< 2 Tarihi 30 >

1 Sai Hezekiya ya aika wa dukan Isra’ila da Yahuda, ya kuma rubuta wasiƙu zuwa Efraim da Manasse, yana gayyatarsu su zo haikalin Ubangiji a Urushalima, su kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
Then sent Hezekiah to all Israel and Judah, and he also wrote letters to Ephraim and Manasseh, that they should come to the house of the Lord at Jerusalem, to prepare the passover-sacrifice unto the Lord the God of Israel.
2 Sarki da fadawansa da dukan taro a Urushalima suka yanke shawara su yi Bikin Ƙetarewa a wata na biyu.
And the king held a consultation, as also his princes, and all the assembly in Jerusalem, to prepare the passover-sacrifice in the second month.
3 Ba su iya yinsa a daidai lokacinsa ba domin babu isashen firistocin da suka tsarkake kansu, mutane kuma ba su taru a Urushalima ba.
For they were not able to prepare it at that time; because the priests had not sanctified themselves sufficiently, nor had the people gathered themselves together to Jerusalem.
4 Shirin ya yi kyau ga sarki da kuma dukan taron.
And the thing seemed right in the eyes of the king and in the eyes of all the assembly.
5 Suka yanke shawara su yi shelar a ko’ina a Isra’ila, daga Beyersheba zuwa Dan, suna kiran mutane su zo Urushalima, suka kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allah na Isra’ila. Ba a yi bikin da mutane masu yawa bisa ga abin da aka rubuta ba.
So they established a decree to cause a proclamation to be made throughout all Israel, from Beer-sheba' even as far as Dan, that they should come to prepare the passover-sacrifice unto thy Lord the God of Israel at Jerusalem; because for a long time past they had not prepared it as it was written,
6 Bisa ga umarnin sarki, sai’yan aika suka tafi ko’ina a Isra’ila da Yahuda da wasiƙu daga sarki da kuma daga fadawansa, wasiƙar tana cewa, “Mutanen Isra’ila, ku dawo ga Ubangiji Allah na Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, domin yă dawo gare ku, ku da kuka tafi, ku da kuka kuɓuce daga hannun sarakuna Assuriya.
So the runners went with the letters from the hand of the king and his princes throughout all Israel and Judah, and according to the command of the king, saying, O children of Israel, return unto the Lord the God of Abraham, of Isaac, and of Israel, and he will return to the remnant of you, that are escaped out of the power of the kings of Assyria.
7 Kada ku zama kamar iyayenku da’yan’uwanku, waɗanda suka yi rashin aminci ga Ubangiji Allah na kakanninsu, har ya mai da su abin tsoro, yadda kuke gani.
And be net like your fathers, and like your brethren, who acted faithlessly against the Lord the God of their fathers, wherefore he gave them up to become an [object of] astonishment, as ye see.
8 Kada ku yi taurinkai, yadda iyayenku suka yi; ku miƙa kai ga Ubangiji. Ku zo wuri mai tsarki, wanda ya tsarkake har abada. Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, domin fushi mai zafi yă juye daga gare ku.
Now do ye not harden your necks, like your fathers: hold out your hand unto the Lord, and come unto his sanctuary, which he hath sanctified for ever, and serve the Lord your God, and so will he turn away from you the fierceness of his wrath.
9 In kuka dawo wurin Ubangiji, sa’an nan waɗanda suka kama’yan’uwanku da’ya’yanku za su nuna musu tausayi, su kuma dawo wannan ƙasa, gama Ubangiji Allahnku mai alheri ne mai jinƙai kuma. Ba zai kau da fuskarsa daga gare ku ba, in kuka dawo gare shi.”
For If ye return unto the Lord, your brethren and your children will find mercy in the presence of their captors, so that they may return to this land; for the Lord your God is gracious and merciful, and will not turn away his countenance from you, if ye return unto him.
10 ’Yan aika suka tafi gari-gari a cikin Efraim da Manasse, har zuwa Zebulun, amma mutane suka yi musu dariyar reni, suka kuma yi musu ba’a.
And as the runners were passing from city to city through the country of Ephraim and Menasseh and as far as Zebulun, they were laughing them to scorn, and mocking at them.
11 Duk da haka, waɗansu mutanen Asher, Manasse da Zebulun suka ƙasƙantar da kansu suka tafi Urushalima.
Nevertheless some men of Asher and Menasseh and of Zebulun humbled themselves, and came to Jerusalem.
12 Haka ma a Yahuda, hannun Allah yana a kan mutane don yă ba su zuciya ɗaya su yi abin da sarki da fadawansa suka umarta, suna bin maganar Ubangiji.
Also over Judah came the hand of God to give unto them one heart to do the command of the king and of the princes, by the word of the Lord.
13 Taron mutane mai girma ya haɗu a Urushalima don Bikin Burodi Marar Yisti a wata na biyu.
And there was gathered together at Jerusalem a numerous people to keep the feast of unleavened bread in the second month, a very great assembly.
14 Suka kawar da bagadai a Urushalima suka fid da bagadan turare suka zubar da su a Kwarin Kidron.
And they arose and removed the altars which were in Jerusalem, and all the vessels for burning incense did they take away, and they threw them into the brook Kidron.
15 Suka yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a rana ta goma sha huɗu na wata na biyu. Firistoci da Lawiyawa suka ji kunya suka tsarkake kansu, suka kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
And they slaughtered the passover-sacrifice on the fourteenth day of the second month: and the priests and the Levites were ashamed, and sanctified themselves, and brought burnt-offerings unto the house of the Lord.
16 Sa’an nan suka ɗauki matsayinsu na kullum yadda yake a Dokar Musa mutumin Allah. Firistoci suka yayyafa jinin da Lawiyawa suka ba su.
And they stood on their station after their prescribed manner, according to the law of Moses the man of God, the priest sprinkling the blood, [which they received] out of the hand of the Levites.
17 Da yake da yawa cikin taron ba su tsarkake kansu ba, dole Lawiyawa su yanka’yan ragunan Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda ba su da tsarki, ba su kuma iya tsarkake ragunansu ga Ubangiji ba.
For there were many in the assembly that had not sanctified themselves: therefore the Levites had the charge of the slaughtering of the passover sacrifices for every one that was not clean, to sanctify [the same] unto the Lord.
18 Ko da yake yawancin mutanen da suka zo daga Efraim, Manasse, Issakar da Zebulun ba su tsarkake kansu ba, duk da haka suka ci Bikin Ƙetarewa, ba tare da bin abin da yake a rubuce ba. Amma Hezekiya ya yi addu’a dominsu cewa, “Bari Ubangiji, wanda yake nagari, yă gafarta wa kowa
For a large portion of the people, even many out of Ephraim, and Menasseh, Issachar, and Zebulun, had not cleansed themselves, but ate the passover not as it is written. However Hezekiah prayed for them, saying, The Lord who is good will grant pardon for this.
19 wanda ya sa zuciyarsa ga neman Allah, Ubangiji Allah na kakanninsa, ko da shi marar tsarki ne bisa ga dokokin wuri mai tsarki.”
To every one that hath directed his heart to seek God, the Lord the God of his fathers; though he be not [cleansed] according to the purification of the sanctuary.
20 Ubangiji kuwa ya ji Hezekiya ya kuma warkar da mutane.
And the Lord hearkened to Hezekiah, and he healed the people.
21 Isra’ilawan da suka kasance a Urushalima suka yi Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai da farin ciki mai girma, yayinda Lawiyawa da firistoci suke rera ga Ubangiji kowace rana, haɗe da kayan kiɗin yabon Ubangiji.
And the children of Israel that were present at Jerusalem celebrated the feast of unleavened bread seven days with great joy; and the Levites and the priests praised the Lord day by day, with loud instruments before the Lord.
22 Hezekiya ya yi magana mai ƙarfafawa ga dukan Lawiyawa waɗanda suka nuna ganewar fasaha a hidimar Ubangiji. Kwana bakwai suka ci rabonsu da aka tsara, suka miƙa hadayun salama, suka kuma yabi Ubangiji Allah na kakanninsu.
And Hezekiah spoke comfortingly unto all the Levites that had good intelligence of the Lord: and they ate the festive-offerings during seven days, offering peace-offerings, and making confession to the Lord the God of their fathers.
23 Dukan mutanen suka yarda su ƙara kwana bakwai kuma, sai suka ci gaba da bikin cikin farin ciki har waɗansu kwana bakwai kuma.
And the whole assembly took counsel to celebrate other seven days: and they celebrated [these] seven days with joy.
24 Hezekiya sarkin Yahuda ya tanada bijimai dubu ɗaya da tumaki da kuma awaki dubu bakwai wa taron, fadawa kuma suka tanada musu bijimai dubu da kuma tumaki da awaki dubu goma. Firistoci masu yawa suka tsarkake kansu.
For Hezekiah king of Judah had provided for the assembly one thousand bullocks and seven thousand sheep; and the princes had provided for the assembly one thousand bullocks and ten thousand sheep: and the priests sanctified themselves in great numbers.
25 Taron gaba ɗaya na Yahuda suka yi farin ciki, tare da firistoci da kuma Lawiyawa da dukan waɗanda suka taru daga Isra’ila, har ma da baƙi waɗanda suka zo daga Isra’ila da waɗanda suke zama a Yahuda.
And thus rejoiced all the assembly of Judah, and the priests and the Levites, and all the assembly that was come out of Israel, and the strangers that were come out of the land of Israel, and those that dwelt in Judah.
26 Aka yi farin ciki mai girma a Urushalima, gama tun zamanin Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila, ba a taɓa yin wani abu kamar haka a Urushalima ba.
And there was great joy in Jerusalem: for since the time of Solomon the son of David the king of Israel had the like not been in Jerusalem.
27 Firistoci da Lawiyawa suka tsaya suka albarkace mutane, Allah kuma ya ji su, gama addu’arsu ya kai sama, mazauninsa mai tsarki.
Then arose the priests the Levites and blessed the people: and their voice was listened to, and their prayer came to His holy dwelling-place, even unto heaven.

< 2 Tarihi 30 >