< 2 Tarihi 30 >

1 Sai Hezekiya ya aika wa dukan Isra’ila da Yahuda, ya kuma rubuta wasiƙu zuwa Efraim da Manasse, yana gayyatarsu su zo haikalin Ubangiji a Urushalima, su kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Puis Ézéchias envoya vers tout Israël et Juda; et il écrivit même des lettres à Éphraïm et à Manassé, pour qu'ils vinssent à la maison de l'Éternel, à Jérusalem, célébrer la pâque en l'honneur de l'Éternel, le Dieu d'Israël.
2 Sarki da fadawansa da dukan taro a Urushalima suka yanke shawara su yi Bikin Ƙetarewa a wata na biyu.
Le roi, et ses chefs et toute l'assemblée, avaient résolu en conseil, à Jérusalem, de célébrer la pâque au second mois;
3 Ba su iya yinsa a daidai lokacinsa ba domin babu isashen firistocin da suka tsarkake kansu, mutane kuma ba su taru a Urushalima ba.
Car on n'avait pas pu la célébrer en son temps, parce qu'il n'y avait pas assez de sacrificateurs sanctifiés, et que le peuple n'était pas rassemblé à Jérusalem.
4 Shirin ya yi kyau ga sarki da kuma dukan taron.
La chose plut au roi et à toute l'assemblée;
5 Suka yanke shawara su yi shelar a ko’ina a Isra’ila, daga Beyersheba zuwa Dan, suna kiran mutane su zo Urushalima, suka kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allah na Isra’ila. Ba a yi bikin da mutane masu yawa bisa ga abin da aka rubuta ba.
Et ils décidèrent de publier par tout Israël, depuis Béer-Shéba jusqu'à Dan, qu'on vînt célébrer la pâque à l'Éternel, le Dieu d'Israël, à Jérusalem; car depuis longtemps ils ne l'avaient pas célébrée conformément à ce qui est écrit.
6 Bisa ga umarnin sarki, sai’yan aika suka tafi ko’ina a Isra’ila da Yahuda da wasiƙu daga sarki da kuma daga fadawansa, wasiƙar tana cewa, “Mutanen Isra’ila, ku dawo ga Ubangiji Allah na Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, domin yă dawo gare ku, ku da kuka tafi, ku da kuka kuɓuce daga hannun sarakuna Assuriya.
Les coureurs allèrent donc avec des lettres de la part du roi et de ses chefs, par tout Israël et Juda, en disant, selon que le roi l'avait commandé: Enfants d'Israël, retournez à l'Éternel, le Dieu d'Abraham, d'Isaac et d'Israël, et il reviendra vers le reste d'entre vous qui est échappé de la main des rois d'Assyrie.
7 Kada ku zama kamar iyayenku da’yan’uwanku, waɗanda suka yi rashin aminci ga Ubangiji Allah na kakanninsu, har ya mai da su abin tsoro, yadda kuke gani.
Ne soyez pas comme vos pères, ni comme vos frères, qui ont péché contre l'Éternel, le Dieu de leurs pères, de sorte qu'il les a mis en désolation, comme vous le voyez.
8 Kada ku yi taurinkai, yadda iyayenku suka yi; ku miƙa kai ga Ubangiji. Ku zo wuri mai tsarki, wanda ya tsarkake har abada. Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, domin fushi mai zafi yă juye daga gare ku.
Maintenant, ne roidissez pas votre cou, comme vos pères; tendez la main vers l'Éternel, venez à son sanctuaire, qu'il a consacré pour toujours, servez l'Éternel, votre Dieu, et l'ardeur de sa colère se détournera de vous.
9 In kuka dawo wurin Ubangiji, sa’an nan waɗanda suka kama’yan’uwanku da’ya’yanku za su nuna musu tausayi, su kuma dawo wannan ƙasa, gama Ubangiji Allahnku mai alheri ne mai jinƙai kuma. Ba zai kau da fuskarsa daga gare ku ba, in kuka dawo gare shi.”
Car si vous retournez à l'Éternel, vos frères et vos fils trouveront miséricorde auprès de ceux qui les ont emmenés captifs, et ils reviendront en ce pays, parce que l'Éternel, votre Dieu, est clément et miséricordieux; et il ne détournera point sa face de vous, si vous revenez à lui.
10 ’Yan aika suka tafi gari-gari a cikin Efraim da Manasse, har zuwa Zebulun, amma mutane suka yi musu dariyar reni, suka kuma yi musu ba’a.
Les coureurs passaient ainsi de ville en ville, par le pays d'Éphraïm et de Manassé, et jusqu'à Zabulon; mais l'on se moquait d'eux et l'on s'en raillait.
11 Duk da haka, waɗansu mutanen Asher, Manasse da Zebulun suka ƙasƙantar da kansu suka tafi Urushalima.
Toutefois, quelques-uns d'Asser, de Manassé et de Zabulon s'humilièrent, et vinrent à Jérusalem.
12 Haka ma a Yahuda, hannun Allah yana a kan mutane don yă ba su zuciya ɗaya su yi abin da sarki da fadawansa suka umarta, suna bin maganar Ubangiji.
La main de Dieu fut aussi sur Juda, pour leur donner un même cœur, afin d'exécuter le commandement du roi et des chefs, selon la parole de l'Éternel.
13 Taron mutane mai girma ya haɗu a Urushalima don Bikin Burodi Marar Yisti a wata na biyu.
Et il s'assembla à Jérusalem un peuple nombreux, pour célébrer la fête des pains sans levain, au second mois: ce fut une fort grande assemblée.
14 Suka kawar da bagadai a Urushalima suka fid da bagadan turare suka zubar da su a Kwarin Kidron.
Ils se levèrent, et ils ôtèrent les autels qui étaient dans Jérusalem; ils ôtèrent aussi tous ceux où l'on brûlait de l'encens, et ils les jetèrent dans le torrent de Cédron.
15 Suka yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a rana ta goma sha huɗu na wata na biyu. Firistoci da Lawiyawa suka ji kunya suka tsarkake kansu, suka kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
Puis on immola la pâque, au quatorzième jour du second mois; car les sacrificateurs et les Lévites avaient eu honte et s'étaient sanctifiés, et ils offrirent des holocaustes dans la maison de l'Éternel.
16 Sa’an nan suka ɗauki matsayinsu na kullum yadda yake a Dokar Musa mutumin Allah. Firistoci suka yayyafa jinin da Lawiyawa suka ba su.
Ils se tinrent, à leur place, suivant leur règle, d'après la loi de Moïse, homme de Dieu. Et les sacrificateurs répandaient le sang qu'ils recevaient de la main des Lévites.
17 Da yake da yawa cikin taron ba su tsarkake kansu ba, dole Lawiyawa su yanka’yan ragunan Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda ba su da tsarki, ba su kuma iya tsarkake ragunansu ga Ubangiji ba.
Car il y en avait une grande partie dans l'assemblée qui ne s'étaient pas purifiés; et les Lévites eurent la charge d'immoler les victimes de la pâque pour tous ceux qui n'étaient pas purs, afin de les consacrer à l'Éternel.
18 Ko da yake yawancin mutanen da suka zo daga Efraim, Manasse, Issakar da Zebulun ba su tsarkake kansu ba, duk da haka suka ci Bikin Ƙetarewa, ba tare da bin abin da yake a rubuce ba. Amma Hezekiya ya yi addu’a dominsu cewa, “Bari Ubangiji, wanda yake nagari, yă gafarta wa kowa
Car une grande partie du peuple, beaucoup de ceux d'Éphraïm, de Manassé, d'Issacar et de Zabulon, ne s'étaient pas purifiés, et mangèrent la pâque, sans se conformer à ce qui est écrit. Mais Ézéchias pria pour eux, en disant: Que l'Éternel, qui est bon, fasse l'expiation,
19 wanda ya sa zuciyarsa ga neman Allah, Ubangiji Allah na kakanninsa, ko da shi marar tsarki ne bisa ga dokokin wuri mai tsarki.”
Pour quiconque a disposé son cœur à rechercher Dieu, l'Éternel, le Dieu de ses pères, bien que ce ne soit pas selon la purification du sanctuaire!
20 Ubangiji kuwa ya ji Hezekiya ya kuma warkar da mutane.
Et l'Éternel exauça Ézéchias, et il pardonna au peuple.
21 Isra’ilawan da suka kasance a Urushalima suka yi Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai da farin ciki mai girma, yayinda Lawiyawa da firistoci suke rera ga Ubangiji kowace rana, haɗe da kayan kiɗin yabon Ubangiji.
Les enfants d'Israël qui se trouvèrent à Jérusalem célébrèrent donc la fête des pains sans levain, pendant sept jours, avec une grande joie; et les Lévites et les sacrificateurs célébraient l'Éternel chaque jour, avec les instruments qui retentissaient à la louange de l'Éternel.
22 Hezekiya ya yi magana mai ƙarfafawa ga dukan Lawiyawa waɗanda suka nuna ganewar fasaha a hidimar Ubangiji. Kwana bakwai suka ci rabonsu da aka tsara, suka miƙa hadayun salama, suka kuma yabi Ubangiji Allah na kakanninsu.
Et Ézéchias parla au cœur de tous les Lévites, qui se montraient intelligents dans la bonne science du service de l'Éternel. Ils mangèrent les repas de la fête pendant sept jours, offrant des sacrifices de prospérités, et louant l'Éternel le Dieu de leurs pères.
23 Dukan mutanen suka yarda su ƙara kwana bakwai kuma, sai suka ci gaba da bikin cikin farin ciki har waɗansu kwana bakwai kuma.
Puis toute l'assemblée résolut de célébrer sept autres jours. Et ils célébrèrent ces sept jours dans la joie.
24 Hezekiya sarkin Yahuda ya tanada bijimai dubu ɗaya da tumaki da kuma awaki dubu bakwai wa taron, fadawa kuma suka tanada musu bijimai dubu da kuma tumaki da awaki dubu goma. Firistoci masu yawa suka tsarkake kansu.
Car Ézéchias, roi de Juda, fit présent à l'assemblée de mille taureaux et de sept mille moutons; et les chefs firent présent à l'assemblée de mille taureaux et de dix mille moutons; et des sacrificateurs, en grand nombre, s'étaient sanctifiés.
25 Taron gaba ɗaya na Yahuda suka yi farin ciki, tare da firistoci da kuma Lawiyawa da dukan waɗanda suka taru daga Isra’ila, har ma da baƙi waɗanda suka zo daga Isra’ila da waɗanda suke zama a Yahuda.
Et toute l'assemblée de Juda, avec les sacrificateurs et les Lévites, et toute l'assemblée venue d'Israël, et les étrangers venus du pays d'Israël, et ceux qui habitaient en Juda, se réjouirent.
26 Aka yi farin ciki mai girma a Urushalima, gama tun zamanin Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila, ba a taɓa yin wani abu kamar haka a Urushalima ba.
Il y eut donc une grande joie à Jérusalem; car depuis le temps de Salomon, fils de David, roi d'Israël, il n'y avait rien eu de semblable dans Jérusalem.
27 Firistoci da Lawiyawa suka tsaya suka albarkace mutane, Allah kuma ya ji su, gama addu’arsu ya kai sama, mazauninsa mai tsarki.
Puis les sacrificateurs lévites se levèrent et bénirent le peuple, et leur voix fut entendue, et leur prière parvint jusqu'aux cieux, jusqu'à la sainte demeure de l'Éternel.

< 2 Tarihi 30 >