< 2 Tarihi 29 >
1 Hezekiya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Abiya,’yar Zakariya.
Ezéchias avait vingt-cinq ans lorsqu'il monta sur le trône, et il régna vingt-neuf ans à Jérusalem; sa mère s'appelait Abia, fille de Zacharie.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda kakansa Dawuda ya yi.
Et il fit ce qui est droit devant le Seigneur, se conformant à tout ce qu'avait fait David, son aïeul.
3 A wata na farkon a farkon shekarar mulkinsa, ya buɗe ƙofofin haikalin Ubangiji ya gyara su.
Dès qu'il fut affermi dans son royaume, le premier mois, il ouvrit les portes du temple du Seigneur, et il les restaura.
4 Ya kawo firistoci da Lawiyawa, ya tattara su a filin da yake a gefen gabas
Et il introduisit dans le temple les prêtres et les lévites, et il les réunit dans l'aile orientale de l'édifice.
5 ya kuma ce musu, “Ku saurare ni, Lawiyawa! Ku tsarkake kanku yanzu, ku kuma tsarkake haikalin Ubangiji Allah na kakanninku. Ku fid da ƙazanta daga wuri mai tsarki.
Et il leur dit: Écoutez, lévites, purifiez-vous d'abord; puis, vous purifierez le temple du Dieu de vos pères, et vous rejetterez toute impureté du lien saint.
6 Kakanninku ba su yi aminci ba; suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnmu, suka kuma yashe shi. Suka juya fuskokinsu daga mazaunin Ubangiji suka kuma juya masa baya.
Car VOS père se sont pervertis et ils ont fait le mal devant le Seigneur notre Dieu; ils l'ont abandonné, ils ont détourné leur face du tabernacle du Seigneur, et s'en sont éloignés.
7 Suka kulle ƙofofin shirayi, suka kuma kashe fitilu. Ba su ƙone turare ko su miƙa hadayun ƙonawa a wuri mai tsarki ga Allah na Isra’ila ba.
Ils ont fermé les portes du temple, ils ont éteint les lampes, ils n'ont plus brûlé d'encens, ils ont cessé d'offrir des holocaustes dans le lieu saint du Dieu d'Israël.
8 Saboda haka, fushin Ubangiji ya fāɗo a kan Yahuda da Urushalima; ya mai da su abin tsoro da abin banrazana da kuma abin ba’a, kamar yadda kuke gani da idanunku.
Alors, le Seigneur s'est vivement irrité contre Juda et contre Jérusalem; il les a livrés au trouble, à l'extermination et aux railleries, comme vous l'avez vu de vos yeux.
9 Abin da ya sa ke nan kakanninmu suka fāɗi ta takobi, kuma shi ya sa aka kai’ya’yanmu maza da’ya’yanmu mata da matanmu bauta.
Vos pères ont été frappés par le glaive; vos fils, vos filles et vos femmes, ont été emmenés captifs en une contrée étrangère, où ils sont encore.
10 Yanzu ina niyya in yi alkawari da Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin fushinsa yă kauce daga gare mu.
A cause de cela, il est maintenant en mon cœur de faire alliance avec le Seigneur Dieu d'Israël, et il détournera de nous sa terrible colère.
11 ’Ya’yana maza, kada ku yi sakaci yanzu, gama Ubangiji ya zaɓe ku don ku tsaya a gabansa ku kuma yi masa hidima, don ku yi hidima a gabansa ku kuma ƙone turare.”
Ne différez pas, car le Seigneur vous a choisis pour que vous vous teniez en sa présence, pour que vous le serviez et que vous brûliez devant lui de l'encens.
12 Sai waɗannan Lawiyawa suka shiga aiki, daga Kohatawa Mahat ɗan Amasai da Yowel ɗan Azariya. Daga Kabilar Merari, Kish ɗan Abdi da Azariya ɗan Yahallelel. Daga Gershonawa, Yowa ɗan Zimma da Eden ɗan Yowa.
Et les lévites se levèrent, savoir: Des fils de Caath, Maath, fils d'Amasi, et Johel, fils d'Azarias; des fils de Mérari: Cis, fils d'Abdi, et Azarias, fils d'Ilaélel; des fils de Gerson: Jodaad, fils de Zemmath, et Joadam; ceux-ci descendaient de Joacha;
13 Daga zuriyar Elizafan, Shimri da Yehiyel. Daga zuriyar Asaf, Zakariya da Mattaniya.
Des fils d'Elisaphan: Zambri et Jehiel; des fils d'Asaph: Zacharie et Matlhanias;
14 Daga iyalin Heman, Yehiyel da Shimeyi. Daga zuriyar Yedutun, Shemahiya da Uzziyel.
Des fils d'Hêman: Jehiel et Sémeï; des fils d'Idithun: Samaias et Oziel.
15 Da suka tattara’yan’uwansu suka kuma tsarkake kansu, sai suka shiga ciki suka tsarkake haikalin Ubangiji, kamar yadda sarki ya umarta, suna bin maganar Ubangiji.
Et ils réunirent leurs frères, et ils se purifièrent selon l'ordre du roi, pour purifier ensuite le peuple du Seigneur, comme lui-même l'avait prescrit.
16 Firistoci suka shiga cikin wuri mai tsarki na Ubangiji suka tsarkake shi. Suka fitar da dukan abin da yake marar tsabta da suka samu a haikalin Ubangiji zuwa filin haikalin Ubangiji. Lawiyawa suka ɗauke su suka kai su Kwarin Kidron.
Et les prêtres entrèrent dans le temple du Seigneur pour le purifier, et ils rejetèrent toute impureté qu'ils trouvèrent dans le temple et dans le parvis; puis, les lévites prirent les choses impures pour les porter au torrent de Cédron.
17 Suka fara tsarkakewar a rana ta farko na farkon wata, a rana ta takwas na watan kuwa suka kai shirayin Ubangiji. Karin kwana takwas kuma suka tsarkake haikalin Ubangiji kansa, suka gama a rana ta goma sha shida na farkon wata.
La purification commença le premier jour du premier mois, pendant la nouvelle lune, et, le huitième jour, ils entrèrent dans le temple du Seigneur, et ils le purifièrent en huit jours; le seizième jour du premier mois, tout était terminé.
18 Sa’an nan suka tafi wurin Sarki Hezekiya suka faɗa masa, “Mun tsarkake haikalin Ubangiji gaba ɗaya, bagaden ƙone hadaya tare da dukan kayayyakinsa, da tebur don shirya tsarkaken burodi, tare da dukan kayayyakinsa.
Et ils allèrent trouver le roi Ezéchias, et ils lui dirent: Nous avons tout purifié dans le temple du Seigneur: l'autel des holocaustes et ses ustensiles, la table de proposition et ses accessoires.
19 Mun shirya muka kuma tsarkake dukan kayayyakin da Sarki Ahaz ya cire cikin rashin amincinsa yayinda yake sarki. Yanzu suna a gaban bagaden Ubangiji.”
Tous les objets que le roi Achaz avait souillés pendant son règne et son apostasie, nous les avons purifiés 'et mis en ordre; voilà que tout est exposé devant l'autel du Seigneur.
20 Da sassafe kashegari Sarki Hezekiya ya tattara manyan birni wuri ɗaya, suka haura zuwa haikalin Ubangiji.
Et le roi Ezéchias se leva de grand matin, et il assembla tous les chefs de la ville, et il monta au temple du Seigneur.
21 Suka kawo bijimai bakwai, raguna bakwai, bunsurai bakwai da kuma awaki mata bakwai a matsayin hadaya don zunubi domin masarauta, domin wuri mai tsarki da kuma domin Yahuda. Sarki ya umarce firistoci, zuriyar Haruna, su miƙa waɗannan a bagaden Ubangiji.
Et il offrit sept bœufs, sept béliers, sept agneaux et sept boucs, pour les péchés, pour le royaume, pour les saints et pour Israël; et il dit aux prêtres, fils d'Aaron, de monter à l'autel du Seigneur.
22 Saboda haka suka yayyanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin suka yayyafa a kan bagade. Suka kuma yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagaden. Haka kuma suka yanka’yan ragunan suka yayyafa jinin a bagaden.
Et ils immolèrent les bœufs, et ils recueillirent le sang, et ils le répandirent sur l'autel; et ils immolèrent les béliers, et ils répandirent le sang sur l'autel; et ils immolèrent les agneaux, et ils répandirent le sang sur l'autel.
23 Aka kawo awaki domin hadaya don zunubi a gaban sarki da taron, suka kuwa ɗibiya hannuwansu a kansu.
Et ils traînèrent devant le roi et devant l'assemblée entière les boucs pour les péchés, et ils imposèrent sur eux les mains;
24 Sa’an nan firistoci suka yayyanka awakin suka miƙa jininsu a bagade domin hadaya don zunubi don kafara saboda dukan Isra’ila, domin sarki ya umarta a yi hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi domin dukan Isra’ila.
Et les prêtres les immolèrent, et ils firent l'expiation en versant leur sang devant l'autel, et ils firent l'expiation en faveur de tout Israël; car le roi avait dit: L'holocauste et le sacrifice pour les péchés sont pour tout Israël.
25 Sarki Hezekiya ya ajiye Lawiyawa a cikin haikalin Ubangiji tare da ganguna, garayu da molaye, yadda Dawuda da Gad mai duba na sarki da kuma annabi Natan suka tsara. Ubangiji ne ya umarta wannan ta wurin annabawansa.
Et il établit les lévites dans le temple du Seigneur au son des cymbales, des cithares et des harpes, comme l'avait réglé le roi David, d'accord avec Gad le voyant, et Nathan le prophète; car le Seigneur transmet ses commandements par les prophètes.
26 Saboda haka Lawiyawa suka tsaya a shirye tare da kayan kiɗin Dawuda, firistoci kuma tare da ƙahoninsu.
Les lévites furent installés au son des instruments de David, et les prêtres au son des trompettes sacrées.
27 Hezekiya ya ba da umarni a miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagade. Yayinda aka fara miƙawa, ana rerawa ga Ubangiji, tare da bushe-bushe da kiɗe-kiɗen kayan waƙa na Dawuda sarkin Isra’ila.
Ensuite, Ezéchias ordonna de porter l'holocauste sur l'autel; et, lorsque l'on commença l'offrande de l'holocauste, on commença à chanter les louanges du Seigneur, au son des trompettes et des instruments de David, roi d'Israël.
28 Dukan taron suka durƙusa suka yi sujada, yayinda mawaƙa suke rerawa, ana kuma busa ƙahoni, dukan wannan ya ci gaba sai da aka gama miƙa hadaya ta ƙonawa.
Et toute l'Église adora, et les chantres-harpistes chantèrent, et les trompettes sonnèrent jusqu'à ce que l'holocauste fût achevé.
29 Sa’ad da aka gama miƙawa, sai sarki da mutanen da suke tare da shi suka durƙusa suka yi sujada.
Et, lorsque les victimes furent consumées, le roi se prosterna, ainsi que toute l'assistance, et ils adorèrent.
30 Sarki Hezekiya da fadawansa suka umarci Lawiyawa su yabi Ubangiji da kalmomin Dawuda da na Asaf mai duba. Saboda haka suka rera yabai da murna, suka sunkuyar da kawunansu suka yi sujada.
Et le roi Ezéchias et les princes dirent aux lévites de chanter au Seigneur les psaumes tant du roi David que du prophète Asaph; ils chantèrent avec allégresse; puis, se prosternant, ils adorèrent.
31 Sa’an nan Hezekiya ya ce, “Yanzu kun keɓe kanku ga Ubangiji. Ku zo ku kuma kawo hadayu da hadayun godiya zuwa ga haikalin Ubangiji.” Saboda haka taron suka kawo hadayu da hadayun godiya, da kuma dukan waɗanda suke da niyya suka kawo hadayun ƙonawa.
Et le roi Ézéchias prit la parole, et dit: Maintenant que vous vous êtes consacrés au Seigneur, amenez et offrez les victimes de louanges dans le temple du, Seigneur; et l'Église offrit dans le temple des sacrifices et des louanges; et ceux qui avaient le cœur plein de zèle amenèrent des holocaustes.
32 Yawan hadayun ƙonawan da taron suka kawo, bijimai saba’in ne, raguna ɗari da kuma bunsurai ɗari biyu, dukansu kuwa domin hadayun ƙonawa ga Ubangiji ne.
Voici le nombre des holocaustes qu'offrit l'Église: soixante-dix bœufs, cent béliers, deux cents agneaux; tous pour les holocaustes au Seigneur.
33 Dabbobin da aka tsarkake a matsayi hadayu sun kai bijimai ɗari shida da tumaki da kuma awaki dubu uku.
Il y eut en outre: six cents bœufs consacrés, et trois mille brebis.
34 Firistoci fa, suka kāsa sosai don fiɗan dukan dabbobin da za a miƙa don hadayun ƙonawa; saboda haka’yan’uwansu Lawiyawa suka taimake su har aka gama aiki kafin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. Gama Lawiyawa sun fi firistoci himma wajen tsarkakewar kansu.
Or, les prêtres étaient en petit nombre, et ils ne suffisaient pas à enlever les peaux des victimes; leurs frères, les lévites, les aidèrent jusqu'à ce que l'œuvre fût achevée, et que les prêtres se fussent purifiés; car les lévites sont plus promptement purifiés que les prêtres.
35 Aka kasance da hadayun ƙonawa a yalwace, tare da kitsen hadayun salama da hadayun sha da suke tafe da hadayun ƙonawa. Saboda haka aka sāke kafa hidimar haikalin Ubangiji.
Il y eut donc nombre de victimes pour les holocaustes; on brûla en grande quantité la graisse des hosties pacifiques, on répandit à flots les libations de l'holocauste, et les cérémonies du temple furent rétablies.
36 Hezekiya da dukan mutane suka yi farin ciki game da abin da Allah ya yi wa mutanensa, domin ya faru farat ɗaya.
Et Ezéchias et tout le peuple ressentirent une vive allégresse de ce que Dieu avait préparé cette fête à son peuple; car la chose s'était faite soudainement.