< 2 Tarihi 32 >

1 Bayan dukan abin da Hezekiya ya yi cikin aminci, sai Sennakerib sarkin Assuriya ya zo ya yaƙi Yahuda. Ya yi kwanto wa biranen katanga, yana zato zai ci su da yaƙi wa kansa.
Depois destas coisas e desta fidelidade, Senaqueribe, rei da Assíria, veio, entrou em Judá, acampou contra as cidades fortificadas, e pretendia ganhá-las para si mesmo.
2 Sa’ad da Hezekiya ya ga Sennakerib ya zo yana kuma niyya yă yaƙi Urushalima,
Quando Ezequias viu que Senaqueribe tinha vindo, e que planejava lutar contra Jerusalém,
3 sai ya yi shawara da fadawansa da hafsoshin mayaƙansa cewa su datse ruwa daga maɓulɓulan ruwan da yake waje da birnin, suka kuwa taimake shi.
aconselhou-se com seus príncipes e seus poderosos homens para deter as águas das nascentes que estavam fora da cidade, e eles o ajudaram.
4 Sai babban taro suka haɗu suka datse dukan maɓulɓulai da rafuffukan da suke gudu cikin ƙasar. Suka ce “Me zai sa sarakunan Assuriya su zo su sami ruwa barkatai?”
Então muitas pessoas se reuniram e pararam todas as nascentes e o riacho que corria pelo meio da terra, dizendo: “Por que os reis da Assíria deveriam vir, e encontrar água abundante”?
5 Sai suka yi aiki tuƙuru suna gyaran dukan sassan katangar da suka fāɗi, suna kuma gina hasumiya a kai. Ya gina wata katanga a waje da wannan, ya kuma ƙara ƙarfin madogaran gini na Birnin Dawuda. Ya yi makamai masu yawa da kuma garkuwoyi.
Ele tomou coragem, construiu toda a muralha que foi derrubada e a elevou até as torres, com a outra muralha do lado de fora, e fortaleceu Millo na cidade de David, e fez armas e escudos em abundância.
6 Ya naɗa manyan hafsoshi a kan mutane, ya tattara su a gabansa a fili a ƙofar birni, ya kuma ƙarfafa su da waɗannan kalmomi.
Ele colocou capitães de guerra sobre o povo, reuniu-os no amplo lugar no portão da cidade e falou encorajadoramente com eles, dizendo:
7 “Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro ko ku yi fargaba saboda sarkin Assuriya, da mayaƙan nan masu yawa da suke tare da shi, gama shi wanda yake tare da mu, ya fi wanda yake tare da su.
“Seja forte e corajoso. Não tenha medo ou consternação por causa do rei da Assíria, nem por toda a multidão que está com ele; pois há um maior entre nós do que com ele.
8 Mayaƙa na jiki ne kawai suke tare da shi, amma Ubangiji Allahnmu ne yake tare da mu, zai kuwa taimake mu yă kuma yi yaƙinmu.” Mutane kuwa suka amince da maganar Hezekiya, Sarkin Yahuda.
Um braço de carne está com ele, mas Javé, nosso Deus, está conosco para nos ajudar e travar nossas batalhas”. O povo descansou sobre as palavras de Ezequias, rei de Judá.
9 Daga baya, sa’ad da Sennakerib sarkin Assuriya da dukan mayaƙansa suke kwanto wa Lakish, sai ya aiki hafsoshinsa da wannan saƙo wa Hezekiya sarkin Yahuda da kuma wa dukan mutanen Yahuda waɗanda suke can cewa,
Depois disso, Senaqueribe, rei da Assíria, enviou seus servos a Jerusalém (agora atacava Laquis, e todas as suas forças estavam com ele), a Ezequias, rei de Judá, e a todo Judá que estava em Jerusalém, dizendo:
10 “Ga abin da Sennakerib sarkin Assuriya ya ce ga me kake dogara, har da ka dāge cikin Urushalima da aka yi mata kwanto?
Senaqueribe, rei da Assíria, diz: “Em quem você confia, que você permanece sitiado em Jerusalém?
11 Ai, Hezekiya, ruɗinku yake yi, don yă sa ku mutu da yunwa da ƙishirwa sa’ad da yake ce muku, ‘Ubangiji Allahnmu zai cece mu daga hannun sarkin Assuriya.’
Não vos convence Ezequias a entregar-vos à morte pela fome e pela sede, dizendo: 'Javé nosso Deus nos livrará das mãos do rei da Assíria'?
12 Hezekiya kansa bai rushe waɗannan masujadan kan tudu da bagadai, yana ce wa Yahuda da Urushalima, ‘Dole ku yi sujada a gaban bagade guda ku kuma ƙone hadayu a kansa ba’?
O mesmo Ezequias não tirou os seus altos e altares e ordenou a Judá e a Jerusalém, dizendo: 'adorareis diante de um altar e nele queimareis incenso'?
13 “Ba ku san abin da ni da kuma kakannina suka yi wa dukan mutanen sauran ƙasashe ba? Allolin ƙasashen nan sun taɓa iya ceton ƙasarsu daga hannuna ne?
Não sabeis o que eu e meus pais fizemos a todos os povos das terras? Será que os deuses das nações dessas terras foram de alguma forma capazes de livrar suas terras das minhas mãos?
14 Wanne a cikin dukan allolin waɗannan ƙasashe da kakannina suka hallaka ya taɓa iya ceton mutanensa daga gare ni? To, yaya Allahnku zai iya cetonku daga hannuna?
Quem estava lá entre todos os deuses daquelas nações que meus pais destruíram completamente e que poderiam livrar seu povo da minha mão, para que seu Deus pudesse livrá-lo da minha mão?
15 Yanzu fa, kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku yă kuma ɓad da ku haka. Kada ku gaskata shi, gama babu allahn wata ƙasa ko masarautar da ya taɓa iya ceton mutanensa daga hannuna ko kuwa hannun kakannina. Balle har Allahnku yă cece ku daga hannuna!”
Agora, portanto, não deixe Hezekiah enganá-lo nem persuadi-lo desta maneira. Não acredite nele, pois nenhum deus de nenhuma nação ou reino foi capaz de livrar seu povo da minha mão, e da mão de meus pais. Quanto menos teu Deus te livrará de minhas mãos”?
16 Hafsoshin Sennakerib suka ci gaba da maganar banza wa Ubangiji Allah da kuma a kan bawansa Hezekiya.
Seus servos falaram ainda mais contra Yahweh Deus e contra seu servo Hezekiah.
17 Sarki ya kuma rubuta wasiƙu yana zagin Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana faɗin wannan a kansa, “Kamar yadda sauran allolin mutanen sauran ƙasashe ba su iya kuɓutar da mutane daga hannuna ba, haka Allahn Hezekiya ba zai kuɓutar da mutanensa daga hannuna ba.”
Ele também escreveu cartas insultando Iavé, o Deus de Israel, e falando contra ele, dizendo: “Como os deuses das nações das terras, que não libertaram seu povo de minhas mãos, assim o Deus de Ezequias não libertará seu povo de minhas mãos”.
18 Sa’an nan suka yi magana da ƙarfi cikin Yahudanci wa mutanen Urushalima waɗanda suke kan katanga, don su firgita su, su kuma sa su ji tsoro don su iya cin birnin.
Eles clamaram com voz alta na língua dos judeus ao povo de Jerusalém que estava no muro, para assustá-los e incomodá-los, para que tomassem a cidade.
19 Suka yi magana game da Allah na Urushalima yadda suka yi game da allolin sauran mutanen duniya, aikin hannuwan mutane.
Falavam do Deus de Jerusalém como dos deuses dos povos da terra, que são obra das mãos dos homens.
20 Sarki Hezekiya da annabi Ishaya ɗan Amoz suka yi kuka cikin addu’a ga sama game da wannan.
O rei Ezequias e o profeta Isaías, o filho de Amoz, rezaram por causa disso, e gritaram ao céu.
21 Sai Ubangiji ya aiki mala’ika, wanda ya karkashe dukan jarumawa da shugabanni da kuma hafsoshi a sansanin sarkin Assuriyawa. Saboda haka sai sarkin Assuriya ya janye zuwa ƙasarsa da kunya. Da ya shiga haikalin Allahnsa, sai waɗansu a cikin’ya’yansa maza suka yanka shi da takobi.
Yahweh enviou um anjo, que cortou todos os homens poderosos de valor, os líderes e capitães do acampamento do rei da Assíria. Assim, ele voltou com vergonha para sua própria terra. Quando entrou na casa de seu deus, aqueles que saíram de seu próprio corpo o mataram lá com a espada.
22 Ta haka Ubangiji ya ceci Hezekiya da mutanen Urushalima daga hannun Sennakerib sarkin Assuriya da kuma daga hannun dukan sauran. Ya magance su a kowane gefe.
Thus Javé salvou Ezequias e os habitantes de Jerusalém da mão de Senaqueribe, o rei da Assíria, e da mão de todos os outros, e os guiou de todos os lados.
23 Yawanci mutane suka kawo hadayun ƙonawa zuwa Urushalima wa Ubangiji da kuma kyautai masu daraja wa Hezekiya sarkin Yahuda. Daga lokacin zuwa gaba dukan ƙasashe suka girmama shi.
Muitos trouxeram presentes a Javé para Jerusalém, e coisas preciosas para Ezequias, rei de Judá, para que ele fosse exaltado à vista de todas as nações a partir de então.
24 A kwanakin nan Hezekiya ya yi ciwo, ya yi kusan mutuwa. Sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wanda ya amsa masa ya kuma ba shi alama.
Naqueles dias Hezekiah estava doente terminal, e rezou a Javé; e falou com ele, e lhe deu um sinal.
25 Amma zuciyar Hezekiya ta yi girman kai, bai kuwa yi amfani da alherin da aka nuna masa ba, saboda haka fushin Ubangiji ya sauko a kansa da kuma a kan Yahuda da Urushalima.
Mas Hezekiah não retribuiu o benefício feito por ele, porque seu coração foi levantado. Portanto, houve ira sobre ele, Judá e Jerusalém.
26 Sai Hezekiya ya tuba daga girma kan zuciyarsa, haka ma mutanen Urushalima; saboda haka fushin Ubangiji bai zo a kansu a kwanakin Hezekiya ba.
However, Ezequias se humilhou pelo orgulho de seu coração, tanto ele como os habitantes de Jerusalém, de modo que a ira de Iavé não veio sobre eles nos dias de Ezequias.
27 Hezekiya mai arziki da girma ne ƙwarai, ya kuma yi baitulmali domin azurfa da zinariyarsa da kuma domin duwatsu masu daraja, kayan yaji, garkuwoyi da kuma domin dukan kayayyaki masu daraja nasa.
Hezekiah tinha riquezas e honrarias extremamente grandes. Ele se proveu de tesouros para prata, ouro, pedras preciosas, especiarias, escudos e todos os tipos de recipientes valiosos;
28 Ya kuma yi gine-gine domin ajiyar hatsi, sabon ruwa inabi da mai; ya kuma yi wuraren ajiyar kowane irin shanu dabam-dabam, da kuma turke domin tumaki.
also armazéns para o aumento de grãos, vinho novo e óleo; e barracas para todos os tipos de animais e rebanhos em dobras.
29 Ya gina ƙauyuka ya kuma samo shanu da garkuna masu yawa, gama Allah ya ba shi arziki mai yawa sosai.
Moreover ele providenciou para si cidades, e possessões de rebanhos e rebanhos em abundância; pois Deus lhe havia dado abundantes possessões.
30 Hezekiya ne ya datse ruwan bisa na maɓulɓular Gihon, ya sa ruwan ya gangara zuwa gefe yamma na Birnin Dawuda. Ya yi nasara a kome da ya yi.
Este mesmo Hezekiah também parou a nascente superior das águas de Gihon, e os trouxe diretamente para o lado oeste da cidade de David. Hezekiah prosperou em todas as suas obras.
31 Amma da masu mulkin Babilon suka aika da jakadu su tambaye shi game alamar da ta faru a ƙasar, Allah ya rabu da shi don yă gwada shi don yă kuma san kome da yake cikin zuciyarsa.
However, a respeito dos embaixadores dos príncipes da Babilônia, que lhe enviaram para indagar sobre a maravilha que foi feita na terra, Deus o deixou para testá-lo, para que ele pudesse saber tudo o que estava em seu coração.
32 Sauran ayyukan mulkin Hezekiya da kuma kyawawa ayyukansa, suna a rubuce a cikin wahayin annabi Ishaya ɗan Amoz, a cikin littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
Agora o resto dos atos de Ezequias e suas boas ações, eis que estão escritos na visão do profeta Isaías, filho de Amoz, no livro dos reis de Judá e Israel.
33 Hezekiya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a kan tudu inda makabartan zuriyar Dawuda suke. Dukan Yahuda da kuma mutanen Urushalima suka girmama shi sa’ad da ya mutu. Sai Manasse ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
Ezequias dormiu com seus pais e eles o enterraram na subida aos túmulos dos filhos de Davi. Todo Judá e os habitantes de Jerusalém o honraram com a sua morte. Manasses, seu filho, reinou em seu lugar.

< 2 Tarihi 32 >