< 2 Tarihi 34 >
1 Yosiya yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara talatin da ɗaya.
V osmi letech byl Joziáš, když kralovati počal, a kraloval jedno a třidceti let v Jeruzalémě.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji ya kuma yi tafiya a hanyoyin kakansa Dawuda, ba tare da juye dama ko hagu ba.
Ten činil to, což jest pravého před očima Hospodinovýma, chodě po cestách Davida otce svého, a neuchýlil se na pravo ani na levo.
3 A shekara ta takwas ta mulkinsa, yayinda yake matashi, sai ya fara neman Allah na kakansa Dawuda. A shekara ta goma sha biyunsa ya fara tsabtacce Yahuda da Urushalima daga masujadan kan tudu, ginshiƙan Ashera, sassaƙaƙƙun gumaka da kuma siffofin da aka yi zubi.
Léta zajisté osmého kralování svého, když ještě mládenček byl, počal hledati Boha Davida otce svého, dvanáctého pak léta počal vyčišťovati Judy a Jeruzaléma od výsostí, hájů, rytin a slitin.
4 A ƙarƙashin umarninsa aka rurrushe bagadan Ba’al, ya kuma tumɓuke bagadan ƙona turare waɗanda suke a bisansu, ya farfashe ginshiƙan Ashera da kuma sassaƙaƙƙun siffofi. Ya ragargaza waɗannan kucu-kucu, ya barbaɗa su a kan kaburburan waɗanda suka miƙa musu hadayu.
Nebo u přítomnosti jeho rozbořili oltáře Bálů, i obrazy slunečné, kteříž byli na nich, zpodtínal. Též i háje a rytiny, i slitiny zdrobil a setřel, a rozsypal po hrobích těch, kteříž jim obětovávali.
5 Ya ƙone ƙasusuwan firistocin gumaka a kan bagaden da a dā suke miƙa hadayunsu, ta haka ya tsabtacce Yahuda da Urushalima.
Kosti pak kněží popálil na oltářích jejich, a vyčistil Judu a Jeruzalém,
6 Ya yi haka cikin garuruwan Manasse, Efraim da Simeyon, har zuwa Naftali, da kuma cikin kangwayen kewayensu,
Též i města v pokolení Manasses, Efraim a Simeon, až i Neftalím i pustiny jejich vůkol.
7 ya farfashe bagadai da ginshiƙan Ashera; ya niƙa gumaka suka zama gari, ya kuma yayyanka dukan bagadan turare kucu-kucu ko’ina a Isra’ila. Sa’an nan ya koma Urushalima.
A tak zkazil oltáře a háje, a rytiny stroskotal na kusy, a všecky obrazy slunečné vysekal po vší zemi Izraelské. Potom navrátil se do Jeruzaléma.
8 A shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yosiya, ya tsarkake ƙasar da haikalin, ya aiki Shafan ɗan Azaliya da Ma’asehiya mai mulkin birni, tare da Yowa ɗan Yowahaz, marubuci, su gyara haikalin Ubangiji Allah.
Léta pak osmnáctého kralování svého, když vyčistil zemi a dům Boží, poslal Safana syna Azaliášova, a Maaseiáše úředníka města, aJoacha syna Joachazova kanclíře, aby opraven byl dům Hospodina Boha jeho.
9 Suka tafi wurin Hilkiya babban firist suka ba shi kuɗin da aka kawo cikin haikalin Allah, wanda Lawiyawa masu tsaron ƙofofi sun tattara daga mutanen Manasse, Efraim da dukan raguwar Isra’ila da kuma daga dukan mutanen Yahuda da Benyamin da kuma mazaunan Urushalima.
Kteříž přišedše k Helkiášovi knězi nejvyššímu, dali peníze snesené do domu Božího, kteréž byli Levítové vrátní vybrali od Manassesa a Efraima, i ode všech ostatků Izraelských, i od všeho Judy a Beniamina, a navrátili se do Jeruzaléma.
10 Sa’an nan suka danƙa su ga mutanen da aka naɗa su lura da aiki a kan haikalin Ubangiji. Waɗannan mutane ne suke biyan ma’aikatan da suka gyara suka kuma mai da haikalin.
Dali je pak v ruce správců toho díla, kteříž představeni byli nad domem Hospodinovým, a ti vydávali je dělníkům, jenž dělali v domě Hospodinově, opravujíce a utvrzujíce jej.
11 Suka kuma ba da kuɗi ga kafintoci da magina don su sayi sassaƙaƙƙun duwatsu, da katakai don yin tsaiko da tankar ginin da sarakunan Yahuda suka bari yă fāɗi ya zama kango.
I dali tesařům a stavitelům, aby najednali kamení tesaného, a dříví k vazbám i k trámům domů, kteréž byli zbořili králové Judští.
12 Mutanen fa suka yi aiki da aminci. Shugabanninsu, su ne Yahat da Obadiya, Lawiyawa zuriyar Merari da Zakariya da Meshullam, zuriyar Kohat. Dukan Lawiyawa waɗanda suke gwanaye a kayan kiɗi,
Muži pak ti věrně se měli při té práci, nad nimiž ustanoveni Jachat a Abdiáš Levítové z synů Merari, Zachariáš a Mesullam z synů Kahat, aby s pilností přídrželi k práci. A z těch Levítů každý uměl hráti na nástroje muzické.
13 sun lura da ma’aikata, suka kuma lura da dukan masu aiki daga aiki zuwa aiki. Waɗansu Lawiyawan su ne marubuta, magatakarda da kuma masu tsaron ƙofofi.
Ale nad nosiči, i kteříž přídrželi dělníky ke všeliké práci, byli z Levítů písaři, úředníci a vrátní.
14 Yayinda suke fitar da kuɗin da aka kai cikin haikalin Ubangiji, sai Hilkiya firist ya sami Littafin Dokar Ubangiji da aka bayar ta wurin Musa.
A když vynášeli peníze, kteréž byli sneseny do domu Hospodinova, našel Helkiáš kněz knihu zákona Hospodinova vydaného skrze Mojžíše.
15 Hilkiya ya ce wa Shafan magatakarda, “Na sami Littafin Doka a cikin haikalin Ubangiji.” Sai ya ba wa Shafan.
I řekl Helkiáš k Safanovi písaři: Knihu zákona nalezl jsem v domě Hospodinově. I dal Helkiáš tu knihu Safanovi.
16 Sa’an nan Shafan ya ɗauki littafin zuwa wurin sarki, ya faɗa masa, “Manyan ma’aikatanka suna yin kome da aka sa su.
Safan pak přinesl tu knihu králi, a při tom jemu oznámil, řka: Všecko, cožkoli bylo poručeno služebníkům tvým, dělají.
17 Mun ɗauke kuɗin da an ajiye a haikalin Ubangiji muka ba wa masu aiki da waɗanda suke lura da su.”
Nebo sebravše peníze, což se jich koli nalezlo v domě Hospodinově, vydali je v ruce úředníkům a dělníkům.
18 Sa’an nan Shafan magatakarda ya sanar da sarki ya ce, “Hilkiya firist ya ba ni wani littafi.” Sai Shafan ya karanta daga cikinsa a gaban sarki.
Oznámil také Safan písař králi, řka: Knihu mi dal Helkiáš kněz. I četl v ní Safan před králem.
19 Da sarki ya ji kalmomin Doka, sai ya yage rigunansa.
Pročež když slyšel král slova zákona, roztrhl roucho své.
20 Ya ba da waɗannan umarnai ga Hilkiya, Ahikam ɗan Shafan, Abdon ɗan Mika, Shafan magatakarda da kuma Asahiya mai hidimar sarki.
A rozkázal král Helkiášovi, též Achikamovi synu Safanovu, a Abdonovi synu Míchovu, a Safanovi písaři, a Asaiášovi služebníku královskému, řka:
21 Ya ce, “Ku tafi ku nemi nufin Ubangiji saboda ni da kuma saboda raguwa a Isra’ila da Yahuda game da abin da aka rubuta a wannan littafin da aka samu. Fushin Ubangiji mai girma ne da aka zuba a kanmu domin kakanninmu ba su kiyaye maganar Ubangiji ba; ba su aikata bisa ga dukan abin da yake a rubuce a wannan littafi ba.”
Jděte, poraďte se s Hospodinem o mne i o pozůstalý lid Izraelský a Judský, z strany slov knihy této, kteráž jest nalezena; nebo veliký jest hněv Hospodinův, kterýž jest vylit na nás, proto že neostříhali otcové naši slova Hospodinova, aby činili všecko, což psáno jest v knize této.
22 Hilkiya tare da waɗanda sarki ya aika, suka tafi suka yi magana da annabiya Hulda, wadda take matar Shallum ɗan Tokhat ɗan Hasra, mai tsaron wurin ajiyar riguna. Tana zama a Urushalima, a Yanki na Biyu.
Tedy šli, Helkiáš a kteříž byli při králi, k Chuldě prorokyni, manželce Salluma syna Tekue, syna Chasrova, strážného nad rouchem, nebo bydlila v Jeruzalémě na druhé straně, a mluvili k ní ty věci.
23 Sai ta ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce faɗa wa mutumin da ya aike ku gare ni,
Kteráž řekla jim: Toto praví Hospodin Bůh Izraelský: Povězte muži tomu, kterýž poslal vás ke mně,
24 ‘Ga abin da Ubangiji ya ce zai kawo masifa a wannan wuri da mutanensa, dukan la’anar da aka rubuta a cikin littafin da aka karanta a gaban sarkin Yahuda.
Takto praví Hospodin: Aj, já uvedu zlé věci na toto místo a na obyvatele jeho, všecka zlořečení napsaná v knize té, kterouž čtli před králem Judským,
25 Domin sun yashe ni suka kuma ƙone turare wa waɗansu alloli, suka tsokane ni in yi fushi ta wurin dukan abin da hannuwansu suka yi, fushina zai zuba a kan wannan wuri, ba kuma za a kwantar da shi ba.’
Proto že opustili mne a kadili bohům cizím, aby mne popouzeli všemi skutky rukou svých. Z té příčiny vylita bude prchlivost má na toto místo, aniž bude uhašena.
26 Ku faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aike ku ku nemi nufin Ubangiji, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yake cewa game da kalmomin da ka ji.
Králi pak Judskému, kterýž poslal vás, abyste se tázali Hospodina, takto povíte: Toto praví Hospodin Bůh Izraelský o slovích těch, kteráž jsi slyšel:
27 Domin zuciyarka mai tuba ce, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Allah sa’ad da ka ji abin da ya yi magana a kan wannan wuri da mutanensa, domin kuma ka ƙasƙantar da kanka a gabana, ka yage rigunanka ka kuma yi kuka a gabana, na ji ka, in ji Ubangiji.
Poněvadž obměkčeno jest srdce tvé, a ponížil jsi se před tváří Boží, kdyžs slyšel slova jeho proti místu tomuto a proti obyvatelům jeho, a ponižuje se přede mnou, roztrhl jsi roucho své, a plakals přede mnou, i já vyslyšel jsem tě, praví Hospodin.
28 Yanzu zan tara ka da kakanninka, za a kuma binne ka cikin salama. Idanunka ba za su ga dukan masifar da zan kawo a kan wannan wuri da kuma a kan waɗanda suke zama a nan ba.’” Sai suka kai amsar wa sarki.
Aj, já připojím tě k otcům tvým, a pochován budeš v hrobích svých v pokoji, aby neviděly oči tvé ničeho z toho zlého, kteréž já uvedu na místo toto a na obyvatele jeho. I oznámili králi tu řeč.
29 Sai sarki ya kira dukan dattawan Yahuda da Urushalima.
Tedy poslav král, shromáždil všecky starší Judské a Jeruzalémské.
30 Ya haura zuwa haikalin Ubangiji tare da mutanen Yahuda, mutanen Urushalima, firistoci da Lawiyawa, dukan mutane daga ƙarami zuwa babba. Ya karanta dukan kalmomin Littafin Alkawari wanda aka samu a cikin haikalin Ubangiji a kunnuwansu.
A vstoupil král do domu Hospodinova, a všickni muži Judští i obyvatelé Jeruzalémští, kněží, Levítové a všecken lid od velikého až do malého, i četl, aby všickni slyšeli všecka slova knihy smlouvy, kteráž byla nalezena v domě Hospodinově.
31 Sai sarkin ya miƙe tsaye a inda yake, ya sabunta alkawari a gaban Ubangiji, don yă bi Ubangiji yă kiyaye umarnansa, ƙa’idodinsa da kuma farillansa da dukan zuciyarsa da kuma dukan ransa, ya kuma yi biyayya da kalmomin alkawarin da aka rubuta a cikin wannan littafi.
Potom stoje král na místě svém, učinil smlouvu před Hospodinem, že bude následovati Hospodina, a ostříhati přikázaní jeho i svědectví jeho a ustanovení jeho z celého srdce svého a ze vší duše své, a plniti slova smlouvy té, kteráž jsou v té knize zapsána.
32 Sa’an nan ya sa kowa a Urushalima da Benyamin ya yi alkawari ga wannan; mutanen Urushalima suka aikata wannan bisa ga alkawarin Allah, Allah na kakanninsu.
I rozkázal, aby k témuž každý stál, kdož by koli nalezen byl v Jeruzalémě a v Beniaminovi. I činili obyvatelé Jeruzalémští podlé smlouvy Boží, Boha otců svých.
33 Yosiya ya fitar da dukan gumakan banƙyama daga dukan yankunan Isra’ilawa, ya kuma sa dukan waɗanda suke a Isra’ila su bauta wa Ubangiji Allahnsu. Muddin ransa, ba su fasa bin Ubangiji Allah na kakanninsu ba.
Tehdáž také vyprázdnil Joziáš všecky ohavnosti ze všech zemí synů Izraelských, a přídržel všecky, kteřížkoli byli v Izraeli, k tomu, aby sloužili Hospodinu Bohu svému. Po všecky dny jeho neodstoupili od následování Hospodina Boha otců svých.