< 2 Tarihi 32 >

1 Bayan dukan abin da Hezekiya ya yi cikin aminci, sai Sennakerib sarkin Assuriya ya zo ya yaƙi Yahuda. Ya yi kwanto wa biranen katanga, yana zato zai ci su da yaƙi wa kansa.
Efter denna handel och trohet kom Sanherib, Konungen i Assur, och drog in i Juda, och lägrade sig för de fasta städer, och hade i sinnet, att han ville taga det in.
2 Sa’ad da Hezekiya ya ga Sennakerib ya zo yana kuma niyya yă yaƙi Urushalima,
Då Jehiskia såg, att Sanherib kom, och hans ansigte stod till att strida emot Jerusalem,
3 sai ya yi shawara da fadawansa da hafsoshin mayaƙansa cewa su datse ruwa daga maɓulɓulan ruwan da yake waje da birnin, suka kuwa taimake shi.
Vardt han till råds med sina öfversta och väldiga, att de skulle öfvertäcka vattnen af källorna, som utanför staden voro; och de hulpo honom.
4 Sai babban taro suka haɗu suka datse dukan maɓulɓulai da rafuffukan da suke gudu cikin ƙasar. Suka ce “Me zai sa sarakunan Assuriya su zo su sami ruwa barkatai?”
Och sig församlade mycket folk, och öfvertäckte alla källor och bäcker midt i landena, och sade, att de Konungar af Assur icke skola mycket vatten finna, när de komma.
5 Sai suka yi aiki tuƙuru suna gyaran dukan sassan katangar da suka fāɗi, suna kuma gina hasumiya a kai. Ya gina wata katanga a waje da wannan, ya kuma ƙara ƙarfin madogaran gini na Birnin Dawuda. Ya yi makamai masu yawa da kuma garkuwoyi.
Och han tog styrko till sig, och byggde igen alla murar, som förfallne voro, och gjorde torn deruppå; och byggde ändå derutanföre en annan mur. Och Millo gjorde han fast i Davids stad, och lät göra många värjor och sköldar;
6 Ya naɗa manyan hafsoshi a kan mutane, ya tattara su a gabansa a fili a ƙofar birni, ya kuma ƙarfafa su da waɗannan kalmomi.
Och skickade höfvitsmän till strids med folket; och han församlade dem till sig på den breda gatona vid stadsporten, och talade hjerteliga till dem, och sade:
7 “Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro ko ku yi fargaba saboda sarkin Assuriya, da mayaƙan nan masu yawa da suke tare da shi, gama shi wanda yake tare da mu, ya fi wanda yake tare da su.
Varer tröste och vid godt mod; frukter eder intet, och gifver eder intet för Konungenom af Assur, eller för all den hop, som när honom är; ty med oss är en större än med honom.
8 Mayaƙa na jiki ne kawai suke tare da shi, amma Ubangiji Allahnmu ne yake tare da mu, zai kuwa taimake mu yă kuma yi yaƙinmu.” Mutane kuwa suka amince da maganar Hezekiya, Sarkin Yahuda.
Med honom är en köttslig arm; men med oss är Herren vår Gud, att han skall hjelpa oss, och föra våra strid. Och folket förlät sig på Jehiskia, Juda Konungs, ord.
9 Daga baya, sa’ad da Sennakerib sarkin Assuriya da dukan mayaƙansa suke kwanto wa Lakish, sai ya aiki hafsoshinsa da wannan saƙo wa Hezekiya sarkin Yahuda da kuma wa dukan mutanen Yahuda waɗanda suke can cewa,
Derefter sände Sanherib, Konungen i Assur, sina tjenare till Jerusalem, ty han låg för Lachis, och all hans magt med honom, till Jehiskia, Juda Konung, och till hela Juda, som i Jerusalem var, och lät säga honom:
10 “Ga abin da Sennakerib sarkin Assuriya ya ce ga me kake dogara, har da ka dāge cikin Urushalima da aka yi mata kwanto?
Detta säger Sanherib, Konungen i Assur: Hvar förtrösten I eder uppå, I som bon uti det belagda Jerusalem?
11 Ai, Hezekiya, ruɗinku yake yi, don yă sa ku mutu da yunwa da ƙishirwa sa’ad da yake ce muku, ‘Ubangiji Allahnmu zai cece mu daga hannun sarkin Assuriya.’
Jehiskia förförer eder, att han må komma eder i döden, hunger och törst, och säger: Herren vår Gud skall undsätta oss utu Konungens hand af Assyrien.
12 Hezekiya kansa bai rushe waɗannan masujadan kan tudu da bagadai, yana ce wa Yahuda da Urushalima, ‘Dole ku yi sujada a gaban bagade guda ku kuma ƙone hadayu a kansa ba’?
Är icke han den Jehiskia, som hans höjder och altare bortkastat hafver, och sagt till Juda och Jerusalem: För ett altare skolen I tillbedja, och deruppå röka.
13 “Ba ku san abin da ni da kuma kakannina suka yi wa dukan mutanen sauran ƙasashe ba? Allolin ƙasashen nan sun taɓa iya ceton ƙasarsu daga hannuna ne?
Veten I icke, hvad jag och mine fäder gjort hafva allom folkom i landen? Hafva ock Hedningarnas gudar i landen kunnat hjelpa deras land ifrå mine hand?
14 Wanne a cikin dukan allolin waɗannan ƙasashe da kakannina suka hallaka ya taɓa iya ceton mutanensa daga gare ni? To, yaya Allahnku zai iya cetonku daga hannuna?
Hvilken är den af alla dessa Hedningarnas gudar, som mina fäder nederlagdt hafva, som hafver kunnat hjelpa sitt folk utu mine hand; att edar Gud skulle förmå hjelpa eder utu mine hand?
15 Yanzu fa, kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku yă kuma ɓad da ku haka. Kada ku gaskata shi, gama babu allahn wata ƙasa ko masarautar da ya taɓa iya ceton mutanensa daga hannuna ko kuwa hannun kakannina. Balle har Allahnku yă cece ku daga hannuna!”
Så låter icke nu Hiskia bedraga eder, och låter icke tälja eder i sådant sinne, och tror honom intet; förty, medan ingen alla Hedningars och Konungarikens gud hafver kunnat hjelpa sitt folk ifrå mine och mina fäders hand, så varda icke heller edre gudar eder hjelpande ifrå mine hand.
16 Hafsoshin Sennakerib suka ci gaba da maganar banza wa Ubangiji Allah da kuma a kan bawansa Hezekiya.
Dertill talade hans tjenare ännu mer emot Herran Gud, och emot hans tjenare Jehiskia.
17 Sarki ya kuma rubuta wasiƙu yana zagin Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana faɗin wannan a kansa, “Kamar yadda sauran allolin mutanen sauran ƙasashe ba su iya kuɓutar da mutane daga hannuna ba, haka Allahn Hezekiya ba zai kuɓutar da mutanensa daga hannuna ba.”
Skref han ock bref ut, deruti han hädde Herran Israels Gud, och talade om honom, och sade: Såsom Hedningarnas gudar i landen icke hafva hulpit deras folk ifrå mine hand, så varder ock icke Jehiskia Gud hjelpandes hans folk ifrå mine hand.
18 Sa’an nan suka yi magana da ƙarfi cikin Yahudanci wa mutanen Urushalima waɗanda suke kan katanga, don su firgita su, su kuma sa su ji tsoro don su iya cin birnin.
Och de ropade med höga röst, på Judiskt mål, till folket i Jerusalem, som på muren voro, till att göra dem rädda och förskräckta, att de så måtte få staden.
19 Suka yi magana game da Allah na Urushalima yadda suka yi game da allolin sauran mutanen duniya, aikin hannuwan mutane.
Och talade de så emot Jerusalems Gud, såsom emot folkens gudar på jordene, hvilke menniskos handaverk voro.
20 Sarki Hezekiya da annabi Ishaya ɗan Amoz suka yi kuka cikin addu’a ga sama game da wannan.
Men Konung Jehiskia med Prophetenom Esaia, Amos son, bådo deremot, och ropade till himmelen.
21 Sai Ubangiji ya aiki mala’ika, wanda ya karkashe dukan jarumawa da shugabanni da kuma hafsoshi a sansanin sarkin Assuriyawa. Saboda haka sai sarkin Assuriya ya janye zuwa ƙasarsa da kunya. Da ya shiga haikalin Allahnsa, sai waɗansu a cikin’ya’yansa maza suka yanka shi da takobi.
Och Herren sände en Ängel, som förgjorde alla de väldiga i hären, och Förstarna och öfverstarna i Konungens lägre af Assyrien; så att han med skam drog åter till sitt land igen. Och då han gick uti sins guds hus, dråpo honom der med svärd, de som af hans eget lif komne voro.
22 Ta haka Ubangiji ya ceci Hezekiya da mutanen Urushalima daga hannun Sennakerib sarkin Assuriya da kuma daga hannun dukan sauran. Ya magance su a kowane gefe.
Alltså halp Herren Jehiskia, och dem i Jerusalem, utu Sanheribs hand, Konungens i Assyrien, och alla andras; och bevarade dem för allom omkring;
23 Yawanci mutane suka kawo hadayun ƙonawa zuwa Urushalima wa Ubangiji da kuma kyautai masu daraja wa Hezekiya sarkin Yahuda. Daga lokacin zuwa gaba dukan ƙasashe suka girmama shi.
Så att månge båro skänker Herranom till Jerusalem, och klenodier Jehiskia, Juda Konung. Och han vardt sedan högt räknad för alla Hedningar.
24 A kwanakin nan Hezekiya ya yi ciwo, ya yi kusan mutuwa. Sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wanda ya amsa masa ya kuma ba shi alama.
På den tiden vardt Jehiskia dödsjuk, och han bad Herran; han hörde honom, och gaf honom ett tecken.
25 Amma zuciyar Hezekiya ta yi girman kai, bai kuwa yi amfani da alherin da aka nuna masa ba, saboda haka fushin Ubangiji ya sauko a kansa da kuma a kan Yahuda da Urushalima.
Dock vedergalt icke Jehiskia, efter som honom gifvet var; ty hans hjerta upphof sig; derföre kom vrede öfver honom, och öfver Juda, och Jerusalem.
26 Sai Hezekiya ya tuba daga girma kan zuciyarsa, haka ma mutanen Urushalima; saboda haka fushin Ubangiji bai zo a kansu a kwanakin Hezekiya ba.
Men Jehiskia ödmjukade sig, att hans hjerta hade upphäfvit sig, samt med dem i Jerusalem; derföre kom Herrans vrede icke öfver dem, så länge Jehiskia lefde.
27 Hezekiya mai arziki da girma ne ƙwarai, ya kuma yi baitulmali domin azurfa da zinariyarsa da kuma domin duwatsu masu daraja, kayan yaji, garkuwoyi da kuma domin dukan kayayyaki masu daraja nasa.
Och Jehiskia hade ganska stora rikedomar och härlighet; och han gjorde sig en skatt af silfver, guld, ädla stenar, örter, sköldar och allahanda kostelig tyg;
28 Ya kuma yi gine-gine domin ajiyar hatsi, sabon ruwa inabi da mai; ya kuma yi wuraren ajiyar kowane irin shanu dabam-dabam, da kuma turke domin tumaki.
Och hus till inkommandes årsväxt, vin och oljo; och stall för allahanda boskap, och hus för får.
29 Ya gina ƙauyuka ya kuma samo shanu da garkuna masu yawa, gama Allah ya ba shi arziki mai yawa sosai.
Och han byggde sig städer, och hade boskap, får och fä till en stor hop; förty Gud gaf honom ganska många ägodelar.
30 Hezekiya ne ya datse ruwan bisa na maɓulɓular Gihon, ya sa ruwan ya gangara zuwa gefe yamma na Birnin Dawuda. Ya yi nasara a kome da ya yi.
Han är den Jehiskia, som igentäppte den öfra vattukällona i Gihon, och ledde henne nedåt, vester om Davids stad. Och var Jehiskia lyckosam i alla sina gerningar.
31 Amma da masu mulkin Babilon suka aika da jakadu su tambaye shi game alamar da ta faru a ƙasar, Allah ya rabu da shi don yă gwada shi don yă kuma san kome da yake cikin zuciyarsa.
Men då de öfverstars sändningabåd af Babel till honom sände voro, att fråga efter det undertecken, som i landena skedt var, öfvergaf Gud honom, så att han försökte honom; på det att kunnigt skulle varda allt det i hans hjerta var.
32 Sauran ayyukan mulkin Hezekiya da kuma kyawawa ayyukansa, suna a rubuce a cikin wahayin annabi Ishaya ɗan Amoz, a cikin littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
Hvad nu mer af Jehiskia sägande är, och om hans barmhertighet, si, det är skrifvet i den Propheten Esaia, Amos sons, syn, uti Juda och Israels Konungars bok.
33 Hezekiya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a kan tudu inda makabartan zuriyar Dawuda suke. Dukan Yahuda da kuma mutanen Urushalima suka girmama shi sa’ad da ya mutu. Sai Manasse ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Och Jehiskia afsomnade med sina fäder, och de begrofvo honom öfver Davids barnas grifter; och hele Juda och de i Jerusalem gjorde honom äro i hans död. Och hans son Manasse vardt Konung i hans stad.

< 2 Tarihi 32 >