< 2 Tarihi 33 >
1 Manasse yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyar.
Дванадесяти лет бе Манассиа, егда царствовати нача, и пятьдесят пять лет царствова во Иерусалиме:
2 Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji, yana bin ayyukan banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
сотвори же лукавое пред Господем по всем мерзостем языческим, ихже истреби Господь от лица сынов Израилевых:
3 Ya sāke gina masujadan kan tudun da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe; ya tā da bagadan Ba’al, ya kuma gina ginshiƙan Ashera. Ya rusuna wa dukan rundunonin taurari, ya kuma yi musu sujada.
и возврати и созда высокая, яже раскопа Езекиа отец его, и сострои кумиры Ваалиму, и сотвори дубравы, и поклонися всему воинству небесному, и послужи им,
4 Ya gina bagadai cikin haikalin Ubangiji, waɗanda Ubangiji ya ce, “Sunana zai kasance cikin Urushalima har abada.”
и созда олтари в дому Господни, о немже глагола Господь: во Иерусалиме будет имя Мое во веки:
5 Cikin filayen haikalin Ubangiji, ya gina bagadai ga dukan rundunonin taurari.
созда же жертвенники всему воинству небесному во двою дворех дому Господня.
6 Ya miƙa’ya’yansa maza hadaya a wuta cikin Kwarin Ben Hinnom, ya yi bokanci, ya yi duba, ya kuma yi maitanci, ya nemi shawarar mabiya da masu ruhohi. Ya yi abin da yake mugu ƙwarai a gaban Ubangiji, yana tsokanarsa yă yi fushi.
Той же проведе чада своя чрез огнь во удоли Веенномли и вражаше (со жребии), и последоваше гаданием, и волхвованием служаше, и имеяше чревоволшебники и обаянники, и многа лукавая сотвори пред Господем, да прогневает Его:
7 Ya ɗauki siffar da aka sassaƙa wadda ya yi, ya sa ta a cikin haikalin Allah, wanda Allah ya ce wa Dawuda da kuma ɗansa Solomon, “Cikin wannan haikali da kuma cikin Urushalima, wanda na zaɓa daga cikin kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
истуканы же и слиянны образы сотвори и постави в дому Божии, о немже глагола Бог к Давиду и к Соломону сыну его: в дому сем и во Иерусалиме, егоже избрах от всех колен Израилевых, положу имя Мое во век,
8 Ba zan ƙara bari ƙafafun Isra’ilawa su bar ƙasar da na ba wa kakanninku ba, in dai suka yi hankali ga yin kome da na umarce su game da duka dokoki, ƙa’idodi da kuma farillai da na bayar ta wurin Musa.”
и не приложу подвигнути ногу Израилеву от земли, юже предах отцем их, токмо аще сохранят сотворити вся, яже повелех им, по всему закону и повелением и судбам, рукою Моисеовою.
9 Amma Manasse ya sa Yahuda da mutanen Urushalima suka kauce, har suka aikata mugunta fiye da al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
И прельсти Манассиа Иуду и живущих во Иерусалиме, да сотворят лукавое паче всех язык, ихже испроверже Господь от лица сынов Израилевых.
10 Ubangiji ya yi magana da Manasse da mutanensa, amma ba su kula ba.
И глагола Господь к Манассии и к людем его, и не послушаша.
11 Saboda haka Ubangiji ya kawo manyan hafsoshin mayaƙan sarkin Assuriya a kansu, waɗanda suka ɗauki Manasse a matsayi ɗan kurkuku, suka sa ƙugiya a hancinsa, suka daure shi da sarƙoƙin tagulla suka kuma kai shi Babilon.
И наведе Господь на них началники воев царя Ассирийска, и яша Манассию во узах, и связаша его оковы ножными, и отведоша в Вавилон.
12 Cikin wahalarsa ya nemi tagomashin Ubangiji Allahnsa ya kuma ƙasƙantar da kansa sosai a gaban Allah na kakanninsa.
И егда озлоблен бысть, взыска лице Господа Бога своего, и смирися зело пред лицем Бога отец своих,
13 Da ya yi addu’a gare shi, sai Ubangiji ya taɓu da tubansa, ya kuma saurari roƙonsa; saboda haka ya dawo da shi Urushalima da kuma zuwa mulkinsa. Sa’an nan Manasse ya san cewa Ubangiji shi ne Allah.
и помолися к Нему и послуша его, и услыша вопль его, и возврати его во Иерусалим на царство его: и позна Манассиа, яко Господь Той есть Бог.
14 Daga baya ya sāke gina katangar waje na Birnin Dawuda, yamma da maɓulɓular Gihon a cikin kwari, har zuwa mashigin Ƙofar Kifi, ya kuma kewaye tudun Ofel; ya yi ta da tsayi sosai. Ya sa hafsoshin mayaƙa cikin dukan biranen katanga a Yahuda.
И по сих созда стену вне града Давидова от Ливы к югу в потоце и ко входу врат Рыбных, исходящым вратами сущими окрест в высоту, и возвыси зело: и постави началники воем во всех градех Иудиных стенатых,
15 Ya fid da baƙin alloli, ya kuma fid da siffofi daga haikalin Ubangiji, haka ma dukan bagadan da ya gina a kan tudun haikali da kuma cikin Urushalima, ya zubar da su a bayan birni.
и отят боги чуждыя и идолы от дому Господня, и вся олтари, яже созда в горе дому Господня и во Иерусалиме, и изверже вся вон из града.
16 Sa’an nan ya gyara bagaden Ubangiji ya kuma miƙa hadayun salama da kuma hadayun godiya a bagaden, ya kuma faɗa wa Yahuda su bauta wa Ubangiji, Allah na Isra’ila.
И паки воздвиже олтарь Господень, и пожре на том жертву спасения и хваления, и заповеда Иуде, да служат Господу Богу Израилеву.
17 Mutane dai suka ci gaba da miƙa hadayu a masujadai kan tudu, amma wa Ubangiji Allahnsu kaɗai.
Но еще людие жряху на высоких, обаче Господу Богу своему.
18 Sauran ayyukan mulkin Manasse, haɗe da addu’arsa ga Allahnsa da kuma kalmomin da mai duba ya yi masa cikin sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, suna a rubuce cikin tarihin sarakunan Isra’ila.
Прочая же словес Манассииных, и молитва его, яже к Богу, и словеса провидящих, иже глаголаху к нему во имя Господа Бога Израилева,
19 Addu’arsa da yadda Allah ya taɓu ta wurin tubansa, da kuma dukan zunubansa da rashin biyayyarsa, da wuraren da ya gina masujadan kan tudu ya kuma kafa ginshiƙan Ashera da gumaka kafin ya ƙasƙantar da kansa, duka suna a rubuce cikin tarihin mai duba.
се, во словесех молитвы его, и яко услыша его, и вси греси его и отступления его, и места, на нихже созида высокая, и сотвори тамо Дубравы и изваянная, прежде неже обратитися ему, се, писана суть во словесех провидящих.
20 Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a fadansa. Sai Amon ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Успе же Манассиа со отцы своими, и погребоша его в саду дому его. И воцарися вместо его сын его Амон.
21 Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki a Urushalima shekara biyu.
Двадесяти дву лет бе Амон, егда царствовати нача, и два лета царствова во Иерусалиме,
22 Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda mahaifinsa Manasse ya yi. Amon ya bauta ya kuma miƙa hadayu ga dukan gumakan da Manasse ya yi.
и сотвори лукавое пред Господем, якоже творяше Манассиа отец его, и всем идолом, ихже сотвори Манассиа отец его, пожре Амон и послужи им:
23 Amma ba kamar mahaifinsa Manasse ba, bai ƙasƙantar da kansa a gaban Ubangiji ba; Amon ya ƙara laifinsa.
и не смирися пред Господем, якоже смирися Манассиа отец его, зане сын его Амон умножи грехи.
24 Fadawan Amon sukan yi masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a fadansa.
И нападоша нань раби его и убиша его в дому его.
25 Sa’an nan mutanen ƙasar suka kashe dukan waɗanda suka yi wa Sarki Amon maƙarƙashiya, suka naɗa Yosiya ɗansa sarki a maimakonsa.
И убиша людие земли нападших на царя Амона, и поставиша людие земли царя Иосию сына его вместо его.