< 2 Tarihi 29 >

1 Hezekiya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Abiya,’yar Zakariya.
HOOMAKA iho la o Hezekia e alii i kona makahiki he iwakaluakumamalima, a he iwakaluakumamaiwa makahiki kona noho alii ana ma Ierusalema; a o ka inoa o kona makuwahine, o Abia, ke kaikamahine a Zekaria.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda kakansa Dawuda ya yi.
Hana pololei iho la oia imua i ke alo o Iehova, e like me na mea a pau a Davida kona kupuna i hana'i.
3 A wata na farkon a farkon shekarar mulkinsa, ya buɗe ƙofofin haikalin Ubangiji ya gyara su.
I ka makahiki mua o kona noho alii ana, a i ka malama mua no hoi, wehe ae la ia i na puka o ka hale o Iehova, a hana hou ia mau mea.
4 Ya kawo firistoci da Lawiyawa, ya tattara su a filin da yake a gefen gabas
Kii aku ia i na kahuna a me na Levi, a houluulu ia lakou ma ke ala ma ka hikina;
5 ya kuma ce musu, “Ku saurare ni, Lawiyawa! Ku tsarkake kanku yanzu, ku kuma tsarkake haikalin Ubangiji Allah na kakanninku. Ku fid da ƙazanta daga wuri mai tsarki.
Olelo aku la oia ia lakou, E hoolohe mai oukou ia'u, e na Levi; ano, e huikala oukou ia oukou iho, a e hoomaemae oukou i ka hale o Iehova ke Akua o ko oukou poe kupuna, a e lawe aku i na mea haumia mai kahi hoano aku.
6 Kakanninku ba su yi aminci ba; suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnmu, suka kuma yashe shi. Suka juya fuskokinsu daga mazaunin Ubangiji suka kuma juya masa baya.
No ka mea, ua lawehala ko kakou poe kupuna, ua hana ino lakou imua i ke alo o Iehova, ko kakou Akua, ua haalele lakou ia ia, ua huli ko lakou maka mai ka halelewa o Iehova aku, a ua haawi mai lakou i ke kua.
7 Suka kulle ƙofofin shirayi, suka kuma kashe fitilu. Ba su ƙone turare ko su miƙa hadayun ƙonawa a wuri mai tsarki ga Allah na Isra’ila ba.
A ua pani lakou i na puka o ka lanai, ua kinai i na kukui, aole lakou i kuni i ka mea ala, aole hoi i mohai aku lakou i kekahi mohai ma kahi hoano o ke Akua o ka Iseraela.
8 Saboda haka, fushin Ubangiji ya fāɗo a kan Yahuda da Urushalima; ya mai da su abin tsoro da abin banrazana da kuma abin ba’a, kamar yadda kuke gani da idanunku.
No ia mea, ua kauia mai ka huhu o Iehova maluna o ka Iuda, a me ko Ierusalema, a ua haawi oia ia lakou i ka hana ino ia mai, a me ka heneheneia mai, a me ka hoowahawahaia mai, e like me ka mea a ko oukou mau maka i ike iho nei.
9 Abin da ya sa ke nan kakanninmu suka fāɗi ta takobi, kuma shi ya sa aka kai’ya’yanmu maza da’ya’yanmu mata da matanmu bauta.
Aia hoi, ua haule ko kakou poe kupuna i ka pahikaua, a o ka kakou poe keiki kane, a me na kaikamahine a kakou, a me na wahine a kakou, he poe pio lakou no keia hewa.
10 Yanzu ina niyya in yi alkawari da Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin fushinsa yă kauce daga gare mu.
Ano, eia no iloko o ko'u naau e hana i berita me Iehova ke Akua o ka Iseraela, i huli ae kona huhu wela mai o kakou aku.
11 ’Ya’yana maza, kada ku yi sakaci yanzu, gama Ubangiji ya zaɓe ku don ku tsaya a gabansa ku kuma yi masa hidima, don ku yi hidima a gabansa ku kuma ƙone turare.”
Ano, e ka'u poe keiki, mai lalau oukou; no ka mea, ua wae mai o Iehova ia oukou e ku imua ona e hookauwa nana, a e lawelawe i kana mau oihana, a e kuni i ka mea ala.
12 Sai waɗannan Lawiyawa suka shiga aiki, daga Kohatawa Mahat ɗan Amasai da Yowel ɗan Azariya. Daga Kabilar Merari, Kish ɗan Abdi da Azariya ɗan Yahallelel. Daga Gershonawa, Yowa ɗan Zimma da Eden ɗan Yowa.
Alaila, ku ae la iluna na Levi, o Mahata, ke keiki a Amasai, a me Ioela, ke keiki a Azaria, no ka poe mamo a Kohata; a no ka poe mamo a Merari, o Kisa ke keiki a Abedi, a me Azaria ke keiki a Iehalelela; a o ka poe mamo a Geresoma, o Ioa ke keiki a Zima, a o Edena ke keiki a Ioa;
13 Daga zuriyar Elizafan, Shimri da Yehiyel. Daga zuriyar Asaf, Zakariya da Mattaniya.
A no ka poe mamo a Elizapana, o Simeri, a me Ieila; a no ka poe mamo a Asapa, o Zekaria, a me Matania;
14 Daga iyalin Heman, Yehiyel da Shimeyi. Daga zuriyar Yedutun, Shemahiya da Uzziyel.
A no ka poe mamo a Hemana, o Iehiela, a me Simei; a no ka poe mamo a Iedutuna, o Semaia a me Uziela.
15 Da suka tattara’yan’uwansu suka kuma tsarkake kansu, sai suka shiga ciki suka tsarkake haikalin Ubangiji, kamar yadda sarki ya umarta, suna bin maganar Ubangiji.
A houluulu lakou i ko lakou poe hoahanau, a huikala ia lakou iho, a hele mai e like me ke kauoha a ke alii, a me ka olelo a Iehova, e hoomaemae i ka hale o Iehova.
16 Firistoci suka shiga cikin wuri mai tsarki na Ubangiji suka tsarkake shi. Suka fitar da dukan abin da yake marar tsabta da suka samu a haikalin Ubangiji zuwa filin haikalin Ubangiji. Lawiyawa suka ɗauke su suka kai su Kwarin Kidron.
A komo na kahuna iloko lilo o ka hale o Iehova e hoomaemae, a lawe lakou iwaho i na mea maemae ole a pau i loaa ia lakou ma ka luakini o Iehova, a waiho ma ke kahua o ka hale o Iehova. A lawe ka poe mamo a Levi ia mau mea, a hali aku i ke kahawai o Kiderona.
17 Suka fara tsarkakewar a rana ta farko na farkon wata, a rana ta takwas na watan kuwa suka kai shirayin Ubangiji. Karin kwana takwas kuma suka tsarkake haikalin Ubangiji kansa, suka gama a rana ta goma sha shida na farkon wata.
Hoomaka lakou e hoomaemae i ka la mua o ka malama mua, a i ka la ewalu o ua malama la ua hiki lakou i ka lanai o Iehova; pela i hoomaemae ai lakou i ka hale o Iehova i na la ewalu, a i ka la umikumamaono o ka malama mua, hoopau ae la lakou.
18 Sa’an nan suka tafi wurin Sarki Hezekiya suka faɗa masa, “Mun tsarkake haikalin Ubangiji gaba ɗaya, bagaden ƙone hadaya tare da dukan kayayyakinsa, da tebur don shirya tsarkaken burodi, tare da dukan kayayyakinsa.
A komo lakou iloko io Hezekia la, ke alii, a olelo aku la ia ia, Ua hoomaemae makou i ka hale o Iehova a pau, a me ke kuahu mohai, a me ko laila mau kiaha a pau, a me ka papa berena hoike, a me ko laila mau kiaha a pau.
19 Mun shirya muka kuma tsarkake dukan kayayyakin da Sarki Ahaz ya cire cikin rashin amincinsa yayinda yake sarki. Yanzu suna a gaban bagaden Ubangiji.”
A me na kiaha a pau a ke alii a Ahaza i kiola aku ai, i kona lawehala ana i kona wa i noho alii ai, hoomakaukau makou, a hoomaemae no hoi, aia hoi ia mau mea imua o ke kuahu o Iehova.
20 Da sassafe kashegari Sarki Hezekiya ya tattara manyan birni wuri ɗaya, suka haura zuwa haikalin Ubangiji.
A kakahiaka nui ala ae la o Hezekia, ke alii, a houluulu i na alii o ke kulanakauhale, a pii aku i ka hale o Iehova.
21 Suka kawo bijimai bakwai, raguna bakwai, bunsurai bakwai da kuma awaki mata bakwai a matsayin hadaya don zunubi domin masarauta, domin wuri mai tsarki da kuma domin Yahuda. Sarki ya umarce firistoci, zuriyar Haruna, su miƙa waɗannan a bagaden Ubangiji.
A lawe mai lakou i ehiku bipi kane, a me na hipa keiki ehiku, a me na kao kane ehiku, i mohaihala no ke aupuni, a no ke keenakapu, a no ka Iuda; a kauoha aku la ia i na mamo a Aarona, i na kahuna, e mohai aku ia mau mea maluna o ke kuahu o Iehova.
22 Saboda haka suka yayyanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin suka yayyafa a kan bagade. Suka kuma yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagaden. Haka kuma suka yanka’yan ragunan suka yayyafa jinin a bagaden.
A pepehi iho la lakou i na bipi, a lawe na kahuna i ke koko, a kapipi iho la maluna o ke kuahu; a pepehi no hoi lakou i na hipa kane, a kapipi iho la i ke koko maluna o ke kuahu; a pepehi lakou i na hipa keiki no hoi, a kapipi iho la i ke koko maluna o ke kuahu.
23 Aka kawo awaki domin hadaya don zunubi a gaban sarki da taron, suka kuwa ɗibiya hannuwansu a kansu.
A kai mai la lakou i na kao kane i mohaihala imua o ke alii, a me ka ahakanaka; a kau lakou i ko lakou mau lima maluna o ia mau mea:
24 Sa’an nan firistoci suka yayyanka awakin suka miƙa jininsu a bagade domin hadaya don zunubi don kafara saboda dukan Isra’ila, domin sarki ya umarta a yi hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi domin dukan Isra’ila.
A pepehi na kahuna ia mau mea, a mohai aku i ko lakou koko maluna o ke kuahu, i mea e uhi ai i ka hala no ka Iseraela a pau; no ka mea, no ka Iseraela a pau i kauoha ai ke alii i ka mohaikuni a me ka mohaihala.
25 Sarki Hezekiya ya ajiye Lawiyawa a cikin haikalin Ubangiji tare da ganguna, garayu da molaye, yadda Dawuda da Gad mai duba na sarki da kuma annabi Natan suka tsara. Ubangiji ne ya umarta wannan ta wurin annabawansa.
A hoonoho iho la oia i na Levi iloko o ka hale o Iehova me na kimebala, a me na pesaletera, a me na mea kani, e like me ke kauoha a Davida, a me Gada ke kumu a ke alii, a me Natana ke kaula: no ka mea, pela ke kauoha a Iehova ma na kaula.
26 Saboda haka Lawiyawa suka tsaya a shirye tare da kayan kiɗin Dawuda, firistoci kuma tare da ƙahoninsu.
A ku ae la iluna na Levi me na mea kani a Davida, a o na kahuna kekahi me na pu.
27 Hezekiya ya ba da umarni a miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagade. Yayinda aka fara miƙawa, ana rerawa ga Ubangiji, tare da bushe-bushe da kiɗe-kiɗen kayan waƙa na Dawuda sarkin Isra’ila.
Alaila, kauoha o Hezekia e mohai aku i ka mohai maluna o ke kuahu; a i ka wa i hoomaka ai lakou e mohai aku, hoomaka no hoi ka himeni o Iehova me na pu a me na mea kani, a Davida ke alii o ka Iseraela.
28 Dukan taron suka durƙusa suka yi sujada, yayinda mawaƙa suke rerawa, ana kuma busa ƙahoni, dukan wannan ya ci gaba sai da aka gama miƙa hadaya ta ƙonawa.
A o ka ahakanaka a pau loa, kulou iho la lakou, a himeni aku ka poe himeni, puhi no hoi ka poe puhi pu; a hana pela a pau ka mohai ana.
29 Sa’ad da aka gama miƙawa, sai sarki da mutanen da suke tare da shi suka durƙusa suka yi sujada.
A pau ae la ka mohai ana, kulou iho la ke alii, a me ka poe malaila pu me ia a pau, a hoomana aku la.
30 Sarki Hezekiya da fadawansa suka umarci Lawiyawa su yabi Ubangiji da kalmomin Dawuda da na Asaf mai duba. Saboda haka suka rera yabai da murna, suka sunkuyar da kawunansu suka yi sujada.
Alaila, kauoha ae la o Hezekia ke alii, a me na kaukaualii i na Levi, e hoomaikai aku ia Iehova ma na olelo a Davida, a me Asapa ke kaula. A hoomaikai aku lakou me ka olioli, kulou iho la, a hoomana aku la.
31 Sa’an nan Hezekiya ya ce, “Yanzu kun keɓe kanku ga Ubangiji. Ku zo ku kuma kawo hadayu da hadayun godiya zuwa ga haikalin Ubangiji.” Saboda haka taron suka kawo hadayu da hadayun godiya, da kuma dukan waɗanda suke da niyya suka kawo hadayun ƙonawa.
Olelo mai la o Hezekia, i mai la, Ano, ua hoolaa oukou ia oukou iho no Iehova, e hele mai, a e lawe mai i na mohai, a me na mohai aloha i ka hale o Iehova. A lawe mai ka ahakanaka i na alana, a me na mohai aloha; a o ka poe a pau i makemake ka naau, lawe mai lakou i na mohaikuni.
32 Yawan hadayun ƙonawan da taron suka kawo, bijimai saba’in ne, raguna ɗari da kuma bunsurai ɗari biyu, dukansu kuwa domin hadayun ƙonawa ga Ubangiji ne.
O na mohaikuni ma ka helu ana, a ka ahakanaka i lawe mai ai, he kanahiku bipi, hookahi haneri hipa kane, a elua haneri hipa keiki: no ka mohaikuni ia Iehova keia mau mea a pau loa.
33 Dabbobin da aka tsarkake a matsayi hadayu sun kai bijimai ɗari shida da tumaki da kuma awaki dubu uku.
A o na mea i hoolaaia, eono haneri bipi, a ekolu tausani hipa.
34 Firistoci fa, suka kāsa sosai don fiɗan dukan dabbobin da za a miƙa don hadayun ƙonawa; saboda haka’yan’uwansu Lawiyawa suka taimake su har aka gama aiki kafin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. Gama Lawiyawa sun fi firistoci himma wajen tsarkakewar kansu.
Aka, aole i nui ka poe kahuna, aole hiki ia lakou wale no ke pepehi i na mohaikuni a pau: no ia mea, kokua mai ko lakou poe hoahanau, o na Levi, a hiki i ka pau ana o ka hana, a i ka wa hoi i huikala mai ai ka poe kahuna ia lakou iho; no ka mea, ua oi aku ka pololei o ka naau o na Levi e huikala ia lakou iho mamua o na kahuna.
35 Aka kasance da hadayun ƙonawa a yalwace, tare da kitsen hadayun salama da hadayun sha da suke tafe da hadayun ƙonawa. Saboda haka aka sāke kafa hidimar haikalin Ubangiji.
Ua nui loa no hoi na mohaikuni me ka momona o na mohai aloha, a me na mohai inu, no kela mohaikuni, keia mohaikuni. Pela i hooponoponoia'i na oihana o ka hale o Iehova.
36 Hezekiya da dukan mutane suka yi farin ciki game da abin da Allah ya yi wa mutanensa, domin ya faru farat ɗaya.
A hauoli o Hezekia a me na kanaka a pau i ko ke Akua hoomakaukau ana i na kanaka; no ka mea, hiki wawe no ka hana.

< 2 Tarihi 29 >