< 2 Tarihi 30 >
1 Sai Hezekiya ya aika wa dukan Isra’ila da Yahuda, ya kuma rubuta wasiƙu zuwa Efraim da Manasse, yana gayyatarsu su zo haikalin Ubangiji a Urushalima, su kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Entonces Ezequías envió un mensaje a todo Israel y a Judá, y envió cartas a Efraín y Manasés, invitándolos que vinieran a la casa del Señor en Jerusalén para celebrar la Pascua al Señor, el Dios de Israel.
2 Sarki da fadawansa da dukan taro a Urushalima suka yanke shawara su yi Bikin Ƙetarewa a wata na biyu.
Porque el rey, después de una discusión con sus jefes y todo el cuerpo del pueblo en Jerusalén, había tomado la decisión de celebrar la Pascua en el segundo mes.
3 Ba su iya yinsa a daidai lokacinsa ba domin babu isashen firistocin da suka tsarkake kansu, mutane kuma ba su taru a Urushalima ba.
No era posible mantenerlo en ese momento, porque no había suficientes sacerdotes que se hubieran purificado, y la gente no se había reunido en Jerusalén.
4 Shirin ya yi kyau ga sarki da kuma dukan taron.
Y la cosa estaba bien ante los ojos del rey y de todo el pueblo.
5 Suka yanke shawara su yi shelar a ko’ina a Isra’ila, daga Beyersheba zuwa Dan, suna kiran mutane su zo Urushalima, suka kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allah na Isra’ila. Ba a yi bikin da mutane masu yawa bisa ga abin da aka rubuta ba.
Así que se ordenó que la palabra fuera enviada a través de todo Israel, desde Beerseba hasta Dan, para que vinieran a guardar la Pascua al Señor, el Dios de Israel, en Jerusalén; porque muchos no lo tenían en práctica de acuerdo con la ley.
6 Bisa ga umarnin sarki, sai’yan aika suka tafi ko’ina a Isra’ila da Yahuda da wasiƙu daga sarki da kuma daga fadawansa, wasiƙar tana cewa, “Mutanen Isra’ila, ku dawo ga Ubangiji Allah na Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, domin yă dawo gare ku, ku da kuka tafi, ku da kuka kuɓuce daga hannun sarakuna Assuriya.
Y los mensajeros fueron con cartas del rey y sus jefes por todo Israel y Judá, por orden del rey, diciendo: Oh hijos de Israel, regresa de nuevo al Señor, el Dios de Abraham, Isaac e Israel, para que pueda volver a esa pequeña banda tuya que se ha mantenido a salvo de las manos de los reyes de Asiria.
7 Kada ku zama kamar iyayenku da’yan’uwanku, waɗanda suka yi rashin aminci ga Ubangiji Allah na kakanninsu, har ya mai da su abin tsoro, yadda kuke gani.
No seas como sus padres y sus hermanos, que fueron pecadores contra el Señor, el Dios de sus padres, de modo que Él los envió a la desolación, como pueden ver.
8 Kada ku yi taurinkai, yadda iyayenku suka yi; ku miƙa kai ga Ubangiji. Ku zo wuri mai tsarki, wanda ya tsarkake har abada. Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, domin fushi mai zafi yă juye daga gare ku.
Ahora, no seas de corazón duro, como lo fueron tus padres; sino entrégate al Señor, y entra en su lugar santo, que él ha hecho suyo para siempre, y sean siervos del Señor tu Dios, para que el calor de su ira se aleje de ustedes.
9 In kuka dawo wurin Ubangiji, sa’an nan waɗanda suka kama’yan’uwanku da’ya’yanku za su nuna musu tausayi, su kuma dawo wannan ƙasa, gama Ubangiji Allahnku mai alheri ne mai jinƙai kuma. Ba zai kau da fuskarsa daga gare ku ba, in kuka dawo gare shi.”
Porque si regresas al Señor, los que se llevaron a tus hermanos y a tus hijos tendrán compasión delante de los que los llevaron cautivos, y volverán a está tierra; porque el Señor tu Dios está lleno de gracia y de misericordia, y su rostro no se apartará de ustedes si vuelven a él.
10 ’Yan aika suka tafi gari-gari a cikin Efraim da Manasse, har zuwa Zebulun, amma mutane suka yi musu dariyar reni, suka kuma yi musu ba’a.
Así que los corredores fueron de ciudad en ciudad a través de todo el país de Efraín y Manasés hasta Zabulón, pero la gente se reía y se burlaban de ellos.
11 Duk da haka, waɗansu mutanen Asher, Manasse da Zebulun suka ƙasƙantar da kansu suka tafi Urushalima.
Sin embargo, algunos de Aser y Manasés y Zabulón se humillaron ante Dios y acudieron a Jerusalén.
12 Haka ma a Yahuda, hannun Allah yana a kan mutane don yă ba su zuciya ɗaya su yi abin da sarki da fadawansa suka umarta, suna bin maganar Ubangiji.
Y en Judá, el poder de Dios les dio un solo corazón para cumplir las órdenes del rey y los capitanes, conforme a la palabra del Señor.
13 Taron mutane mai girma ya haɗu a Urushalima don Bikin Burodi Marar Yisti a wata na biyu.
Entonces, un gran número de personas se reunieron en Jerusalén para celebrar la fiesta del pan sin levadura en el segundo mes.
14 Suka kawar da bagadai a Urushalima suka fid da bagadan turare suka zubar da su a Kwarin Kidron.
Y se pusieron a trabajar y se llevaron todos los altares de Jerusalén, y los echaron todas las vasijas para quemar incienso en él arroyo de Cedrón.
15 Suka yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a rana ta goma sha huɗu na wata na biyu. Firistoci da Lawiyawa suka ji kunya suka tsarkake kansu, suka kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
Y a los catorce días del segundo mes mataron a los corderos de la Pascua; y los sacerdotes y los levitas se avergonzaron, se purificaron y llevaron ofrendas quemadas a la casa del Señor.
16 Sa’an nan suka ɗauki matsayinsu na kullum yadda yake a Dokar Musa mutumin Allah. Firistoci suka yayyafa jinin da Lawiyawa suka ba su.
Y tomaron sus lugares en el orden correcto, como estaba ordenado en la ley de Moisés, el hombre de Dios; los sacerdotes rociaban sobre el altar la sangre que les dieron los levitas.
17 Da yake da yawa cikin taron ba su tsarkake kansu ba, dole Lawiyawa su yanka’yan ragunan Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda ba su da tsarki, ba su kuma iya tsarkake ragunansu ga Ubangiji ba.
Porque todavía había un número de personas que no se habían purificado; así los levitas tuvieron que dar muerte a los corderos de la Pascua por aquellos que no estaban purificados, y consagrarlos para el Señor.
18 Ko da yake yawancin mutanen da suka zo daga Efraim, Manasse, Issakar da Zebulun ba su tsarkake kansu ba, duk da haka suka ci Bikin Ƙetarewa, ba tare da bin abin da yake a rubuce ba. Amma Hezekiya ya yi addu’a dominsu cewa, “Bari Ubangiji, wanda yake nagari, yă gafarta wa kowa
Para un gran número de personas de Efraín y Manasés, Isacar y Zabulón, no se habían purificado, pero tomaron la comida de la Pascua, aunque no de la manera correcta. Pero Ezequías había orado por ellos, diciendo: Que el buen Señor tenga misericordia de todos aquellos que de corazón sincero lo buscan,
19 wanda ya sa zuciyarsa ga neman Allah, Ubangiji Allah na kakanninsa, ko da shi marar tsarki ne bisa ga dokokin wuri mai tsarki.”
Que con todo su corazón se dirige a Dios el Señor, el Dios de sus antepasados, aunque no hayan sido purificados según las reglas del santuario.
20 Ubangiji kuwa ya ji Hezekiya ya kuma warkar da mutane.
Y él Señor oyó a Ezequías, y sanó a la gente.
21 Isra’ilawan da suka kasance a Urushalima suka yi Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai da farin ciki mai girma, yayinda Lawiyawa da firistoci suke rera ga Ubangiji kowace rana, haɗe da kayan kiɗin yabon Ubangiji.
Entonces los hijos de Israel que estaban presentes en Jerusalén celebraron la fiesta del pan sin levadura durante siete días con gran gozo: y los levitas y los sacerdotes alababan al Señor día tras día, haciendo la melodía con instrumentos al Señor y con voz fuerte.
22 Hezekiya ya yi magana mai ƙarfafawa ga dukan Lawiyawa waɗanda suka nuna ganewar fasaha a hidimar Ubangiji. Kwana bakwai suka ci rabonsu da aka tsara, suka miƙa hadayun salama, suka kuma yabi Ubangiji Allah na kakanninsu.
Entonces Ezequías dijo palabras amables a los levitas que eran expertos en la ministración de la adoración al Señor: así celebraron la fiesta durante siete días, ofreciendo ofrendas de paz y alabando al Señor, el Dios de sus antepasados.
23 Dukan mutanen suka yarda su ƙara kwana bakwai kuma, sai suka ci gaba da bikin cikin farin ciki har waɗansu kwana bakwai kuma.
Y por el deseo de todo el pueblo, la fiesta duró otros siete días, y guardaron los siete días con alegría.
24 Hezekiya sarkin Yahuda ya tanada bijimai dubu ɗaya da tumaki da kuma awaki dubu bakwai wa taron, fadawa kuma suka tanada musu bijimai dubu da kuma tumaki da awaki dubu goma. Firistoci masu yawa suka tsarkake kansu.
Porque Ezequías, rey de Judá, dio al pueblo por ofrendas, mil bueyes y siete mil ovejas; y los príncipes dieron mil bueyes y diez mil ovejas; y muchos sacerdotes se purificaron.
25 Taron gaba ɗaya na Yahuda suka yi farin ciki, tare da firistoci da kuma Lawiyawa da dukan waɗanda suka taru daga Isra’ila, har ma da baƙi waɗanda suka zo daga Isra’ila da waɗanda suke zama a Yahuda.
Y todo el pueblo de Judá, con los sacerdotes y los levitas, y los que habían venido de Israel, y los hombres extranjeros que habían venido de Israel o que vivían en Judá, se alegraron con gran alegría.
26 Aka yi farin ciki mai girma a Urushalima, gama tun zamanin Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila, ba a taɓa yin wani abu kamar haka a Urushalima ba.
Y hubo gran gozo en Jerusalén: porque nada como esto había sido visto en Jerusalén desde el tiempo de Salomón, el hijo de David, rey de Israel.
27 Firistoci da Lawiyawa suka tsaya suka albarkace mutane, Allah kuma ya ji su, gama addu’arsu ya kai sama, mazauninsa mai tsarki.
Entonces los sacerdotes y los levitas dieron a las personas una bendición; y la voz de su oración subió al lugar santo de Dios en el cielo.