< 2 Tarihi 31 >

1 Sa’ad da aka gama dukan wannan, sai Isra’ilawan da suke can suka fita zuwa garuruwan Yahuda, suka rurrushe keɓaɓɓun duwatsu suka kuma farfashe ginshiƙan Ashera. Suka rurrushe masujadan kan tudu da bagadai, ko’ina a Yahuda da Benyamin da kuma cikin Efraim da Manasse. Bayan sun rurrushe dukansu, sai Isra’ilawa suka koma garuruwansu, kowanne zuwa mahallinsa.
Då detta alltså uträttadt var, drogo ut alle de Israeliter, som i Juda städer funne voro, och bröto ned stoderna, och höggo bort lundarna, och bröto ned höjderna och altaren, i hela Juda, BenJamin, Ephraim och Manasse, tilldess de gjorde en ända på dem. Och Israels barn drogo alle till sina ägor i sina städer igen.
2 Hezekiya kuma ya raba firistoci da Lawiyawa kashi-kashi, kowanne da hidimarsa, firistoci da Lawiyawa, don hadayu na ƙonawa da na salama, su yi hidima, su yi godiya, su kuma rera yabai a ƙofofin mazaunin Ubangiji.
Men Jehiskia ställde Presterna och Leviterna uti deras ordning, hvar och en efter sitt ämbete, både Prester och Leviter, till bränneoffer och tackoffer, att de skulle tjena, tacka och lofva, i portarna åt Herrans lägre.
3 Sarki ya ba da taimako daga mallakarsa domin hadayun ƙonawa, safe da yamma da kuma don hadayun ƙonawa a Asabbatai, Sabon Wata da kuma ƙayyadaddun bukukkuwa kamar yadda yake a rubuce a cikin Dokar Ubangiji.
Och Konungen gaf sin del af sina håfvor till bränneoffer, om morgon och om afton, och till bränneoffer om Sabbatherna, och nymånadom, och högtidom, efter som skrifvet står i Herrans lag.
4 Ya umarci mutanen da suke zama a Urushalima su ba da rabon da yake na firistoci da Lawiyawa, don su ƙwallafa ransu ga Dokar Ubangiji.
Och han sade till folket, som i Jerusalem bodde, att de skulle gifva Presterna och Leviterna delar, att de måtte desto bättre akta på Herrans lag.
5 Nan da nan aka baza umarnin, sai Isra’ilawa suka bayar’ya’yan farin hatsinsu, sabon ruwan inabi, mai da kuma zuma da dukan abin da gona ta bayar, hannu sake. Suka kawo zakan kowane abu da yawa.
Och då det talet kom ut, gåfvo Israels barn mycken förstling af säd, vin, oljo, hannog och allahanda årsväxt på markene; och allahanda tiond förde de in, ganska mycket.
6 Mutanen Isra’ila da Yahuda waɗanda suke zama a garuruwan Yahuda, su ma suka kawo zakan shanu da na tumaki da kuma zakan abubuwa masu tsarki da aka keɓe ga Ubangiji Allahnsu, suka jibge su tsibi-tsibi.
Förde också Israels barn och Juda, som i Juda städer bodde, tiond fram af fä och får, och tiond af det helgada som de Herranom sinom Gud helgat hade, och lade en hop här, och en hop der.
7 Sun fara yin haka a wata na uku, suka kuma gama a wata na bakwai.
Uti tredje månadenom begynte de att lägga hoparna, och i sjunde månadenom lyktade de det.
8 Sa’ad da Hezekiya da fadawansa suka zo suka ga tsibin, sai suka yabi Ubangiji, suka kuma albarkace mutanensa Isra’ila.
Och då Jehiskia med de öfversta ingingo, och sågo hoparna, lofvade de Herran, och hans folk Israel;
9 Hezekiya ya tambayi firistoci da Lawiyawa game da tsibin;
Och Jehiskia frågade Presterna och Leviterna om hoparna.
10 sai Azariya babban firist, daga iyalin Zadok ya amsa, “Tun daga lokacin da mutane suka fara kawo taimakonsu ga haikalin Ubangiji, muna da isashe don abinci da kuma da yawa da za mu rage, domin Ubangiji ya albarkaci mutanensa, saboda haka abin da ya ragu a rumbu yana da yawa.”
Och Asaria Presten, den ypperste i Zadoks hus, sade till honom: Ifrå den tid man begynte införa häfoffret i Herrans hus, hafve vi ätit och äre mätte vordne, och här är ännu mycket qvart; förty Herren hafver välsignat sitt folk; derföre är denne hopen öfverblefven.
11 Hezekiya ya ba da umarni a shirya ɗakunan ajiya a haikalin Ubangiji, aka kuwa yi haka.
Då befallde Konungen, att de skulle reda till kistor i Herrans hus; och de tillredde dem;
12 Sa’an nan cikin aminci suka kawo taimako, zakka da keɓaɓɓun kyautai. Konaniya, wani Balawe, shi ne ke lura da waɗannan abubuwa, kuma ɗan’uwansa Shimeyi shi ne na biye da shi.
Och lade derin häfoffret, tionden, och det helgada, på sina tro. Och öfver det samma var skickad Chanania den Leviten, och Simei hans broder den andre;
13 Yehiyel, Azaziya, Nahat, Asahel, Yerimot, Yozabad, Eliyel, Ismakiya, Mahat da Benahiya su ne shugabanni, mataimakan Konaniya da Shimeyi ɗan’uwansa, waɗanda sarki Hezekiya da Azariya babban shugaban haikalin Allah suka naɗa.
Och Jehiel, Asasia, Nahath, Asahel, Jerimoth, Josabad, Eliel, Jismacha, Mahath och Benaja, förskickade af Chanania och Simei hans broders hand, efter Konungens Jehiskia befallning. Men Asaria var öfverste i Guds hus.
14 Kore ɗan Imna Balawe, mai tsaron Ƙofar Gabas, shi ne yake lura da baikon yardan ran da aka yi wa Allah, don ya karkasa bayarwar da aka keɓe domin Ubangiji da hadayu mafi tsarki.
Och Kore, Jimna son, den Leviten, den dörravaktaren östantill, var öfver de friviljoga Guds gåfvor, som Herranom till häfoffer gifna vordo, och öfver det aldrahelgasta.
15 Eden, Miniyamin, Yeshuwa, Shemahiya, Amariya da Shekaniya sun taimake shi da aminci a cikin garuruwan firistoci, suna ba da rabo wa’yan’uwansu firistoci bisa ga sassansu, tsofaffi da yara.
Och under hans hand voro Eden, Minjamin, Jesua, Semaja, Amaria och Sechania, uti Presternas städer, på sina tro; att de skulle gifva sina bröder efter deras ordning, dem minsta såsom dem största;
16 Bugu da ƙari, suka ba da rabo ga maza’yan shekaru uku ko fiye waɗanda sunayensu suna a tarihin zuriya, dukan waɗanda ba za su iya shiga haikalin Ubangiji su yi ayyukansu na kullum ba, bisa ga nawayarsu da kuma sassansu.
Desslikes dem som för manspersoner räknade vordo, tre åra gamle, och derutöfver, ibland alla dem som uti Herrans hus gingo, hvar på sin dag till sitt ämbete, och i sine vakt efter sitt skifte;
17 Suka kuma ba da rabo ga firistocin da aka rubuta ta iyalansu cikin tarihin zuriya, haka kuma ga Lawiyawa masu shekara ashirin ko fiye, bisa ga nawayarsu da kuma sassansu.
Sammalunda dem som för Prester räknade vordo, i deras fäders hus, och Leviterna, ifrå tjugu år och derutöfver, i deras vakt efter deras skifte;
18 Suka haɗa da dukan ƙanana’ya’yansu, mata, da kuma’ya’ya maza da’ya’ya mata, al’umma gaba ɗaya da aka jera a waɗannan tarihin zuriya. Gama sun yi aminci cikin tsarkake kansu.
Dertill dem som räknade vordo ibland deras barn, hustrur, söner och döttrar, i hela menighetene; förty de helgade på sina tro det helgada.
19 Akwai mutane a garuruwa da yawa waɗanda aka sa don su rarraba wa’ya’yan Haruna, firist, maza, waɗanda suke zaune a gonaki na ƙasar garuruwansu su ba kowane namijin da aka rubuta na Lawiyawa, rabonsa.
Voro också män vid namn nämnde ibland Aarons barn, Presterna uppå förstädernes mark, i alla städer, att de skulle del gifva alla manspersoner ibland Presterna, och allom dem som ibland Leviterna räknade vordo.
20 Abin da Hezekiya ya yi ke nan ko’ina a Yahuda, yana yin abin da yake da kyau, daidai da kuma mai aminci a gaban Ubangiji Allahnsa.
Alltså gjorde Jehiskia i hela Juda, och gjorde det godt, rätt och sant var för Herranom sinom Gud.
21 Cikin kome da ya yi cikin hidimar haikalin Allah, cikin biyayya kuma ga doka da umarnai, ya nemi Allahnsa, ya kuma yi aiki gabagadi. Ta haka kuwa ya yi nasara.
Och i all handel, som han tog sig före med Guds hus tjenste, efter lagen och buden, till att söka sin Gud, det gjorde han af allt hjerta; derföre gick han det ock väl igenom.

< 2 Tarihi 31 >