< 2 Tarihi 32 >

1 Bayan dukan abin da Hezekiya ya yi cikin aminci, sai Sennakerib sarkin Assuriya ya zo ya yaƙi Yahuda. Ya yi kwanto wa biranen katanga, yana zato zai ci su da yaƙi wa kansa.
After King Hezekiah had obeyed Yahweh’s instructions and had done all those things, King Sennacherib of Assyria came [with his army] and invaded Judah. He commanded his soldiers to surround the cities that had walls around them, thinking that they would [break through those walls and] conquer those cities.
2 Sa’ad da Hezekiya ya ga Sennakerib ya zo yana kuma niyya yă yaƙi Urushalima,
When Hezekiah saw that Sennacherib had come [with his army] and that they intended to attack Jerusalem,
3 sai ya yi shawara da fadawansa da hafsoshin mayaƙansa cewa su datse ruwa daga maɓulɓulan ruwan da yake waje da birnin, suka kuwa taimake shi.
he consulted with his officials and army leaders. They said among themselves, “Why should we allow the king of Assyria [and his army] to come and find plenty of water to drink?” So they decided to stop the water from flowing outside the city. So a large group of men gathered together and blocked all the springs and the stream that flowed through that area.
4 Sai babban taro suka haɗu suka datse dukan maɓulɓulai da rafuffukan da suke gudu cikin ƙasar. Suka ce “Me zai sa sarakunan Assuriya su zo su sami ruwa barkatai?”
5 Sai suka yi aiki tuƙuru suna gyaran dukan sassan katangar da suka fāɗi, suna kuma gina hasumiya a kai. Ya gina wata katanga a waje da wannan, ya kuma ƙara ƙarfin madogaran gini na Birnin Dawuda. Ya yi makamai masu yawa da kuma garkuwoyi.
Then they worked hard to repair all the sections of the city wall that had been broken, and they built watchtowers on the walls. They built another wall outside/around the wall that was already outside the city, and they strengthened the defenses on the sloping terraces [on the east side of the area called ‘The City of David’]. They also made a large number of weapons and shields.
6 Ya naɗa manyan hafsoshi a kan mutane, ya tattara su a gabansa a fili a ƙofar birni, ya kuma ƙarfafa su da waɗannan kalmomi.
Hezekiah appointed army commanders, and he gathered them in front of him in the square at one of the city gates, and he encouraged them by saying this to them:
7 “Ku ƙarfafa, ku yi ƙarfin hali. Kada ku ji tsoro ko ku yi fargaba saboda sarkin Assuriya, da mayaƙan nan masu yawa da suke tare da shi, gama shi wanda yake tare da mu, ya fi wanda yake tare da su.
“Be strong and courageous. Do not be afraid or discouraged on account of the king of Assyria and the huge army that is with him, because [Yahweh] is with us, and his [power] is greater than their [power].
8 Mayaƙa na jiki ne kawai suke tare da shi, amma Ubangiji Allahnmu ne yake tare da mu, zai kuwa taimake mu yă kuma yi yaƙinmu.” Mutane kuwa suka amince da maganar Hezekiya, Sarkin Yahuda.
They have to rely on the power of humans, but we have Yahweh our God to help us and to fight battles for us.” So the people became more confident because of what Hezekiah, the king of Judah, said.
9 Daga baya, sa’ad da Sennakerib sarkin Assuriya da dukan mayaƙansa suke kwanto wa Lakish, sai ya aiki hafsoshinsa da wannan saƙo wa Hezekiya sarkin Yahuda da kuma wa dukan mutanen Yahuda waɗanda suke can cewa,
Later, when Sennacherib and all his soldiers were surrounding Lachish [city], he sent some officers to Jerusalem to give this message to King Hezekiah and to all the people of Judah who were there:
10 “Ga abin da Sennakerib sarkin Assuriya ya ce ga me kake dogara, har da ka dāge cikin Urushalima da aka yi mata kwanto?
“[I am] Sennacherib, the [great] king of Assyria, [and] this is what I say: 'While you are staying in Jerusalem, my soldiers are surrounding the city. So why [RHQ] are you so confident?
11 Ai, Hezekiya, ruɗinku yake yi, don yă sa ku mutu da yunwa da ƙishirwa sa’ad da yake ce muku, ‘Ubangiji Allahnmu zai cece mu daga hannun sarkin Assuriya.’
Hezekiah says to you, “Yahweh our God will save us from [being defeated by the army of] the king of Assyria,” but he is misleading you. He wants you to die from having no food or water.
12 Hezekiya kansa bai rushe waɗannan masujadan kan tudu da bagadai, yana ce wa Yahuda da Urushalima, ‘Dole ku yi sujada a gaban bagade guda ku kuma ƙone hadayu a kansa ba’?
Isn’t Hezekiah the one who told his men to get rid of your god Yahweh’s shrines and altars on the hilltops, saying to [you people of] Jerusalem and other places in Judah, “You must worship at only one altar and burn sacrifices on only that altar”?
13 “Ba ku san abin da ni da kuma kakannina suka yi wa dukan mutanen sauran ƙasashe ba? Allolin ƙasashen nan sun taɓa iya ceton ƙasarsu daga hannuna ne?
'Do you people not know what I and my ancestors have done to all the people-groups in other countries? [We destroyed them all, and] none of the gods of those nations were ever able to prevent my [troops] from conquering them! So how can your god prevent my soldiers from conquering you?
14 Wanne a cikin dukan allolin waɗannan ƙasashe da kakannina suka hallaka ya taɓa iya ceton mutanensa daga gare ni? To, yaya Allahnku zai iya cetonku daga hannuna?
15 Yanzu fa, kada ku bar Hezekiya yă ruɗe ku yă kuma ɓad da ku haka. Kada ku gaskata shi, gama babu allahn wata ƙasa ko masarautar da ya taɓa iya ceton mutanensa daga hannuna ko kuwa hannun kakannina. Balle har Allahnku yă cece ku daga hannuna!”
So do not allow Hezekiah to deceive you like this. Do not believe what he says, because no god of any nation or kingdom has ever been able to rescue his people from being conquered by my army and the armies of my ancestors. So certainly your god will not be able to rescue you from my power'.”
16 Hafsoshin Sennakerib suka ci gaba da maganar banza wa Ubangiji Allah da kuma a kan bawansa Hezekiya.
Sennacherib’s officers said more things to belittle Yahweh the God of the Israelis and Hezekiah, who served God [well].
17 Sarki ya kuma rubuta wasiƙu yana zagin Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana faɗin wannan a kansa, “Kamar yadda sauran allolin mutanen sauran ƙasashe ba su iya kuɓutar da mutane daga hannuna ba, haka Allahn Hezekiya ba zai kuɓutar da mutanensa daga hannuna ba.”
King Sennacherib wrote more letters insulting Yahweh, the God whom the Israelis [belonged to/worshiped]. He said things like this: “The gods [worshiped by] the people-groups in other countries did not rescue their people from my power. Similarly, the god of Hezekiah will not rescue his people from my power.”
18 Sa’an nan suka yi magana da ƙarfi cikin Yahudanci wa mutanen Urushalima waɗanda suke kan katanga, don su firgita su, su kuma sa su ji tsoro don su iya cin birnin.
Then King Sennachereb’s officers shouted in the Hebrew language to the people who were on the wall, in order to cause them to be terrified, thinking that as a result the army of Assyria could capture the city [without a battle].
19 Suka yi magana game da Allah na Urushalima yadda suka yi game da allolin sauran mutanen duniya, aikin hannuwan mutane.
They belittled the God [worshiped by the people] of Jerusalem as they belittled the gods of the other people-groups of the world—saying that they were only [idols] made by humans.
20 Sarki Hezekiya da annabi Ishaya ɗan Amoz suka yi kuka cikin addu’a ga sama game da wannan.
Then King Hezekiah and the prophet Isaiah cried out to God, praying about this.
21 Sai Ubangiji ya aiki mala’ika, wanda ya karkashe dukan jarumawa da shugabanni da kuma hafsoshi a sansanin sarkin Assuriyawa. Saboda haka sai sarkin Assuriya ya janye zuwa ƙasarsa da kunya. Da ya shiga haikalin Allahnsa, sai waɗansu a cikin’ya’yansa maza suka yanka shi da takobi.
And [that night] Yahweh sent an angel who killed all the soldiers of Assyria and their leaders and their officers in the place where the king of Assyria and his army had set up their tents. So the king of Assyria left and returned to his own country, very disgraced. And one day when he went into the temple of his god, some of his sons struck him with their swords and killed him.
22 Ta haka Ubangiji ya ceci Hezekiya da mutanen Urushalima daga hannun Sennakerib sarkin Assuriya da kuma daga hannun dukan sauran. Ya magance su a kowane gefe.
That is how Yahweh rescued Hezekiah and the people of Jerusalem from the power of Sennacherib, the king of Assyria, and from their other enemies. Yahweh took care of them (OR, gave them peace) everywhere in the country.
23 Yawanci mutane suka kawo hadayun ƙonawa zuwa Urushalima wa Ubangiji da kuma kyautai masu daraja wa Hezekiya sarkin Yahuda. Daga lokacin zuwa gaba dukan ƙasashe suka girmama shi.
Many people brought offerings for Yahweh to Jerusalem, and also brought valuable gifts for King Hezekiah. And from that time, Hezekiah was highly respected/honored by the people of all the other nations.
24 A kwanakin nan Hezekiya ya yi ciwo, ya yi kusan mutuwa. Sai ya yi addu’a ga Ubangiji, wanda ya amsa masa ya kuma ba shi alama.
About that time, Hezekiah became very ill. He was about to die. But he prayed to Yahweh, and Yahweh answered his prayer. He performed a miracle [and healed Hezekiah].
25 Amma zuciyar Hezekiya ta yi girman kai, bai kuwa yi amfani da alherin da aka nuna masa ba, saboda haka fushin Ubangiji ya sauko a kansa da kuma a kan Yahuda da Urushalima.
But Hezekiah [SYN] was very proud, and he did not thank Yahweh for being kind to him. Therefore Yahweh was angry with him and [and punished him] and [the people of] Jerusalem and other places in Judah.
26 Sai Hezekiya ya tuba daga girma kan zuciyarsa, haka ma mutanen Urushalima; saboda haka fushin Ubangiji bai zo a kansu a kwanakin Hezekiya ba.
Then Hezekiah said that he was sorry for being proud, and the people of Jerusalem also said that they were sorry [for their sins]. So Yahweh did not punish them during the remaining years that Hezekiah [was their king].
27 Hezekiya mai arziki da girma ne ƙwarai, ya kuma yi baitulmali domin azurfa da zinariyarsa da kuma domin duwatsu masu daraja, kayan yaji, garkuwoyi da kuma domin dukan kayayyaki masu daraja nasa.
Hezekiah became very rich and was greatly honored. His [workers] made storerooms for his silver and gold, and for his very valuable stones, and for spices and shields and other valuable things.
28 Ya kuma yi gine-gine domin ajiyar hatsi, sabon ruwa inabi da mai; ya kuma yi wuraren ajiyar kowane irin shanu dabam-dabam, da kuma turke domin tumaki.
[His workers] also built buildings to store the grain and wine and [olive] oil [that people produced and brought to him]. They also made stalls for various kinds of cattle and pens for his flocks [of sheep and goats].
29 Ya gina ƙauyuka ya kuma samo shanu da garkuna masu yawa, gama Allah ya ba shi arziki mai yawa sosai.
They built towns and acquired for the king many flocks [of sheep and goats] and herds [of cattle], because God had enabled him to become very rich.
30 Hezekiya ne ya datse ruwan bisa na maɓulɓular Gihon, ya sa ruwan ya gangara zuwa gefe yamma na Birnin Dawuda. Ya yi nasara a kome da ya yi.
Hezekiah was the one who told his workers to block the place where the water flows out of the Gihon Spring, and to build a tunnel through which the water flowed to the west side of the area called ‘The City of David’. He was able to do everything that he wanted to do.
31 Amma da masu mulkin Babilon suka aika da jakadu su tambaye shi game alamar da ta faru a ƙasar, Allah ya rabu da shi don yă gwada shi don yă kuma san kome da yake cikin zuciyarsa.
But when messengers who were sent by the rulers of Babylon came and asked about the miracle that God had performed for him, God allowed Hezekiah to say what he himself wanted to say, in order to test [whether or not Hezekiah would admit that God had performed a miracle].
32 Sauran ayyukan mulkin Hezekiya da kuma kyawawa ayyukansa, suna a rubuce a cikin wahayin annabi Ishaya ɗan Amoz, a cikin littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
A record of the other things that happened while Hezekiah was ruling, and the things that he did to please God, is on the scroll in which is written the vision that [Yahweh gave to] the prophet Isaiah. It is also written in the scroll called ‘The History of the Kings of Judah and Israel’.
33 Hezekiya ya huta tare da kakanninsa, aka kuma binne shi a kan tudu inda makabartan zuriyar Dawuda suke. Dukan Yahuda da kuma mutanen Urushalima suka girmama shi sa’ad da ya mutu. Sai Manasse ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
When Hezekiah died, he was buried in the tombs where the most respected kings [of Judah] were buried. Everyone in Jerusalem and other places in Judah honored him. Then his son Manasseh became the king.

< 2 Tarihi 32 >