< 2 Tarihi 29 >

1 Hezekiya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Abiya,’yar Zakariya.
Ézéchias devint roi à l'âge de vingt-cinq ans, et il régna vingt-neuf ans à Jérusalem. Sa mère s'appelait Abija, fille de Zacharie.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda kakansa Dawuda ya yi.
Il fit ce qui est droit aux yeux de l'Éternel, tout comme avait fait David, son père.
3 A wata na farkon a farkon shekarar mulkinsa, ya buɗe ƙofofin haikalin Ubangiji ya gyara su.
La première année de son règne, au premier mois, il ouvrit les portes de la maison de l'Éternel, et il les répara.
4 Ya kawo firistoci da Lawiyawa, ya tattara su a filin da yake a gefen gabas
Il fit venir les sacrificateurs et les Lévites, et les assembla dans la place orientale.
5 ya kuma ce musu, “Ku saurare ni, Lawiyawa! Ku tsarkake kanku yanzu, ku kuma tsarkake haikalin Ubangiji Allah na kakanninku. Ku fid da ƙazanta daga wuri mai tsarki.
Et il leur dit: Écoutez-moi, Lévites! sanctifiez-vous maintenant, et sanctifiez la maison de l'Éternel, le Dieu de vos pères, et ôtez du sanctuaire la souillure.
6 Kakanninku ba su yi aminci ba; suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnmu, suka kuma yashe shi. Suka juya fuskokinsu daga mazaunin Ubangiji suka kuma juya masa baya.
Car nos pères ont péché et fait ce qui est mauvais aux yeux de l'Éternel, notre Dieu; ils l'ont abandonné, ils ont détourné leurs faces de la demeure de l'Éternel et lui ont tourné le dos.
7 Suka kulle ƙofofin shirayi, suka kuma kashe fitilu. Ba su ƙone turare ko su miƙa hadayun ƙonawa a wuri mai tsarki ga Allah na Isra’ila ba.
Ils ont même fermé les portes du portique, et ont éteint les lampes, et ils n'ont point fait fumer le parfum, et ils n'ont point offert l'holocauste au Dieu d'Israël dans le sanctuaire.
8 Saboda haka, fushin Ubangiji ya fāɗo a kan Yahuda da Urushalima; ya mai da su abin tsoro da abin banrazana da kuma abin ba’a, kamar yadda kuke gani da idanunku.
C'est pourquoi le courroux de l'Éternel a été sur Juda et sur Jérusalem; et il les a livrés au trouble, à la désolation, à la moquerie, comme vous le voyez de vos yeux.
9 Abin da ya sa ke nan kakanninmu suka fāɗi ta takobi, kuma shi ya sa aka kai’ya’yanmu maza da’ya’yanmu mata da matanmu bauta.
Et voici, à cause de cela, nos pères sont tombés par l'épée, et nos fils, nos filles et nos femmes sont en captivité.
10 Yanzu ina niyya in yi alkawari da Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin fushinsa yă kauce daga gare mu.
Maintenant donc j'ai l'intention de traiter alliance avec l'Éternel, le Dieu d'Israël, pour que l'ardeur de sa colère se détourne de nous.
11 ’Ya’yana maza, kada ku yi sakaci yanzu, gama Ubangiji ya zaɓe ku don ku tsaya a gabansa ku kuma yi masa hidima, don ku yi hidima a gabansa ku kuma ƙone turare.”
Or, mes enfants, ne soyez pas indifférents; car l'Éternel vous a choisis, afin que vous vous teniez devant lui pour le servir, pour être ses serviteurs, et pour lui offrir le parfum.
12 Sai waɗannan Lawiyawa suka shiga aiki, daga Kohatawa Mahat ɗan Amasai da Yowel ɗan Azariya. Daga Kabilar Merari, Kish ɗan Abdi da Azariya ɗan Yahallelel. Daga Gershonawa, Yowa ɗan Zimma da Eden ɗan Yowa.
Et les Lévites se levèrent: Machath, fils d'Amasaï, Joël, fils d'Azaria, des enfants des Kéhathites; et des enfants de Mérari, Kis, fils d'Abdi, Azaria, fils de Jéhalléléel; et des Guershonites, Joach, fils de Zimma, et Éden, fils de Joach;
13 Daga zuriyar Elizafan, Shimri da Yehiyel. Daga zuriyar Asaf, Zakariya da Mattaniya.
Et des enfants d'Élitsaphan, Shimri et Jéïel; et des enfants d'Asaph, Zacharie et Matthania;
14 Daga iyalin Heman, Yehiyel da Shimeyi. Daga zuriyar Yedutun, Shemahiya da Uzziyel.
Et des enfants d'Héman, Jéhiel et Shimeï, et des enfants de Jéduthun, Shémaja et Uzziel.
15 Da suka tattara’yan’uwansu suka kuma tsarkake kansu, sai suka shiga ciki suka tsarkake haikalin Ubangiji, kamar yadda sarki ya umarta, suna bin maganar Ubangiji.
Ils assemblèrent leurs frères, et ils se sanctifièrent; et ils entrèrent selon le commandement du roi, et suivant les paroles de l'Éternel, pour purifier la maison de l'Éternel.
16 Firistoci suka shiga cikin wuri mai tsarki na Ubangiji suka tsarkake shi. Suka fitar da dukan abin da yake marar tsabta da suka samu a haikalin Ubangiji zuwa filin haikalin Ubangiji. Lawiyawa suka ɗauke su suka kai su Kwarin Kidron.
Ainsi les sacrificateurs entrèrent dans l'intérieur de la maison de l'Éternel, pour la purifier; et ils portèrent dehors, au parvis de la maison de l'Éternel, toutes les souillures qu'ils trouvèrent dans le temple de l'Éternel; et les Lévites les reçurent pour les emporter dehors, au torrent de Cédron.
17 Suka fara tsarkakewar a rana ta farko na farkon wata, a rana ta takwas na watan kuwa suka kai shirayin Ubangiji. Karin kwana takwas kuma suka tsarkake haikalin Ubangiji kansa, suka gama a rana ta goma sha shida na farkon wata.
Ils commencèrent à sanctifier le temple, le premier jour du premier mois; le huitième jour du mois, ils entrèrent au portique de l'Éternel, et ils sanctifièrent la maison de l'Éternel pendant huit jours; le seizième jour du premier mois, ils eurent achevé.
18 Sa’an nan suka tafi wurin Sarki Hezekiya suka faɗa masa, “Mun tsarkake haikalin Ubangiji gaba ɗaya, bagaden ƙone hadaya tare da dukan kayayyakinsa, da tebur don shirya tsarkaken burodi, tare da dukan kayayyakinsa.
Après cela ils se rendirent chez le roi Ézéchias, et dirent: Nous avons purifié toute la maison de l'Éternel, l'autel des holocaustes et tous ses ustensiles, et la table des pains de proposition et tous ses ustensiles.
19 Mun shirya muka kuma tsarkake dukan kayayyakin da Sarki Ahaz ya cire cikin rashin amincinsa yayinda yake sarki. Yanzu suna a gaban bagaden Ubangiji.”
Nous avons remis en état et sanctifié tous les ustensiles que le roi Achaz avait rejetés pendant son règne, par suite de son péché; et voici, ils sont devant l'autel de l'Éternel.
20 Da sassafe kashegari Sarki Hezekiya ya tattara manyan birni wuri ɗaya, suka haura zuwa haikalin Ubangiji.
Alors le roi Ézéchias se leva de bon matin, assembla les principaux de la ville, et monta à la maison de l'Éternel.
21 Suka kawo bijimai bakwai, raguna bakwai, bunsurai bakwai da kuma awaki mata bakwai a matsayin hadaya don zunubi domin masarauta, domin wuri mai tsarki da kuma domin Yahuda. Sarki ya umarce firistoci, zuriyar Haruna, su miƙa waɗannan a bagaden Ubangiji.
Et ils amenèrent sept taureaux, sept béliers, sept agneaux et sept boucs, destinés à des sacrifices pour le péché, pour le royaume, pour le sanctuaire et pour Juda. Puis le roi dit aux sacrificateurs, fils d'Aaron, qu'ils les offrissent sur l'autel de l'Éternel.
22 Saboda haka suka yayyanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin suka yayyafa a kan bagade. Suka kuma yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagaden. Haka kuma suka yanka’yan ragunan suka yayyafa jinin a bagaden.
Ils égorgèrent donc les bœufs, et les sacrificateurs en reçurent le sang, et le répandirent sur l'autel; ils égorgèrent les béliers, et en répandirent le sang sur l'autel; ils égorgèrent les agneaux, et en répandirent le sang sur l'autel.
23 Aka kawo awaki domin hadaya don zunubi a gaban sarki da taron, suka kuwa ɗibiya hannuwansu a kansu.
Puis on fit approcher les boucs du sacrifice pour le péché, devant le roi et devant l'assemblée, et ils posèrent leurs mains sur eux;
24 Sa’an nan firistoci suka yayyanka awakin suka miƙa jininsu a bagade domin hadaya don zunubi don kafara saboda dukan Isra’ila, domin sarki ya umarta a yi hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi domin dukan Isra’ila.
Et les sacrificateurs les égorgèrent, et offrirent en expiation leur sang sur l'autel, pour faire l'expiation pour tout Israël; car le roi avait ordonné l'holocauste et le sacrifice pour le péché, pour tout Israël.
25 Sarki Hezekiya ya ajiye Lawiyawa a cikin haikalin Ubangiji tare da ganguna, garayu da molaye, yadda Dawuda da Gad mai duba na sarki da kuma annabi Natan suka tsara. Ubangiji ne ya umarta wannan ta wurin annabawansa.
Il fit aussi tenir les Lévites dans la maison de l'Éternel, avec des cymbales, des lyres et des harpes, selon le commandement de David et de Gad, le Voyant du roi, et de Nathan, le prophète; car c'était un commandement de l'Éternel, par ses prophètes.
26 Saboda haka Lawiyawa suka tsaya a shirye tare da kayan kiɗin Dawuda, firistoci kuma tare da ƙahoninsu.
Les Lévites se tinrent donc là avec les instruments de David, et les sacrificateurs avec les trompettes.
27 Hezekiya ya ba da umarni a miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagade. Yayinda aka fara miƙawa, ana rerawa ga Ubangiji, tare da bushe-bushe da kiɗe-kiɗen kayan waƙa na Dawuda sarkin Isra’ila.
Alors Ézéchias commanda qu'on offrît l'holocauste sur l'autel; et au moment où commença l'holocauste, commença aussi le cantique de l'Éternel, avec les trompettes et l'accompagnement des instruments de David, roi d'Israël.
28 Dukan taron suka durƙusa suka yi sujada, yayinda mawaƙa suke rerawa, ana kuma busa ƙahoni, dukan wannan ya ci gaba sai da aka gama miƙa hadaya ta ƙonawa.
Et toute l'assemblée se prosterna, le chant retentit, et les trompettes sonnèrent; le tout jusqu'à ce qu'on eût achevé l'holocauste.
29 Sa’ad da aka gama miƙawa, sai sarki da mutanen da suke tare da shi suka durƙusa suka yi sujada.
Et quand on eut achevé d'offrir l'holocauste, le roi et tous ceux qui se trouvaient avec lui fléchirent les genoux et se prosternèrent.
30 Sarki Hezekiya da fadawansa suka umarci Lawiyawa su yabi Ubangiji da kalmomin Dawuda da na Asaf mai duba. Saboda haka suka rera yabai da murna, suka sunkuyar da kawunansu suka yi sujada.
Puis le roi Ézéchias et les chefs dirent aux Lévites de louer l'Éternel avec les paroles de David et d'Asaph, le Voyant; et ils le louèrent avec des transports de joie, et ils s'inclinèrent et se prosternèrent.
31 Sa’an nan Hezekiya ya ce, “Yanzu kun keɓe kanku ga Ubangiji. Ku zo ku kuma kawo hadayu da hadayun godiya zuwa ga haikalin Ubangiji.” Saboda haka taron suka kawo hadayu da hadayun godiya, da kuma dukan waɗanda suke da niyya suka kawo hadayun ƙonawa.
Alors Ézéchias prit la parole, et dit: Vous avez maintenant consacré vos mains à l'Éternel; approchez-vous, amenez des sacrifices, et offrez des louanges dans la maison de l'Éternel. Et l'assemblée amena des sacrifices et offrit des louanges, et tous ceux qui étaient de bonne volonté offrirent des holocaustes.
32 Yawan hadayun ƙonawan da taron suka kawo, bijimai saba’in ne, raguna ɗari da kuma bunsurai ɗari biyu, dukansu kuwa domin hadayun ƙonawa ga Ubangiji ne.
Le nombre des holocaustes que l'assemblée offrit, fut de soixante et dix taureaux, cent béliers, deux cents agneaux, le tout en holocauste à l'Éternel.
33 Dabbobin da aka tsarkake a matsayi hadayu sun kai bijimai ɗari shida da tumaki da kuma awaki dubu uku.
Six cents bœufs et trois mille brebis furent en outre consacrés.
34 Firistoci fa, suka kāsa sosai don fiɗan dukan dabbobin da za a miƙa don hadayun ƙonawa; saboda haka’yan’uwansu Lawiyawa suka taimake su har aka gama aiki kafin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. Gama Lawiyawa sun fi firistoci himma wajen tsarkakewar kansu.
Mais les sacrificateurs étaient en petit nombre, et ils ne purent pas dépouiller tous les holocaustes; les Lévites, leurs frères, les aidèrent, jusqu'à ce que l'ouvrage fût achevé, et jusqu'à ce que les autres sacrificateurs se fussent sanctifiés; car les Lévites eurent le cœur plus droit pour se sanctifier, que les sacrificateurs.
35 Aka kasance da hadayun ƙonawa a yalwace, tare da kitsen hadayun salama da hadayun sha da suke tafe da hadayun ƙonawa. Saboda haka aka sāke kafa hidimar haikalin Ubangiji.
Il y eut aussi un grand nombre d'holocaustes, avec les graisses des sacrifices de prospérités, et avec les libations des holocaustes. Ainsi le service de la maison de l'Éternel fut rétabli.
36 Hezekiya da dukan mutane suka yi farin ciki game da abin da Allah ya yi wa mutanensa, domin ya faru farat ɗaya.
Et Ézéchias et tout le peuple se réjouirent de ce que Dieu avait ainsi disposé le peuple; car la chose se fit subitement.

< 2 Tarihi 29 >