< 2 Tarihi 33 >

1 Manasse yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyar.
Manassé était âgé de douze ans quand il commença à régner, et il régna cinquante-cinq ans à Jérusalem.
2 Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji, yana bin ayyukan banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
Et il fit ce qui déplaît à l'Eternel, selon les abominations des nations que l'Eternel avait chassées de devant les enfants d'Israël.
3 Ya sāke gina masujadan kan tudun da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe; ya tā da bagadan Ba’al, ya kuma gina ginshiƙan Ashera. Ya rusuna wa dukan rundunonin taurari, ya kuma yi musu sujada.
Car il rebâtit les hauts lieux qu'Ezéchias son père avait démolis, et redressa les autels des Bahalins, et fit des bocages, et se prosterna devant toute l'armée des cieux, et les servit.
4 Ya gina bagadai cikin haikalin Ubangiji, waɗanda Ubangiji ya ce, “Sunana zai kasance cikin Urushalima har abada.”
Il bâtit aussi des autels dans la maison de l'Eternel, de laquelle l'Eternel avait dit: Mon Nom sera dans Jérusalem à jamais.
5 Cikin filayen haikalin Ubangiji, ya gina bagadai ga dukan rundunonin taurari.
Il bâtit, [dis-je], des autels à toute l'armée des cieux dans les deux parvis de la maison de l'Eternel.
6 Ya miƙa’ya’yansa maza hadaya a wuta cikin Kwarin Ben Hinnom, ya yi bokanci, ya yi duba, ya kuma yi maitanci, ya nemi shawarar mabiya da masu ruhohi. Ya yi abin da yake mugu ƙwarai a gaban Ubangiji, yana tsokanarsa yă yi fushi.
Il fit passer ses fils par le feu dans la vallée du fils de Hinnon, et il prédisait le temps, et usait de prédictions et de sortilèges; et il dressa un [oracle d']esprit de Python, et eut des diseurs de bonne aventure; [en un mot], il s'adonna extrêmement à faire ce qui déplaît à l'Eternel pour l'irriter.
7 Ya ɗauki siffar da aka sassaƙa wadda ya yi, ya sa ta a cikin haikalin Allah, wanda Allah ya ce wa Dawuda da kuma ɗansa Solomon, “Cikin wannan haikali da kuma cikin Urushalima, wanda na zaɓa daga cikin kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
Il posa aussi une image taillée qu'il avait faite pour une représentation en la maison de Dieu, de laquelle Dieu avait dit à David et à Salomon son fils: Je mettrai à perpétuité mon Nom dans cette maison, et dans Jérusalem, que j'ai choisie d'entre toutes les Tribus d'Israël.
8 Ba zan ƙara bari ƙafafun Isra’ilawa su bar ƙasar da na ba wa kakanninku ba, in dai suka yi hankali ga yin kome da na umarce su game da duka dokoki, ƙa’idodi da kuma farillai da na bayar ta wurin Musa.”
Et je ne ferai plus sortir Israël de la terre que j'ai assignée à leurs pères, pourvu seulement qu'ils prennent garde à faire tout ce que je leur ai commandé par le moyen de Moïse, [c'est-à-dire] toute la Loi, et les statuts, et les ordonnances.
9 Amma Manasse ya sa Yahuda da mutanen Urushalima suka kauce, har suka aikata mugunta fiye da al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
Manassé donc fit égarer Juda et les habitants de Jérusalem, jusqu'à faire pis que les nations que l'Eternel avait exterminées de devant les enfants d'Israël.
10 Ubangiji ya yi magana da Manasse da mutanensa, amma ba su kula ba.
Et l'Eternel parla à Manassé, et à son peuple; mais ils n'y voulurent point entendre.
11 Saboda haka Ubangiji ya kawo manyan hafsoshin mayaƙan sarkin Assuriya a kansu, waɗanda suka ɗauki Manasse a matsayi ɗan kurkuku, suka sa ƙugiya a hancinsa, suka daure shi da sarƙoƙin tagulla suka kuma kai shi Babilon.
C'est pourquoi l'Eternel fit venir contr'eux les capitaines de l'armée du Roi des Assyriens, qui prirent Manassé dans des halliers, et le lièrent de doubles chaînes d'airain, et l'emmenèrent à Babylone.
12 Cikin wahalarsa ya nemi tagomashin Ubangiji Allahnsa ya kuma ƙasƙantar da kansa sosai a gaban Allah na kakanninsa.
Et dès qu'il fut en angoisse, il supplia l'Eternel son Dieu, et s'humilia fort devant le Dieu de ses pères.
13 Da ya yi addu’a gare shi, sai Ubangiji ya taɓu da tubansa, ya kuma saurari roƙonsa; saboda haka ya dawo da shi Urushalima da kuma zuwa mulkinsa. Sa’an nan Manasse ya san cewa Ubangiji shi ne Allah.
Il lui adressa donc ses supplications, et [Dieu] fléchi par ses prières, exauça sa supplication, et le fit retourner à Jérusalem dans son Royaume; et Manassé reconnut que l'Eternel est celui qui est Dieu.
14 Daga baya ya sāke gina katangar waje na Birnin Dawuda, yamma da maɓulɓular Gihon a cikin kwari, har zuwa mashigin Ƙofar Kifi, ya kuma kewaye tudun Ofel; ya yi ta da tsayi sosai. Ya sa hafsoshin mayaƙa cikin dukan biranen katanga a Yahuda.
Après cela il bâtit la muraille de dehors pour la Cité de David vers l'Occident de Guihon, dans la vallée, et jusqu'à l'entrée de la porte des poissons, et il environna Hophel, et l'éleva beaucoup; puis il établit des capitaines de l'armée dans toutes les villes fortes de Juda.
15 Ya fid da baƙin alloli, ya kuma fid da siffofi daga haikalin Ubangiji, haka ma dukan bagadan da ya gina a kan tudun haikali da kuma cikin Urushalima, ya zubar da su a bayan birni.
Et il ôta de la maison de l'Eternel l'idole, et les dieux des étrangers, et tous les autels qu'il avait bâtis sur la montagne de la maison de l'Eternel, et à Jérusalem, et les jeta hors de la ville.
16 Sa’an nan ya gyara bagaden Ubangiji ya kuma miƙa hadayun salama da kuma hadayun godiya a bagaden, ya kuma faɗa wa Yahuda su bauta wa Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Puis il rebâtit l'autel de l'Eternel, et y sacrifia des sacrifices de prospérités, et de louange, et il commanda à Juda de servir l'Eternel le Dieu d'Israël.
17 Mutane dai suka ci gaba da miƙa hadayu a masujadai kan tudu, amma wa Ubangiji Allahnsu kaɗai.
Toutefois le peuple sacrifiait encore dans les hauts lieux, mais c'était seulement à l'Eternel leur Dieu.
18 Sauran ayyukan mulkin Manasse, haɗe da addu’arsa ga Allahnsa da kuma kalmomin da mai duba ya yi masa cikin sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, suna a rubuce cikin tarihin sarakunan Isra’ila.
Le reste des faits de Manassé, et la prière qu'il fit à son Dieu, et les paroles des Voyants qui lui parlaient au Nom de l'Eternel le Dieu d'Israël, voilà, toutes ces choses sont [écrites] parmi les actions des Rois d'Israël.
19 Addu’arsa da yadda Allah ya taɓu ta wurin tubansa, da kuma dukan zunubansa da rashin biyayyarsa, da wuraren da ya gina masujadan kan tudu ya kuma kafa ginshiƙan Ashera da gumaka kafin ya ƙasƙantar da kansa, duka suna a rubuce cikin tarihin mai duba.
Et sa prière, et comment [Dieu] fut fléchi par ses prières, tout son péché, et son crime, et les places dans lesquelles il bâtit des hauts lieux, et dressa des bocages, et des images taillées, avant qu'il se fût humilié, voilà, toutes ces choses sont écrites dans les paroles des Voyants.
20 Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a fadansa. Sai Amon ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Puis Manassé s'endormit avec ses pères, et on l'ensevelit dans sa maison; et Amon son fils régna en sa place.
21 Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki a Urushalima shekara biyu.
Amon [était] âgé de vingt-deux ans quand il commença à régner, et il régna deux ans à Jérusalem.
22 Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda mahaifinsa Manasse ya yi. Amon ya bauta ya kuma miƙa hadayu ga dukan gumakan da Manasse ya yi.
Et il fit ce qui déplaît à l'Eternel, comme avait fait Manassé son père; car Amon sacrifia à toutes les images taillées que Manassé son père avait faites, et les servit.
23 Amma ba kamar mahaifinsa Manasse ba, bai ƙasƙantar da kansa a gaban Ubangiji ba; Amon ya ƙara laifinsa.
Mais il ne s'humilia point devant l'Eternel, comme s'était humilié Manassé son père, mais se rendit coupable de plus en plus.
24 Fadawan Amon sukan yi masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a fadansa.
Et ses serviteurs ayant fait une conspiration contre lui, le firent mourir dans sa maison.
25 Sa’an nan mutanen ƙasar suka kashe dukan waɗanda suka yi wa Sarki Amon maƙarƙashiya, suka naɗa Yosiya ɗansa sarki a maimakonsa.
Mais le peuple du pays frappa tous ceux qui avaient conspiré contre le Roi Amon; et le peuple du pays établit pour Roi en sa place Josias son fils.

< 2 Tarihi 33 >