< 2 Tarihi 30 >
1 Sai Hezekiya ya aika wa dukan Isra’ila da Yahuda, ya kuma rubuta wasiƙu zuwa Efraim da Manasse, yana gayyatarsu su zo haikalin Ubangiji a Urushalima, su kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
And Ezechie sente to al Israel and to Juda, and he wroot pistlis to Effraym and to Manasses, that thei schulden come in to the hous of the Lord in Jerusalem, and make paske to the Lord God of Israel.
2 Sarki da fadawansa da dukan taro a Urushalima suka yanke shawara su yi Bikin Ƙetarewa a wata na biyu.
Therfor whanne counseil was takun of the kyng, and of princes, and of al the cumpeny of Jerusalem, thei demyden to make paske in the secounde moneth.
3 Ba su iya yinsa a daidai lokacinsa ba domin babu isashen firistocin da suka tsarkake kansu, mutane kuma ba su taru a Urushalima ba.
For thei demyden not to do in his tyme; for the preestis that myyten suffice weren not halewid, and the puple was not yit gaderid in to Jerusalem.
4 Shirin ya yi kyau ga sarki da kuma dukan taron.
And the word pleside the king, and al the multitude.
5 Suka yanke shawara su yi shelar a ko’ina a Isra’ila, daga Beyersheba zuwa Dan, suna kiran mutane su zo Urushalima, suka kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allah na Isra’ila. Ba a yi bikin da mutane masu yawa bisa ga abin da aka rubuta ba.
And thei demyden to sende messangeris in to al Israel, fro Bersabee `til to Dan, that thei schulden come, and make pask to the Lord God of Israel in Jerusalem; for many men hadden not do, as it is bifor writun in the lawe.
6 Bisa ga umarnin sarki, sai’yan aika suka tafi ko’ina a Isra’ila da Yahuda da wasiƙu daga sarki da kuma daga fadawansa, wasiƙar tana cewa, “Mutanen Isra’ila, ku dawo ga Ubangiji Allah na Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, domin yă dawo gare ku, ku da kuka tafi, ku da kuka kuɓuce daga hannun sarakuna Assuriya.
And corouris yeden forth with pistlis, bi comaundement of the kyng and of hise princis, in to al Israel and Juda, and prechiden bi that, that the kyng hadde comaundid, Sones of Israel, turne ye ayen to the Lord God of Abraham, and of Isaac, and of Israel; and he schal turne ayen to the residue men, that ascapiden the hondis of the kyng of Assiriens.
7 Kada ku zama kamar iyayenku da’yan’uwanku, waɗanda suka yi rashin aminci ga Ubangiji Allah na kakanninsu, har ya mai da su abin tsoro, yadda kuke gani.
Nyle ye be maad as youre fadris and britheren, that yeden awei fro the Lord God of her fadris; and he yaue hem in to perischyng, as ye seen.
8 Kada ku yi taurinkai, yadda iyayenku suka yi; ku miƙa kai ga Ubangiji. Ku zo wuri mai tsarki, wanda ya tsarkake har abada. Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, domin fushi mai zafi yă juye daga gare ku.
Nyle ye make hard youre nollis, as youre fadris diden; yyue ye hondis to the Lord, and come ye to his seyntuarie, which he halewide withouten ende; serue ye the Lord God of youre fadris, and the ire of his strong veniaunce schal `be turned awey fro you.
9 In kuka dawo wurin Ubangiji, sa’an nan waɗanda suka kama’yan’uwanku da’ya’yanku za su nuna musu tausayi, su kuma dawo wannan ƙasa, gama Ubangiji Allahnku mai alheri ne mai jinƙai kuma. Ba zai kau da fuskarsa daga gare ku ba, in kuka dawo gare shi.”
For if ye turnen ayen to the Lord, youre britheren and youre sones schulen haue mercy, bifor her lordis that ledden hem prisoneris; and thei schulen turne ayen in to this lond. For `oure Lord God is pitouse, `ethir benygne, and merciful; and he schal not turne awey his face fro you, if ye turne ayen to hym.
10 ’Yan aika suka tafi gari-gari a cikin Efraim da Manasse, har zuwa Zebulun, amma mutane suka yi musu dariyar reni, suka kuma yi musu ba’a.
Therfor the corours yeden swiftli fro cytee in to citee thorou the lond of Effraym and of Manasses `til to Zabulon, while thei scorniden and bimowiden hem.
11 Duk da haka, waɗansu mutanen Asher, Manasse da Zebulun suka ƙasƙantar da kansu suka tafi Urushalima.
Netheles sum men of Aser, and of Manasses, and of Zabulon, assentiden to the counsel, and camen in to Jerusalem.
12 Haka ma a Yahuda, hannun Allah yana a kan mutane don yă ba su zuciya ɗaya su yi abin da sarki da fadawansa suka umarta, suna bin maganar Ubangiji.
Forsothe the hond of the Lord was maad in Juda, that he yaf to hem oon herte, and that thei diden the word of the Lord, bi the comaundement of the kyng and of the princes.
13 Taron mutane mai girma ya haɗu a Urushalima don Bikin Burodi Marar Yisti a wata na biyu.
And many puplis weren gaderid in to Jerusalem, for to make the solempnyte of therf looues in the secounde monethe.
14 Suka kawar da bagadai a Urushalima suka fid da bagadan turare suka zubar da su a Kwarin Kidron.
And thei risiden, and destrieden the auteris, that weren in Jerusalem; and `thei destriynge alle thingis in whiche encense was brent to idols, castiden forth in to the stronde of Cedron.
15 Suka yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a rana ta goma sha huɗu na wata na biyu. Firistoci da Lawiyawa suka ji kunya suka tsarkake kansu, suka kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
Forsothe thei offriden pask in the fourtenthe dai of the secounde monethe; also the preestis and the dekenes weren halewid at the laste, and offriden brent sacrifices in the hows of the Lord.
16 Sa’an nan suka ɗauki matsayinsu na kullum yadda yake a Dokar Musa mutumin Allah. Firistoci suka yayyafa jinin da Lawiyawa suka ba su.
And thei stoden in her ordre, bi the ordynaunce and lawe of Moises, the man of God. Sothely the preestis token of the hondis of dekenes the blood to be sched out,
17 Da yake da yawa cikin taron ba su tsarkake kansu ba, dole Lawiyawa su yanka’yan ragunan Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda ba su da tsarki, ba su kuma iya tsarkake ragunansu ga Ubangiji ba.
for myche cumpeny was not halewid; and therfor the dekenes offriden pask for hem, that myyten not be halewid to the Lord.
18 Ko da yake yawancin mutanen da suka zo daga Efraim, Manasse, Issakar da Zebulun ba su tsarkake kansu ba, duk da haka suka ci Bikin Ƙetarewa, ba tare da bin abin da yake a rubuce ba. Amma Hezekiya ya yi addu’a dominsu cewa, “Bari Ubangiji, wanda yake nagari, yă gafarta wa kowa
Also a greet part of the puple of Effraym, and Manasses, and of Ysachar, and of Zabulon, that was not halewid, eet pask not bi that that is writun. And Ezechie preyde for hem, and seide, The good Lord schal do mercy to alle men,
19 wanda ya sa zuciyarsa ga neman Allah, Ubangiji Allah na kakanninsa, ko da shi marar tsarki ne bisa ga dokokin wuri mai tsarki.”
that seken in al the herte the Lord God of her fadris; and it schal not be arettid to hem, that thei ben not halewid.
20 Ubangiji kuwa ya ji Hezekiya ya kuma warkar da mutane.
And the Lord herde hym, and was plesid to the puple.
21 Isra’ilawan da suka kasance a Urushalima suka yi Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai da farin ciki mai girma, yayinda Lawiyawa da firistoci suke rera ga Ubangiji kowace rana, haɗe da kayan kiɗin yabon Ubangiji.
And the sones of Israel, that weren founden in Jerusalem, maden solempnyte of therf looues seuene daies in greet gladnesse, and herieden the Lord bi ech dai; and dekenes and preestis `preisiden the Lord bi orguns, that acordiden to her offices.
22 Hezekiya ya yi magana mai ƙarfafawa ga dukan Lawiyawa waɗanda suka nuna ganewar fasaha a hidimar Ubangiji. Kwana bakwai suka ci rabonsu da aka tsara, suka miƙa hadayun salama, suka kuma yabi Ubangiji Allah na kakanninsu.
And Ezechie spak to the herte of alle the dekenes, that hadden good vndurstondyng of the Lord; and thei eeten bi seuene daies of the solempnyte, offrynge sacrifices of pesible thingis, and heriynge the Lord God of her fadris.
23 Dukan mutanen suka yarda su ƙara kwana bakwai kuma, sai suka ci gaba da bikin cikin farin ciki har waɗansu kwana bakwai kuma.
And it pleside al the multitude to halewe also othere seuene daies; which thing also thei diden with greet ioye.
24 Hezekiya sarkin Yahuda ya tanada bijimai dubu ɗaya da tumaki da kuma awaki dubu bakwai wa taron, fadawa kuma suka tanada musu bijimai dubu da kuma tumaki da awaki dubu goma. Firistoci masu yawa suka tsarkake kansu.
Forsothe Ezechie, kyng of Juda, yaf to the multitude a thousynde bolis, and seuene thousynde of scheep; sotheli the princes yauen to the puple a thousynde bolis, and ten thousynde scheep. Therfor ful greet multitude of preestis was halewid;
25 Taron gaba ɗaya na Yahuda suka yi farin ciki, tare da firistoci da kuma Lawiyawa da dukan waɗanda suka taru daga Isra’ila, har ma da baƙi waɗanda suka zo daga Isra’ila da waɗanda suke zama a Yahuda.
and al the cumpany of Juda was fillid with gladnesse, as wel of preestis and dekenes, as of al the multitude, that camen fro Israel, and `of conuersis of the lond of Israel, and of dwelleris in Juda.
26 Aka yi farin ciki mai girma a Urushalima, gama tun zamanin Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila, ba a taɓa yin wani abu kamar haka a Urushalima ba.
And greet solempnytee was maad in Jerusalem, which maner solempnyte was not in that citee fro the daies of Salomon, sone of Dauid, kyng of Israel.
27 Firistoci da Lawiyawa suka tsaya suka albarkace mutane, Allah kuma ya ji su, gama addu’arsu ya kai sama, mazauninsa mai tsarki.
Sotheli preestis and dekenes rysyden, and blessiden the puple; and the vois of hem was herd, and the preier cam in to the hooli dwelling place of heuene.