg hverken til højre eller venstre Side.
3 A shekara ta takwas ta mulkinsa, yayinda yake matashi, sai ya fara neman Allah na kakansa Dawuda. A shekara ta goma sha biyunsa ya fara tsabtacce Yahuda da Urushalima daga masujadan kan tudu, ginshiƙan Ashera, sassaƙaƙƙun gumaka da kuma siffofin da aka yi zubi.
Thi i sin Regerings ottende Aar, der han endnu var et ungt Menneske, begyndte han at søge sin Fader Davids Gud; og i det tolvte Aar begyndte han at rense Juda og Jerusalem fra Højene og Astartebillederne og de udskaarne og støbte Billeder.
4 A ƙarƙashin umarninsa aka rurrushe bagadan Ba’al, ya kuma tumɓuke bagadan ƙona turare waɗanda suke a bisansu, ya farfashe ginshiƙan Ashera da kuma sassaƙaƙƙun siffofi. Ya ragargaza waɗannan kucu-kucu, ya barbaɗa su a kan kaburburan waɗanda suka miƙa musu hadayu.
Og de nedbrøde for hans Ansigt Baalernes Altre, og han omhuggede de Solbilleder, som vare oven paa dem; han sønderbrød baade Astartebilleder og de udskaarne og støbte Billeder og stødte dem smaa og strøede dem oven paa deres Grave, som havde ofret til dem.
5 Ya ƙone ƙasusuwan firistocin gumaka a kan bagaden da a dā suke miƙa hadayunsu, ta haka ya tsabtacce Yahuda da Urushalima.
Og han opbrændte Præsternes Ben paa deres Altre og rensede Juda og Jerusalem.
6 Ya yi haka cikin garuruwan Manasse, Efraim da Simeyon, har zuwa Naftali, da kuma cikin kangwayen kewayensu,
Og udi Manasses og Efraims og Simeons Stæder, ja indtil Nafthali, i deres ødelagte Stæder trindt omkring,
7 ya farfashe bagadai da ginshiƙan Ashera; ya niƙa gumaka suka zama gari, ya kuma yayyanka dukan bagadan turare kucu-kucu ko’ina a Isra’ila. Sa’an nan ya koma Urushalima.
der nedbrød han Altrene og Astartebillederne og sønderknuste de udskaarne Billeder og stødte dem smaa og omhuggede alle Solbillederne i alt Israels Land og vendte tilbage til Jerusalem.
8 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya, ya tsarkake ƙasar da haikalin, ya aiki Shafan ɗan Azaliya da Ma’asehiya mai mulkin birni, tare da Yowa ɗan Yowahaz, marubuci, su gyara haikalin Ubangiji Allah.
Og i sin Regerings attende Aar, der han havde renset Landet og Huset, sendte han Safan, Azalias Søn, og Maeseja, Stadens Befalingsmand, og Joa, Joakas's Søn, Historieskriveren, for at istandsætte Herrens, sin Guds Hus.
9 Suka tafi wurin Hilkiya babban firist suka ba shi kuɗin da aka kawo cikin haikalin Allah, wanda Lawiyawa masu tsaron ƙofofi sun tattara daga mutanen Manasse, Efraim da dukan raguwar Isra’ila da kuma daga dukan mutanen Yahuda da Benyamin da kuma mazaunan Urushalima.
Og de kom til Hilkia, Ypperstepræsten, og overgave Pengene, som vare bragte til Guds Hus, hvilke Leviterne, som toge Vare paa Dørtærskelen, havde samlet af Manasses og Efraims Haand og af alle overblevne i Israel og af al Juda og Benjamin, og med hvilke de vendte tilbage til Jerusalem.
10 Sa’an nan suka danƙa su ga mutanen da aka naɗa su lura da aiki a kan haikalin Ubangiji. Waɗannan mutane ne suke biyan ma’aikatan da suka gyara suka kuma mai da haikalin.
Og de gave dem i deres Haand, som havde med Gerningen at gøre, og som vare beskikkede over Herrens Hus; og disse gave dem til dem, som gjorde Gerningen, og som arbejdede paa Herrens Hus for at udbedre og istandsætte Huset.
11 Suka kuma ba da kuɗi ga kafintoci da magina don su sayi sassaƙaƙƙun duwatsu, da katakai don yin tsaiko da tankar ginin da sarakunan Yahuda suka bari yă fāɗi ya zama kango.
Og de gave dem ud til Tømmermændene og Bygningsmændene og til at købe hugne Stene og Træ til Bjælkeværk og til at sammentømre Husene med, som Judas Konger havde ødelagt.
12 Mutanen fa suka yi aiki da aminci. Shugabanninsu, su ne Yahat da Obadiya, Lawiyawa zuriyar Merari da Zakariya da Meshullam, zuriyar Kohat. Dukan Lawiyawa waɗanda suke gwanaye a kayan kiɗi,
Og Mændene arbejdede trolig paa Gerningen, og over dem vare Jahath og Obadia, Leviterne af Meraris Børn, og Sakaria og Mesullam af Kahathiternes Børn, beskikkede til at have Opsyn, og alle de Leviter, som forstode sig paa Sangens Instrumenter.
13 sun lura da ma’aikata, suka kuma lura da dukan masu aiki daga aiki zuwa aiki. Waɗansu Lawiyawan su ne marubuta, magatakarda da kuma masu tsaron ƙofofi.
De vare og over Lastdragerne og havde Opsyn over hver den, som gjorde Gerningen ved ethvert enkelt Arbejde; men af Leviterne var der Skrivere og Fogeder og Portnere.
14 Yayinda suke fitar da kuɗin da aka kai cikin haikalin Ubangiji, sai Hilkiya firist ya sami Littafin Dokar Ubangiji da aka bayar ta wurin Musa.
Og der de udtoge Pengene, som vare indbragte i Herrens Hus, fandt Præsten Hilkia Herrens Lovbog, af Mose.
15 Hilkiya ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a cikin haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan.
Og Hilkia svarede og sagde til Safan, Kansleren: Jeg har fundet Lovbogen i Herrens Hus; og Hilkia gav Safan Bogen.
16 Sa’an nan Shafan ya ɗauki littafin zuwa wurin sarki, ya faɗa masa, “Manyan ma’aikatanka suna yin kome da aka sa su.
Og Safan bragte Bogen til Kongen, fremdeles gav han og Kongen Underretning, sigende: Alt det, som er givet i dine Tjeneres Hænder, det gøre de;
17 Mun ɗauke kuɗin da an ajiye a haikalin Ubangiji muka ba wa masu aiki da waɗanda suke lura da su.”
og de havde samlet Pengene, som fandtes i Herrens Hus, og givet dem i deres Haand, som ere beskikkede over Arbejdet, og i deres Haand, som gøre Gerningen.
18 Sa’an nan Shafan magatakarda ya sanar da sarki ya ce, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta daga cikinsa a gaban sarki.
Og Kansleren Safan gav Kongen til Kende og sagde: Hilkia, Præsten, gav mig en Bog; og Safan læste i den for Kongens Ansigt.
19 Da sarki ya ji kalmomin Doka, sai ya yage rigunansa.
Og det skete, der Kongen hørte Lovens Ord, da sønderrev han sine Klæder.
20 Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya, Ahikam ɗan Shafan, Abdon ɗan Mika, Shafan magatakarda da kuma Asahiya mai hidimar sarki.
Og Kongen bød Hilkia og Ahikam, Safans Søn, og Abdon, Mikas Søn, og Safan, Kansleren, og Asaja, Kongens Tjener, og sagde:
21 Ya ce, “Ku tafi ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da kuma saboda raguwa a Isra’ila da Yahuda game da abin da aka rubuta a wannan littafin da aka samu. Fushin Ubangiji mai girma ne da aka zuba a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye maganar Ubangiji ba; ba su aikata bisa ga dukan abin da yake a rubuce a wannan littafi ba.”
Gaar hen, adspørger Herren for mig og for de overblevne i Israel og i Juda om den Bogs Ord, som er funden; thi stor er Herrens Vrede, som er udøst over os, fordi vore Fædre ikke have holdt Herrens Ord, saa at de gjorde efter alt det, som er skrevet i denne Bog.
22 Hilkiya tare da waɗanda sarki ya aika, suka tafi suka yi magana da annabiya Hulda, wadda take matar Shallum ɗan Tokhat ɗan Hasra, mai tsaron wurin ajiyar riguna. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
Da gik Hilkia og Kongens Folk til den Profetinde Hulda, som var gift med Sallum, der var en Søn af Takhat, en Søn af Hasra, og som havde Tilsyn med Klæderne, og hun boede i Jerusalem i den anden Del; og de talte saadant med hende.
23 Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce faɗa wa mutumin da ya aike ku gare ni,
Og hun sagde til dem: Saa sagde Herren, Israels Gud: Siger til den Mand, som sendte eder til mig:
24 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce zai kawo masifa a wannan wuri da mutanensa, dukan la’anar da aka rubuta a cikin littafin da aka karanta a gaban sarkin Yahuda.
Saa sagde Herren: Se, jeg fører Ulykke over dette Sted og over dets Indbyggere, nemlig alle de Forbandelser, som ere skrevne i denne Bog, som de læste for Judas Konge;
25 Domin sun yashe ni suka kuma ƙone turare wa waɗansu alloli, suka tsokane ni in yi fushi ta wurin dukan abin da hannuwansu suka yi, fushina zai zuba a kan wannan wuri, ba kuma za a kwantar da shi ba.’
fordi de have forladt mig og gjort Røgoffer for andre Guder for at opirre mig med alle deres Hænders Gerninger, derfor skal min Vrede udøses over dette Sted og ikke udslukkes.
26 Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yake cewa game da kalmomin da ka ji.
Men til Judas Konge, som sendte eder for at adspørge Herren, til ham skulle I sige saaledes: Saa sagde Herren, Israels Gud, angaaende de Ord, som du har hørt:
27 Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Allah sa’ad da ka ji abin da ya yi magana a kan wannan wuri da mutanensa, domin kuma ka ƙasƙantar da kanka a gabana, ka yage rigunanka ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
Fordi dit Hjerte er blevet blødt, og du ydmygede dig for Guds Ansigt, der du hørte hans Ord imod dette Sted og imod dets Indbyggere, ja, ydmygede dig for mit Ansigt og sønderrev dine Klæder og græd for mit Ansigt: Saa har ogsaa jeg hørt det, siger Herren.
28 Yanzu zan tara ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka ba za su ga dukan masifar da zan kawo a kan wannan wuri da kuma a kan waɗanda suke zama a nan ba.’” Sai suka kai amsar wa sarki.
Se, jeg vil samle dig til dine Fædre, og du skal samles til din Grav i Fred, og dine Øjne skulle ikke se paa al den Ulykke, som jeg vil føre over dette Sted og over dets Indbyggere. Og de bragte Kongen Svar tilbage.
29 Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
Da sendte Kongen hen og lod alle de Ældste samles i Juda og Jerusalem.
30 Ya haura zuwa haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, mutanen Urushalima, firistoci da Lawiyawa, dukan mutane daga ƙarami zuwa babba. Ya karanta dukan kalmomin Littafin Alkawari wanda aka samu a cikin haikalin Ubangiji a kunnuwansu.
Og Kongen gik op i Herrens Hus og alle Judas Mænd og Indbyggerne i Jerusalem, Præsterne og Leviterne og alt Folket, baade store og smaa, og han læste for deres Øren alle Ordene i Pagtens Bog, som var funden i Herrens Hus.
31 Sai sarkin ya miƙe tsaye a inda yake, ya sabunta alkawari a gaban Ubangiji, don yă bi Ubangiji yă kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa da kuma farillansa da dukan zuciyarsa da kuma dukan ransa, ya kuma yi biyayya da kalmomin alkawarin da aka rubuta a cikin wannan littafi.
Og Kongen stod paa sit Sted og gjorde en Pagt for Herrens Ansigt, at han vilde vandre efter Herren og holde hans Bud og hans Vidnesbyrd og hans Skikke af sit ganske Hjerte og af sin ganske Sjæl for at opfylde Pagtens Ord, som vare skrevne i denne Bog.
32 Sa’an nan ya sa kowa a Urushalima da Benyamin ya yi alkawari ga wannan; mutanen Urushalima suka aikata wannan bisa ga alkawarin Allah, Allah na kakanninsu.
Og han lod alle dem, som bleve fundne i Jerusalem og i Benjamin, træde til, og Jerusalems Indbyggere gjorde efter Guds, deres Fædres Guds, Pagt.
33 Yosiya ya fitar da dukan gumakan banƙyama daga dukan yankunan Isra’ilawa, ya kuma sa dukan waɗanda suke a Isra’ila su bauta wa Ubangiji Allahnsu. Muddin ransa, ba su fasa bin Ubangiji Allah na kakanninsu ba.
Og Josias borttog alle Vederstyggeligheder af alle Lande, som hørte Israels Børn til, og han holdt dem alle, som fandtes i Israel, til at tjene Herren deres Gud; i alle hans Dage vege de ikke fra Herren, deres Fædres Gud.

< 2 Tarihi 34 >