< 2 Tarihi 30 >
1 Sai Hezekiya ya aika wa dukan Isra’ila da Yahuda, ya kuma rubuta wasiƙu zuwa Efraim da Manasse, yana gayyatarsu su zo haikalin Ubangiji a Urushalima, su kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Ezéchias envoya aussi vers tout Israël et Juda, et il écrivit des lettres à Ephraïm et à Manassé, afin de les inviter à venir à la maison du Seigneur à Jérusalem, pour faire la Pâque du Seigneur, Dieu d’Israël.
2 Sarki da fadawansa da dukan taro a Urushalima suka yanke shawara su yi Bikin Ƙetarewa a wata na biyu.
Un conseil du roi, des princes et de toute l’assemblée du peuple ayant donc été tenu à Jérusalem, ils décidèrent qu’ils feraient la Pâque au second mois;
3 Ba su iya yinsa a daidai lokacinsa ba domin babu isashen firistocin da suka tsarkake kansu, mutane kuma ba su taru a Urushalima ba.
Car ils n’avaient pu la faire en son temps, parce que les prêtres qui pouvaient exercer n’avaient pas été sanctifiés, et que le peuple ne s’était pas encore assemblé à Jérusalem.
4 Shirin ya yi kyau ga sarki da kuma dukan taron.
La chose plut au roi et à toute la multitude.
5 Suka yanke shawara su yi shelar a ko’ina a Isra’ila, daga Beyersheba zuwa Dan, suna kiran mutane su zo Urushalima, suka kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allah na Isra’ila. Ba a yi bikin da mutane masu yawa bisa ga abin da aka rubuta ba.
Et ils décidèrent qu’ils enverraient des messagers dans tout Israël, de Bersabée jusqu’à Dan, pour qu’on vînt faire la Pâque du Seigneur Dieu d’Israël dans Jérusalem; car beaucoup ne l’avaient pas faite, comme il est prescrit.
6 Bisa ga umarnin sarki, sai’yan aika suka tafi ko’ina a Isra’ila da Yahuda da wasiƙu daga sarki da kuma daga fadawansa, wasiƙar tana cewa, “Mutanen Isra’ila, ku dawo ga Ubangiji Allah na Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, domin yă dawo gare ku, ku da kuka tafi, ku da kuka kuɓuce daga hannun sarakuna Assuriya.
Les messagers partirent donc avec les lettres par le commandement du roi et des princes, et ils passèrent dans tout Israël et Juda, publiant suivant ce que le roi avait commandé: Enfants d’Israël, revenez au Seigneur Dieu d’Abraham, d’Isaac et d’Israël, et il reviendra aux restes qui ont échappé à la main du roi des Assyriens.
7 Kada ku zama kamar iyayenku da’yan’uwanku, waɗanda suka yi rashin aminci ga Ubangiji Allah na kakanninsu, har ya mai da su abin tsoro, yadda kuke gani.
Ne soyez pas comme vos pères et vos frères, qui se sont retirés du Seigneur Dieu de leurs pères, qui les a livrés à la mort, comme vous-mêmes le voyez.
8 Kada ku yi taurinkai, yadda iyayenku suka yi; ku miƙa kai ga Ubangiji. Ku zo wuri mai tsarki, wanda ya tsarkake har abada. Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, domin fushi mai zafi yă juye daga gare ku.
N’endurcissez pas vos cœurs comme vos pères; donnez les mains au Seigneur, et venez à son sanctuaire qu’il a sanctifié pour jamais: servez le Seigneur Dieu de vos pères, et la colère de sa fureur se détournera de vous.
9 In kuka dawo wurin Ubangiji, sa’an nan waɗanda suka kama’yan’uwanku da’ya’yanku za su nuna musu tausayi, su kuma dawo wannan ƙasa, gama Ubangiji Allahnku mai alheri ne mai jinƙai kuma. Ba zai kau da fuskarsa daga gare ku ba, in kuka dawo gare shi.”
Car, si vous revenez au Seigneur, vos frères et vos fils trouveront miséricorde devant les maîtres qui les ont emmenés captifs, et ils reviendront en cette terre; car il est clément et miséricordieux, le Seigneur votre Dieu, et il ne détournera point sa face de vous, si vous revenez à lui.
10 ’Yan aika suka tafi gari-gari a cikin Efraim da Manasse, har zuwa Zebulun, amma mutane suka yi musu dariyar reni, suka kuma yi musu ba’a.
Ainsi les courriers allaient rapidement de ville en ville dans toute la terre d’Ephraïm et de Manassé, jusqu’à Zabulon, ces peuples les raillant et les insultant.
11 Duk da haka, waɗansu mutanen Asher, Manasse da Zebulun suka ƙasƙantar da kansu suka tafi Urushalima.
Cependant quelques hommes d’Azer, de Manassé et de Zabulon, acquiesçant au conseil donné, vinrent à Jérusalem.
12 Haka ma a Yahuda, hannun Allah yana a kan mutane don yă ba su zuciya ɗaya su yi abin da sarki da fadawansa suka umarta, suna bin maganar Ubangiji.
Quant à Juda, la main du Seigneur y fut de manière à leur donner un seul cœur, pour qu’ils fissent, selon le commandement du roi et des princes, la parole du Seigneur.
13 Taron mutane mai girma ya haɗu a Urushalima don Bikin Burodi Marar Yisti a wata na biyu.
Beaucoup de peuples donc s’assemblèrent à Jérusalem, pour faire la solennité des azymes, au second mois.
14 Suka kawar da bagadai a Urushalima suka fid da bagadan turare suka zubar da su a Kwarin Kidron.
Et, se levant, ils détruisirent les autels qui étaient à Jérusalem, et mettant en pièces toutes les choses dans lesquelles on brûlait de l’encens aux idoles, ils les jetèrent dans le torrent de Cédron.
15 Suka yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a rana ta goma sha huɗu na wata na biyu. Firistoci da Lawiyawa suka ji kunya suka tsarkake kansu, suka kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
Ils immolèrent donc la Pâque le quatorzième jour du second mois. De plus les prêtres et les Lévites, enfin sanctifiés, offrirent des holocaustes dans la maison du Seigneur.
16 Sa’an nan suka ɗauki matsayinsu na kullum yadda yake a Dokar Musa mutumin Allah. Firistoci suka yayyafa jinin da Lawiyawa suka ba su.
Et ils se tinrent en leur rang, selon les prescriptions et la loi de Moïse, l’homme de Dieu; mais les prêtres recevaient le sang qui devait être répandu, des mains des Lévites,
17 Da yake da yawa cikin taron ba su tsarkake kansu ba, dole Lawiyawa su yanka’yan ragunan Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda ba su da tsarki, ba su kuma iya tsarkake ragunansu ga Ubangiji ba.
Parce qu’une foule nombreuse n’était pas sanctifiée; et c’est pour cela que les Lévites immolèrent la Pâque pour ceux qui ne s’étaient pas empressés de se sanctifier au Seigneur.
18 Ko da yake yawancin mutanen da suka zo daga Efraim, Manasse, Issakar da Zebulun ba su tsarkake kansu ba, duk da haka suka ci Bikin Ƙetarewa, ba tare da bin abin da yake a rubuce ba. Amma Hezekiya ya yi addu’a dominsu cewa, “Bari Ubangiji, wanda yake nagari, yă gafarta wa kowa
Comme aussi une grande partie du peuple d’Ephraïm, de Manassé, d’Issachar de Zabulon, qui n’avait pas été sanctifiée, mangea la Pâque, non suivant ce qui est écrit; et Ezéchias pria pour eux, disant: Le Seigneur, qui est bon, se montrera propice
19 wanda ya sa zuciyarsa ga neman Allah, Ubangiji Allah na kakanninsa, ko da shi marar tsarki ne bisa ga dokokin wuri mai tsarki.”
À tous ceux qui en tout leur cœur cherchent le Seigneur Dieu de leurs pères, et il ne leur imputera point de n’être pas sanctifiés.
20 Ubangiji kuwa ya ji Hezekiya ya kuma warkar da mutane.
Le Seigneur l’exauça, et s’apaisa pour le peuple.
21 Isra’ilawan da suka kasance a Urushalima suka yi Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai da farin ciki mai girma, yayinda Lawiyawa da firistoci suke rera ga Ubangiji kowace rana, haɗe da kayan kiɗin yabon Ubangiji.
Et les enfants d’Israël qui se trouvèrent à Jérusalem firent la solennité des azymes durant sept jours, dans une grande joie, louant le Seigneur chaque jour aussi bien que les Lévites et les prêtres, sur les instruments qui répondaient à leur fonction.
22 Hezekiya ya yi magana mai ƙarfafawa ga dukan Lawiyawa waɗanda suka nuna ganewar fasaha a hidimar Ubangiji. Kwana bakwai suka ci rabonsu da aka tsara, suka miƙa hadayun salama, suka kuma yabi Ubangiji Allah na kakanninsu.
Et Ezéchias parla au cœur de tous les Lévites qui avaient une intelligence parfaite de ce qui regarde le Seigneur; et ils mangèrent, durant les sept jours de la solennité, immolant des victimes de sacrifices pacifiques, et louant le Seigneur Dieu de leurs pères.
23 Dukan mutanen suka yarda su ƙara kwana bakwai kuma, sai suka ci gaba da bikin cikin farin ciki har waɗansu kwana bakwai kuma.
Et il plut à toute la multitude de célébrer encore sept autres, jours, ce qu’ils firent aussi avec une grande joie;
24 Hezekiya sarkin Yahuda ya tanada bijimai dubu ɗaya da tumaki da kuma awaki dubu bakwai wa taron, fadawa kuma suka tanada musu bijimai dubu da kuma tumaki da awaki dubu goma. Firistoci masu yawa suka tsarkake kansu.
Car Ezéchias, roi de Juda, avait donné à la multitude mille taureaux et sept mille brebis: et les princes avaient donné au peuple mille taureaux et dix mille brebis. Ainsi une très grande multitude de prêtres se purifia.
25 Taron gaba ɗaya na Yahuda suka yi farin ciki, tare da firistoci da kuma Lawiyawa da dukan waɗanda suka taru daga Isra’ila, har ma da baƙi waɗanda suka zo daga Isra’ila da waɗanda suke zama a Yahuda.
Et tout le peuple de Juda fut comblé de joie, tant les prêtres et les Lévites, que toute la foule qui était venue d’Israël, les prosélytes mêmes de la terre d’Israël, et ceux qui habitaient en Juda.
26 Aka yi farin ciki mai girma a Urushalima, gama tun zamanin Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila, ba a taɓa yin wani abu kamar haka a Urushalima ba.
Et il se fit une grande solennité à Jérusalem, telle qu’il n’y en avait pas eu dans cette ville depuis les jours de Salomon, fils de David, roi d’Israël.
27 Firistoci da Lawiyawa suka tsaya suka albarkace mutane, Allah kuma ya ji su, gama addu’arsu ya kai sama, mazauninsa mai tsarki.
Or les prêtres et les Lévites se levèrent pour bénir le peuple; et leur voix fut exaucée, et leur prière parvint jusqu’à la demeure sainte du ciel.