< 2 Tarihi 33 >

1 Manasse yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyar.
Ve dvanácti letech byl Manasses, když počal kralovati, a padesáte pět let kraloval v Jeruzalémě.
2 Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji, yana bin ayyukan banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
Èinil pak to, což jest zlého před očima Hospodinovýma, vedlé ohavností těch národů, kteréž Hospodin vyhnal před syny Izraelskými.
3 Ya sāke gina masujadan kan tudun da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe; ya tā da bagadan Ba’al, ya kuma gina ginshiƙan Ashera. Ya rusuna wa dukan rundunonin taurari, ya kuma yi musu sujada.
Nebo vzdělal zase výsosti, kteréž byl rozbořil Ezechiáš otec jeho, a vystavěl oltáře Bálům, a vysadil háje, a klaněje se všemu vojsku nebeskému, sloužil jim.
4 Ya gina bagadai cikin haikalin Ubangiji, waɗanda Ubangiji ya ce, “Sunana zai kasance cikin Urushalima har abada.”
Vzdělal také oltáře v domě Hospodinově, o němž byl řekl Hospodin: V Jeruzalémě bude jméno mé na věky.
5 Cikin filayen haikalin Ubangiji, ya gina bagadai ga dukan rundunonin taurari.
Vzdělal, pravím, oltáře všemu vojsku nebeskému ve dvou síních domu Hospodinova.
6 Ya miƙa’ya’yansa maza hadaya a wuta cikin Kwarin Ben Hinnom, ya yi bokanci, ya yi duba, ya kuma yi maitanci, ya nemi shawarar mabiya da masu ruhohi. Ya yi abin da yake mugu ƙwarai a gaban Ubangiji, yana tsokanarsa yă yi fushi.
Přesto dal provoditi syny své skrze oheň v údolí Benhinnom, a šetřil času, s hadačstvím a s kouzly se obíral, a nařídil zaklinače a čarodějníky, a mnoho zlého páchal před očima Hospodinovýma, popouzeje ho.
7 Ya ɗauki siffar da aka sassaƙa wadda ya yi, ya sa ta a cikin haikalin Allah, wanda Allah ya ce wa Dawuda da kuma ɗansa Solomon, “Cikin wannan haikali da kuma cikin Urushalima, wanda na zaɓa daga cikin kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
Postavil také obraz rytý, kterýž byl udělal, v domě Božím, o kterémž byl řekl Bůh Davidovi a Šalomounovi synu jeho: V domě tomto a v Jeruzalémě, kterýž jsem vyvolil ze všech pokolení Izraelských, oslavím jméno své na věky.
8 Ba zan ƙara bari ƙafafun Isra’ilawa su bar ƙasar da na ba wa kakanninku ba, in dai suka yi hankali ga yin kome da na umarce su game da duka dokoki, ƙa’idodi da kuma farillai da na bayar ta wurin Musa.”
Aniž více pohnu nohou lidu Izraelského z země, kterouž jsem oddělil otcům vašim, jen toliko budou-li šetřiti, aby plnili všecko to, což jsem jim přikázal, všecken zákon, ustanovení a soudy skrze Mojžíše vydané.
9 Amma Manasse ya sa Yahuda da mutanen Urushalima suka kauce, har suka aikata mugunta fiye da al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
Ale Manasses uvedl v blud Judské i obyvatele Jeruzalémské, tak že činili horší věci nežli ti národové, kteréž vyplénil Hospodin před tváří synů Izraelských.
10 Ubangiji ya yi magana da Manasse da mutanensa, amma ba su kula ba.
A ačkoli mluvil Hospodin k Manassesovi a k lidu jeho, oni však nepozorovali.
11 Saboda haka Ubangiji ya kawo manyan hafsoshin mayaƙan sarkin Assuriya a kansu, waɗanda suka ɗauki Manasse a matsayi ɗan kurkuku, suka sa ƙugiya a hancinsa, suka daure shi da sarƙoƙin tagulla suka kuma kai shi Babilon.
Pročež přivedl na ně Hospodin hejtmany vojska krále Assyrského, kteříž jali Manassesa v trní, a svázavše ho dvěma řetězy ocelivými, dovedli jej do Babylona.
12 Cikin wahalarsa ya nemi tagomashin Ubangiji Allahnsa ya kuma ƙasƙantar da kansa sosai a gaban Allah na kakanninsa.
Tam pak jsa sevřín, modlil se Hospodinu Bohu svému, a ponižoval se velmi před oblíčejem Boha otců svých,
13 Da ya yi addu’a gare shi, sai Ubangiji ya taɓu da tubansa, ya kuma saurari roƙonsa; saboda haka ya dawo da shi Urushalima da kuma zuwa mulkinsa. Sa’an nan Manasse ya san cewa Ubangiji shi ne Allah.
A modlil se jemu. I naklonil se k němu, a vyslyšel modlitbu jeho, a uvedl jej zase do Jeruzaléma do království jeho. Tehdy poznal Manasses, že sám Hospodin jest Bohem.
14 Daga baya ya sāke gina katangar waje na Birnin Dawuda, yamma da maɓulɓular Gihon a cikin kwari, har zuwa mashigin Ƙofar Kifi, ya kuma kewaye tudun Ofel; ya yi ta da tsayi sosai. Ya sa hafsoshin mayaƙa cikin dukan biranen katanga a Yahuda.
A potom vystavěl zed zevnitřní města Davidova k západní straně Gihonu potoku, až kudy se chodí k bráně rybné, a obehnal Ofel, a vyhnal ji velmi vysoko. Rozsadil také hejtmany vojska po všech městech hrazených v Judstvu.
15 Ya fid da baƙin alloli, ya kuma fid da siffofi daga haikalin Ubangiji, haka ma dukan bagadan da ya gina a kan tudun haikali da kuma cikin Urushalima, ya zubar da su a bayan birni.
Vymetal také bohy cizí a rytinu z domu Hospodinova, a všecky oltáře, kterýchž byl nadělal na hoře domu Hospodinova i v Jeruzalémě, a vyházel za město.
16 Sa’an nan ya gyara bagaden Ubangiji ya kuma miƙa hadayun salama da kuma hadayun godiya a bagaden, ya kuma faɗa wa Yahuda su bauta wa Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Opravil zase i oltář Hospodinův, a obětoval na něm oběti pokojné a díkčinění, a přikázal Judským, aby sloužili Hospodinu Bohu Izraelskému.
17 Mutane dai suka ci gaba da miƙa hadayu a masujadai kan tudu, amma wa Ubangiji Allahnsu kaɗai.
A však vždy ještě lid obětoval na výsostech, ale toliko Hospodinu Bohu svému.
18 Sauran ayyukan mulkin Manasse, haɗe da addu’arsa ga Allahnsa da kuma kalmomin da mai duba ya yi masa cikin sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, suna a rubuce cikin tarihin sarakunan Isra’ila.
Jiné pak věci Manassesovy, i modlitba jeho k Bohu jeho, a slova proroků, kteříž mluvívali k němu ve jménu Hospodina Boha Izraelského, to vše zapsáno v knize o králích Izraelských.
19 Addu’arsa da yadda Allah ya taɓu ta wurin tubansa, da kuma dukan zunubansa da rashin biyayyarsa, da wuraren da ya gina masujadan kan tudu ya kuma kafa ginshiƙan Ashera da gumaka kafin ya ƙasƙantar da kansa, duka suna a rubuce cikin tarihin mai duba.
Modlitba pak jeho i to, že vyslyšán jest, a každý hřích jeho, i přestoupení jeho, i místa, na kterýchž byl postavil výsosti, a zdělal háje a rytiny, ještě prvé než se pokořil, to vše zapsáno jest v knihách Chozai.
20 Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a fadansa. Sai Amon ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
I usnul Manasses s otci svými, a pochovali jej v domě jeho, a kraloval Amon syn jeho místo něho.
21 Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki a Urushalima shekara biyu.
Ve dvamecítma letech byl Amon, když počal kralovati, a dvě létě kraloval v Jeruzalémě.
22 Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda mahaifinsa Manasse ya yi. Amon ya bauta ya kuma miƙa hadayu ga dukan gumakan da Manasse ya yi.
I činil to, což jest zlého před očima Hospodinovýma, tak jako byl činil Manasses otec jeho; nebo všechněm rytinám, kterýchž byl nadělal Manasses otec jeho, obětoval Amon a sloužil jim.
23 Amma ba kamar mahaifinsa Manasse ba, bai ƙasƙantar da kansa a gaban Ubangiji ba; Amon ya ƙara laifinsa.
Aniž se ponížil před Hospodinem, jako se ponížil Manasses otec jeho, nýbrž on Amon mnohem více hřešil.
24 Fadawan Amon sukan yi masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a fadansa.
Spuntovali se pak proti němu služebníci jeho, a zamordovali jej v domě jeho.
25 Sa’an nan mutanen ƙasar suka kashe dukan waɗanda suka yi wa Sarki Amon maƙarƙashiya, suka naɗa Yosiya ɗansa sarki a maimakonsa.
Tedy pobil lid země všecky ty, kteříž se byli spuntovali proti králi Amonovi, a ustanovil lid země krále Joziáše syna jeho místo něho.

< 2 Tarihi 33 >