< 2 Tarihi 32 >
1 Bayan dukan abin da Hezekiya ya yi cikin aminci, sai Sennakerib sarkin Assuriya ya zo ya yaƙi Yahuda. Ya yi kwanto wa biranen katanga, yana zato zai ci su da yaƙi wa kansa.
A MAHOPE iho o keia mau mea a me ka hooponopono ana, hiki mai la o Senakeriba ke alii o Asuria, hiki mai la ia ma Iuda, a hoomoana ku e iho la i na kulanakauhale paa i ka pa, me ka manao e lawe pio ia mau mea nona.
2 Sa’ad da Hezekiya ya ga Sennakerib ya zo yana kuma niyya yă yaƙi Urushalima,
A ike o Hezekia, ua hiki mai o Senakeriba, aia hoi kona manao e kaua mai ia Ierusalema,
3 sai ya yi shawara da fadawansa da hafsoshin mayaƙansa cewa su datse ruwa daga maɓulɓulan ruwan da yake waje da birnin, suka kuwa taimake shi.
Kukakuka pu ia me kona poe koa e pani i ka wai o na punawai, aia no mawaho o ke kulanakauhale: a kokua lakou ia ia.
4 Sai babban taro suka haɗu suka datse dukan maɓulɓulai da rafuffukan da suke gudu cikin ƙasar. Suka ce “Me zai sa sarakunan Assuriya su zo su sami ruwa barkatai?”
Hoakoakoaia na kanaka he nui loa, a pani lakou i na punawai a pau, a me ke kahawai i kahe mai mawaena konu o ka aina, i iho la, No ke aha la e hele mai ai na'lii o Asuria, a loaa ia lakou ka wai he nui loa?
5 Sai suka yi aiki tuƙuru suna gyaran dukan sassan katangar da suka fāɗi, suna kuma gina hasumiya a kai. Ya gina wata katanga a waje da wannan, ya kuma ƙara ƙarfin madogaran gini na Birnin Dawuda. Ya yi makamai masu yawa da kuma garkuwoyi.
A hooikaika oia a uhau iho la i kela wahi keia wahi o ka pa i wawahiia, a hookiekie ae a hiki i na halekiai, a i kekahi pa e ae mawaho, a hana hou ia Milo i ke kulanakauhale o Davida, a hana iho la i na ihe a me na palekaua he nui loa.
6 Ya naɗa manyan hafsoshi a kan mutane, ya tattara su a gabansa a fili a ƙofar birni, ya kuma ƙarfafa su da waɗannan kalmomi.
Hoonoho no hoi oia i na luna kaua maluna o na kanaka, a hoakoakoa ia lakou io na la ma ke alanui ma ka ipuka o ke kulanakauhale, a olelo oluolu ia lakou, i aku la,
7 “Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro ko ku yi fargaba saboda sarkin Assuriya, da mayaƙan nan masu yawa da suke tare da shi, gama shi wanda yake tare da mu, ya fi wanda yake tare da su.
E ikaika oukou, e koa hoi, mai makau, aole hoi e weliweli imua o ke alii o Asuria, a imua o keia poe lehulehu a pau me ia: no ka mea, ua oi aku ka poe me makou i ka poe me ia.
8 Mayaƙa na jiki ne kawai suke tare da shi, amma Ubangiji Allahnmu ne yake tare da mu, zai kuwa taimake mu yă kuma yi yaƙinmu.” Mutane kuwa suka amince da maganar Hezekiya, Sarkin Yahuda.
Me ia he lima kanaka; aka, me kakou o Iehova ko kakou Akua, e kokua mai ia kakou, a e kaua i ko kakou kaua. A hilinai na kanaka i na olelo a Hezekia, ke alii o ka Iuda.
9 Daga baya, sa’ad da Sennakerib sarkin Assuriya da dukan mayaƙansa suke kwanto wa Lakish, sai ya aiki hafsoshinsa da wannan saƙo wa Hezekiya sarkin Yahuda da kuma wa dukan mutanen Yahuda waɗanda suke can cewa,
A mahope iho o keia mea, hoouna o Senakeriba ke alii o Asuria i kana poe kaua i Ierusalema, (aia no ia a me kaua poe ikaika me ia e ku e ana ia Lakisa, ) io Hezekia la, ke alii o Iuda, a i ka Iuda a pau, aia ma Ierusalema, i mai la,
10 “Ga abin da Sennakerib sarkin Assuriya ya ce ga me kake dogara, har da ka dāge cikin Urushalima da aka yi mata kwanto?
Penei i olelo ai o Senakeriba, ke alii o Asuria, Ma ke aha la i paulele ai oukou i ko oukou noho ana i ka popilikia ma Ierusalema.
11 Ai, Hezekiya, ruɗinku yake yi, don yă sa ku mutu da yunwa da ƙishirwa sa’ad da yake ce muku, ‘Ubangiji Allahnmu zai cece mu daga hannun sarkin Assuriya.’
Aole anei i hooikaika o Hezekia ia oukou e haawi ia oukou iho i ka make i ka pololi a me ka makewai, i kana olelo ana ae, O Iehova ko kakou Akua, e hoopakele oia ia kakou mai ka lima aku o ke alii o Asuria.
12 Hezekiya kansa bai rushe waɗannan masujadan kan tudu da bagadai, yana ce wa Yahuda da Urushalima, ‘Dole ku yi sujada a gaban bagade guda ku kuma ƙone hadayu a kansa ba’?
Aole anei o ua Hezekia la keia, ka mea nana i lawe aku i kona mau wahi kiekie, a me kona mau kuahu, a olelo aku i ka Iuda, a me ko Ierusalema, i aku la, Imua o ke kuahu hookahi, o hoomana ai oukou, a maluna iho o ia mea e kuni ai i ka mea ala?
13 “Ba ku san abin da ni da kuma kakannina suka yi wa dukan mutanen sauran ƙasashe ba? Allolin ƙasashen nan sun taɓa iya ceton ƙasarsu daga hannuna ne?
Aole anei oukou i ike i ka mea a'u i hana'i, Owau a me ko'u mau makua, i na kanaka a pau o na aina? Ua hiki anei i na akua o na lahuikanaka o na aina ke hoopakele i ko lakou aina mai ko'u lima aku?
14 Wanne a cikin dukan allolin waɗannan ƙasashe da kakannina suka hallaka ya taɓa iya ceton mutanensa daga gare ni? To, yaya Allahnku zai iya cetonku daga hannuna?
Owai ka mea o na akua a pau o ia mau lahuikanaka a ko'u mau makua i luku loa ai, i hiki ia ia ke hoopakele i kona poe kanaka mai ko'u lima aku, i maopopo e hiki i ko oukou Akua ke hoopakele ia oukou mai ko'u lima aku?
15 Yanzu fa, kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku yă kuma ɓad da ku haka. Kada ku gaskata shi, gama babu allahn wata ƙasa ko masarautar da ya taɓa iya ceton mutanensa daga hannuna ko kuwa hannun kakannina. Balle har Allahnku yă cece ku daga hannuna!”
Ano, mai noho a hoopunipuni o Hezekia ia oukou, a malimali mai ia oukou pela, mai paulele oukou ia ia; no ka mea, aole hiki i kekahi akua o kekahi lahuikanaka, a me kekahi aupuni ke hoopakele i kona poe kanaka mai ko'u lima aku, a mai ka lima aku o ko'u poe kupuna; a pehea la e hoopakele ai ko oukou Akua ia oukou mai ko'u lima aku?
16 Hafsoshin Sennakerib suka ci gaba da maganar banza wa Ubangiji Allah da kuma a kan bawansa Hezekiya.
A olelo ino hou aku kana poe kauwa ia Iehova, ke Akua, a ia Hezekia kana kauwa.
17 Sarki ya kuma rubuta wasiƙu yana zagin Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana faɗin wannan a kansa, “Kamar yadda sauran allolin mutanen sauran ƙasashe ba su iya kuɓutar da mutane daga hannuna ba, haka Allahn Hezekiya ba zai kuɓutar da mutanensa daga hannuna ba.”
A kakau ia i na palapala e hoino aku ia Iehova ke Akua o ka Iseraela, me ka olelo aku ia ia, i aku la, E like me na akua o na lahuikanaka o na aina e, aole lakou i hoopakele i ko lakou poe kanaka mai ko'u lima aku, pela hoi, aole e hoopakele ke Akua o Hezekia i kona poe kanaka mai ko'u lima aku.
18 Sa’an nan suka yi magana da ƙarfi cikin Yahudanci wa mutanen Urushalima waɗanda suke kan katanga, don su firgita su, su kuma sa su ji tsoro don su iya cin birnin.
Kahea lakou me ka leo nui, ma ka olelo a ka Iuda, i na kanaka o Ierusalema i ka poe maluna o ka pa, e hoomakau ia lakou, a e hoopihoihoi ia lakou, i loaa mai ke kulanakauhale ia lakou.
19 Suka yi magana game da Allah na Urushalima yadda suka yi game da allolin sauran mutanen duniya, aikin hannuwan mutane.
Olelo ino aku la lakou i ke Akua o Ierusalema, e like me na akua o ko na aina e, na mea a kanaka i hana'i.
20 Sarki Hezekiya da annabi Ishaya ɗan Amoz suka yi kuka cikin addu’a ga sama game da wannan.
No keia mea, pule aku la o Hezekia ke alii, a me Isaia ke keiki a Amosa, ke kaula, a kahea aku laua i ka lani.
21 Sai Ubangiji ya aiki mala’ika, wanda ya karkashe dukan jarumawa da shugabanni da kuma hafsoshi a sansanin sarkin Assuriyawa. Saboda haka sai sarkin Assuriya ya janye zuwa ƙasarsa da kunya. Da ya shiga haikalin Allahnsa, sai waɗansu a cikin’ya’yansa maza suka yanka shi da takobi.
A hoouna mai o Iehova i anela, nana i luku iho i ka poe koa ikaika a pau, a me na luna, a me na kapena, ma kahi i hoomoana'i ke alii o Asuria: a hoi aku ia i kona aina me ka maka hilahila. A hiki ia i ka hale o kona akua, o na mea i puka mailoko mai o kona puhaka, pepehi lakou ia ia malaila i ka pahikaua.
22 Ta haka Ubangiji ya ceci Hezekiya da mutanen Urushalima daga hannun Sennakerib sarkin Assuriya da kuma daga hannun dukan sauran. Ya magance su a kowane gefe.
Pela i hoola ai o Iehova ia Hezekia a me ko Ierusalema mai ka lima aku o Senakeriba ke alii o Asuria, a mai ka lima aku o na mea a pau, a kiai oia maluna o lakou a puni.
23 Yawanci mutane suka kawo hadayun ƙonawa zuwa Urushalima wa Ubangiji da kuma kyautai masu daraja wa Hezekiya sarkin Yahuda. Daga lokacin zuwa gaba dukan ƙasashe suka girmama shi.
A nui ka poe i lawe mai i na makana na Iehova ma Ierusalema, a me na mea haawi wale na Hezekia ke alii o ka Iuda; a ua kiekie oia i na maka o na lahuikanaka a pau mai ia manawa mai.
24 A kwanakin nan Hezekiya ya yi ciwo, ya yi kusan mutuwa. Sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wanda ya amsa masa ya kuma ba shi alama.
Ia mau la, he mai make ko Hezekia, a pule aku la oia ia Iehova; a olelo mai kela ia ia, a hana mai ia ia i ka hana mana.
25 Amma zuciyar Hezekiya ta yi girman kai, bai kuwa yi amfani da alherin da aka nuna masa ba, saboda haka fushin Ubangiji ya sauko a kansa da kuma a kan Yahuda da Urushalima.
Aole hoi i hana aku o Hezekia e like me kana lokomaikaiia mai; no ka mea, ua hookiekieia kona naau: no ia mea, ua hiki mai ka huhu maluna ona, a maluna o ka Iuda a me ko Ierusalema.
26 Sai Hezekiya ya tuba daga girma kan zuciyarsa, haka ma mutanen Urushalima; saboda haka fushin Ubangiji bai zo a kansu a kwanakin Hezekiya ba.
Aka, hoohaahaa o Hezekia ia ia iho no ke kiekie o kona naau, oia a me ko Ierusalema, no ia mea, aole i hiki mai ka huhu o Iehova maluna o lakou i na la o Hezekia.
27 Hezekiya mai arziki da girma ne ƙwarai, ya kuma yi baitulmali domin azurfa da zinariyarsa da kuma domin duwatsu masu daraja, kayan yaji, garkuwoyi da kuma domin dukan kayayyaki masu daraja nasa.
Aia no ia Hezekia ka waiwai a me ka hanohano he nui loa; a hana iho la ia nona i mau waihonawaiwai no ke kala, a no ke gula, a no na pohaku makamae, a no na mea ala, a no na palekaua, a no na ipu maikai a pau o kela ano keia ano;
28 Ya kuma yi gine-gine domin ajiyar hatsi, sabon ruwa inabi da mai; ya kuma yi wuraren ajiyar kowane irin shanu dabam-dabam, da kuma turke domin tumaki.
I na hale paapaa no hoi no ka hoahu ana o ka ai, a me ka waina, a me ka aila; i na wahi no na holoholona a pau loa, a i na pa no hoi no na hipa.
29 Ya gina ƙauyuka ya kuma samo shanu da garkuna masu yawa, gama Allah ya ba shi arziki mai yawa sosai.
Hana no hoi ia nona i na kulanakauhale, a loaa ia ia na hipa, a me na bipi he nui loa; no ka mea, haawi mai no ke Akua ia ia i ka waiwai he nui loa.
30 Hezekiya ne ya datse ruwan bisa na maɓulɓular Gihon, ya sa ruwan ya gangara zuwa gefe yamma na Birnin Dawuda. Ya yi nasara a kome da ya yi.
A o ua Hezekia la, ua pani oia i ke kahawai o Gihona maluna iho, a hookahe pololei mai ia mea ma ka aoao komohana o ke kulanakauhale o Davida. A ua hoopomaikaiia mai o Hezekia ma kana hana ana a pau loa.
31 Amma da masu mulkin Babilon suka aika da jakadu su tambaye shi game alamar da ta faru a ƙasar, Allah ya rabu da shi don yă gwada shi don yă kuma san kome da yake cikin zuciyarsa.
Aka, ma ka mea a na elele a na alii o Babulona i hoounaia mai ai io na la, e imi i ka mea kupanaha i hanaia ma ka aina, ua haalele ke Akua ia ia, e hoao ia ia, i ike oia i kona naau a pau loa.
32 Sauran ayyukan mulkin Hezekiya da kuma kyawawa ayyukansa, suna a rubuce a cikin wahayin annabi Ishaya ɗan Amoz, a cikin littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
A o na mea i koe a Hezekia i hana'i, a me kona maikai, aia hoi ua kakauia ma ka wanana a Isaia ke keiki a Amosa ke kaula, a ma ka buke no na'lii o Iuda a me Iseraela.
33 Hezekiya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a kan tudu inda makabartan zuriyar Dawuda suke. Dukan Yahuda da kuma mutanen Urushalima suka girmama shi sa’ad da ya mutu. Sai Manasse ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
A hiamoe o Hezekia me kona poe kupuna, a kanu lakou ia ia ma kahi kiekie o na ilina no na mamo a Davida, a hoohanohano ka Iuda a pau, a me ko Ierusalema ia ia i kona make ana; a noho alii iho la, o Manase kana keiki ma kona hakahaka.