< 2 Tarihi 33 >

1 Manasse yana da shekara ashirin sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara hamsin da biyar.
Manašeu je bilo dvanaest godina kad se zakraljio. Pedeset i pet godina kraljevao je u Jeruzalemu.
2 Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji, yana bin ayyukan banƙyama na al’umman da Ubangiji ya kora a gaban Isra’ilawa.
Činio je što je zlo u Jahvinim očima, povodeći se za gnusobama naroda što ih je Jahve protjerao pred sinovima Izraelovim.
3 Ya sāke gina masujadan kan tudun da mahaifinsa Hezekiya ya rurrushe; ya tā da bagadan Ba’al, ya kuma gina ginshiƙan Ashera. Ya rusuna wa dukan rundunonin taurari, ya kuma yi musu sujada.
Obnovio je uzvišice što ih bijaše oborio otac mu Ezekija, podigao je žrtvenike Baalu, načinio ašere i stao se klanjati svoj nebeskoj vojsci i služiti joj.
4 Ya gina bagadai cikin haikalin Ubangiji, waɗanda Ubangiji ya ce, “Sunana zai kasance cikin Urushalima har abada.”
Podigao je žrtvenike i u Domu Jahvinu, za koji bijaše rekao Jahve: “U Jeruzalemu će prebivati Ime moje zauvijek.”
5 Cikin filayen haikalin Ubangiji, ya gina bagadai ga dukan rundunonin taurari.
Sagradio je žrtvenike svoj nebeskoj vojsci u oba predvorja Doma Jahvina.
6 Ya miƙa’ya’yansa maza hadaya a wuta cikin Kwarin Ben Hinnom, ya yi bokanci, ya yi duba, ya kuma yi maitanci, ya nemi shawarar mabiya da masu ruhohi. Ya yi abin da yake mugu ƙwarai a gaban Ubangiji, yana tsokanarsa yă yi fushi.
I sinove je svoje proveo kroz oganj u dolini Hinomova sina. Vračao je, gatao, čarao, stvorio bajače i opsjenare i uopće učinio premnogo zla u Jahvinim očima razjarujući ga.
7 Ya ɗauki siffar da aka sassaƙa wadda ya yi, ya sa ta a cikin haikalin Allah, wanda Allah ya ce wa Dawuda da kuma ɗansa Solomon, “Cikin wannan haikali da kuma cikin Urushalima, wanda na zaɓa daga cikin kabilan Isra’ila, zan sa Sunana har abada.
Načinio je idolski lik i posadio ga u Domu Božjem, za koji Bog bijaše rekao Davidu i njegovu sinu Salomonu: “U ovom Domu i u Jeruzalemu, koji sam izabrao među svim izraelskim plemenima, postavit ću Ime svoje zauvijek.
8 Ba zan ƙara bari ƙafafun Isra’ilawa su bar ƙasar da na ba wa kakanninku ba, in dai suka yi hankali ga yin kome da na umarce su game da duka dokoki, ƙa’idodi da kuma farillai da na bayar ta wurin Musa.”
Neću više dati da noga Izraelaca uzmakne iz zemlje koju sam dao u baštinu vašim očevima, samo ako budu držali i provodili u djelo sve što sam im zapovjedio: sav Zakon, uredbe i običaje dane preko Mojsija.”
9 Amma Manasse ya sa Yahuda da mutanen Urushalima suka kauce, har suka aikata mugunta fiye da al’umman da Ubangiji ya hallaka a gaban Isra’ilawa.
Ali je Manaše zaveo Judejce i Jeruzalemce te su radili još gore nego narodi što ih je Jahve iskorijenio pred sinovima Izraelovim.
10 Ubangiji ya yi magana da Manasse da mutanensa, amma ba su kula ba.
Jahve je opominjao Manašea i njegov narod, ali oni nisu poslušali.
11 Saboda haka Ubangiji ya kawo manyan hafsoshin mayaƙan sarkin Assuriya a kansu, waɗanda suka ɗauki Manasse a matsayi ɗan kurkuku, suka sa ƙugiya a hancinsa, suka daure shi da sarƙoƙin tagulla suka kuma kai shi Babilon.
Stoga je Jahve doveo na njih vojskovođe asirskoga kralja. Uhvativši Manašea kukama, svezali su ga u dvoje mjedene verige i odveli u Babilon.
12 Cikin wahalarsa ya nemi tagomashin Ubangiji Allahnsa ya kuma ƙasƙantar da kansa sosai a gaban Allah na kakanninsa.
Kad se našao u nevolji, počeo se moliti za milost Jahvi, svome Bogu, ponizivši se veoma pred Bogom otaca.
13 Da ya yi addu’a gare shi, sai Ubangiji ya taɓu da tubansa, ya kuma saurari roƙonsa; saboda haka ya dawo da shi Urushalima da kuma zuwa mulkinsa. Sa’an nan Manasse ya san cewa Ubangiji shi ne Allah.
Molio se i Bog mu se smilovao te usliša njegovu prošnju i vrati ga u Jeruzalem u kraljevstvo. Manaše tada spozna da je Jahve Bog.
14 Daga baya ya sāke gina katangar waje na Birnin Dawuda, yamma da maɓulɓular Gihon a cikin kwari, har zuwa mashigin Ƙofar Kifi, ya kuma kewaye tudun Ofel; ya yi ta da tsayi sosai. Ya sa hafsoshin mayaƙa cikin dukan biranen katanga a Yahuda.
Poslije toga sagradio je vanjski zid Davidovu gradu zapadno od Gihona, od doline pa do Ribljih vrata, i opasao zidom Ofel, izvevši ga vrlo visoko. Postavio je bojne vojvode u svim tvrdim gradovima u Judi.
15 Ya fid da baƙin alloli, ya kuma fid da siffofi daga haikalin Ubangiji, haka ma dukan bagadan da ya gina a kan tudun haikali da kuma cikin Urushalima, ya zubar da su a bayan birni.
Osim toga, uklonio je iz Jahvina Doma tuđinske bogove, onaj idolski lik i sve žrtvenike što ih bijaše posagradio na gori Jahvina Doma i u Jeruzalemu i sve ih baci izvan grada.
16 Sa’an nan ya gyara bagaden Ubangiji ya kuma miƙa hadayun salama da kuma hadayun godiya a bagaden, ya kuma faɗa wa Yahuda su bauta wa Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Zatim opet podiže Jahvin žrtvenik i žrtvova na njemu žrtve pričesnice i zahvalnice. Zapovjedi i Judejcima da služe Jahvi, Bogu Izraelovu.
17 Mutane dai suka ci gaba da miƙa hadayu a masujadai kan tudu, amma wa Ubangiji Allahnsu kaɗai.
Ipak je narod još žrtvovao po uzvišicama, ali samo Jahvi, svojem Bogu.
18 Sauran ayyukan mulkin Manasse, haɗe da addu’arsa ga Allahnsa da kuma kalmomin da mai duba ya yi masa cikin sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, suna a rubuce cikin tarihin sarakunan Isra’ila.
Ostala Manašeova djela i njegova molitva Bogu, riječi koje su mu govorili vidioci u ime Jahve, Izraelova Boga, zapisane su u Povijesti izraelskih kraljeva.
19 Addu’arsa da yadda Allah ya taɓu ta wurin tubansa, da kuma dukan zunubansa da rashin biyayyarsa, da wuraren da ya gina masujadan kan tudu ya kuma kafa ginshiƙan Ashera da gumaka kafin ya ƙasƙantar da kansa, duka suna a rubuce cikin tarihin mai duba.
Njegova molitva i kako je bio uslišan, svi njegovi grijesi i njegova nevjera te mjesta na kojima je pogradio uzvišice, podigao ašere i idole prije nego što se ponizio - sve je to zapisano u povijesti Hozajevoj.
20 Manasse ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a fadansa. Sai Amon ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Tada Manaše počinu kraj svojih otaca. Sahranili su ga u dvoru. Na njegovo se mjesto zakraljio sim mu Amon.
21 Amon yana da shekara ashirin da biyu sa’ad da ya zama sarki, ya yi mulki a Urushalima shekara biyu.
Dvadeset su i dvije godine bile Amonu kad se zakraljio, a kraljevao je dvije godine u Jeruzalemu.
22 Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda mahaifinsa Manasse ya yi. Amon ya bauta ya kuma miƙa hadayu ga dukan gumakan da Manasse ya yi.
Činio je što je zlo u Jahvinim očima, kao i otac mu Manaše, jer je svim idolima koje bijaše načinio njegov otac Manaše on prinosio žrtve i služio im.
23 Amma ba kamar mahaifinsa Manasse ba, bai ƙasƙantar da kansa a gaban Ubangiji ba; Amon ya ƙara laifinsa.
Ali se nije ponizio pred Jahvom kako se ponizio otac mu Manaše, nego je još i umnožio svoju krivicu.
24 Fadawan Amon sukan yi masa maƙarƙashiya, suka kashe shi a fadansa.
Tada se protiv njega urotiše njegove sluge i ubiše ga u dvoru.
25 Sa’an nan mutanen ƙasar suka kashe dukan waɗanda suka yi wa Sarki Amon maƙarƙashiya, suka naɗa Yosiya ɗansa sarki a maimakonsa.
Ali je prosti puk pobio sve one koji se bijahu urotili protiv kralja Amona i na njegovo mjesto zakraljio sina mu Jošiju.

< 2 Tarihi 33 >