< 2 Tarihi 29 >

1 Hezekiya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Abiya,’yar Zakariya.
And, Hezekiah, began to reign when he was twenty-five years old, and, twenty-nine years, reigned he in Jerusalem, —and, the name of his mother, was Abijah, daughter of Zechariah.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda kakansa Dawuda ya yi.
And he did that which was right in the eyes of Yahweh, —according to all that, David his father, had done.
3 A wata na farkon a farkon shekarar mulkinsa, ya buɗe ƙofofin haikalin Ubangiji ya gyara su.
He, in the first year of his reign, in the first month, opened the doors of the house of Yahweh, and repaired them.
4 Ya kawo firistoci da Lawiyawa, ya tattara su a filin da yake a gefen gabas
And he brought in the priests, and the Levites, —and gathered them together in the broadway on the east;
5 ya kuma ce musu, “Ku saurare ni, Lawiyawa! Ku tsarkake kanku yanzu, ku kuma tsarkake haikalin Ubangiji Allah na kakanninku. Ku fid da ƙazanta daga wuri mai tsarki.
and said unto them, Hear me, O Levites! Now, hallow yourselves, and hallow the house of Yahweh, God of your fathers, and take forth the impure thing out of the holy place.
6 Kakanninku ba su yi aminci ba; suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnmu, suka kuma yashe shi. Suka juya fuskokinsu daga mazaunin Ubangiji suka kuma juya masa baya.
For our fathers have acted unfaithfully and done the thing that was wicked in the eyes of Yahweh our God, and have forsaken him, -and have turned round their faces from the habitation of Yahweh, and have offered their backs.
7 Suka kulle ƙofofin shirayi, suka kuma kashe fitilu. Ba su ƙone turare ko su miƙa hadayun ƙonawa a wuri mai tsarki ga Allah na Isra’ila ba.
Moreover they have shut up the doors of the porch, and have quenched the lamps, and, incense, have they not burned, -and, ascending-sacrifice, have they not caused to go up in the holy place, unto the God of Israel.
8 Saboda haka, fushin Ubangiji ya fāɗo a kan Yahuda da Urushalima; ya mai da su abin tsoro da abin banrazana da kuma abin ba’a, kamar yadda kuke gani da idanunku.
Thus hath it come to pass, that, the wrath of Yahweh, hath been upon Judah and Jerusalem, —and he hath delivered them up as a terror and as an astonishment and as hissing, even as, ye, can see with your own eyes.
9 Abin da ya sa ke nan kakanninmu suka fāɗi ta takobi, kuma shi ya sa aka kai’ya’yanmu maza da’ya’yanmu mata da matanmu bauta.
And lo! our fathers have fallen by the sword, and, our sons and our daughters and our wives, are in captivity for this.
10 Yanzu ina niyya in yi alkawari da Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin fushinsa yă kauce daga gare mu.
Now, is it near my heart, to solemnise a covenant unto Yahweh, God of Israel, —that he may turn from him the glow of his anger.
11 ’Ya’yana maza, kada ku yi sakaci yanzu, gama Ubangiji ya zaɓe ku don ku tsaya a gabansa ku kuma yi masa hidima, don ku yi hidima a gabansa ku kuma ƙone turare.”
My sons! now, do not be faulty, —for, of you, hath Yahweh made choice, to stand before him, and to wait upon him, and to be his attendants and burners of incense.
12 Sai waɗannan Lawiyawa suka shiga aiki, daga Kohatawa Mahat ɗan Amasai da Yowel ɗan Azariya. Daga Kabilar Merari, Kish ɗan Abdi da Azariya ɗan Yahallelel. Daga Gershonawa, Yowa ɗan Zimma da Eden ɗan Yowa.
Then arose the Levites—Mahath son of Amasai, and Joel son of Azariah, of the sons of the Kohathites, and, of the sons of Merari, Kish son of Abdi, and Azariah son of Jehallelel, —and, of the Gershonites, Joah son of Zimmah, and Eden son of Joah;
13 Daga zuriyar Elizafan, Shimri da Yehiyel. Daga zuriyar Asaf, Zakariya da Mattaniya.
and, of the sons of Elizaphan, Shimri and Jeiel, —and, of the sons of Asaph, Zechariah, and Mattaniah;
14 Daga iyalin Heman, Yehiyel da Shimeyi. Daga zuriyar Yedutun, Shemahiya da Uzziyel.
and, of the sons of Heman, Jehiel and Shimei, —and, of the sons of Jeduthun, Shemaiah, and Uzziel;
15 Da suka tattara’yan’uwansu suka kuma tsarkake kansu, sai suka shiga ciki suka tsarkake haikalin Ubangiji, kamar yadda sarki ya umarta, suna bin maganar Ubangiji.
and they gathered together their brethren, who hallowed themselves, and came in according to the command of the king, in the things of Yahweh, —to purify the house of Yahweh.
16 Firistoci suka shiga cikin wuri mai tsarki na Ubangiji suka tsarkake shi. Suka fitar da dukan abin da yake marar tsabta da suka samu a haikalin Ubangiji zuwa filin haikalin Ubangiji. Lawiyawa suka ɗauke su suka kai su Kwarin Kidron.
So the priests entered into the inner part of the house of Yahweh, to make purification, and they brought out every unclean thing which they found in the temple of Yahweh, into the court of the house of Yahweh, —where the Levites received it, to carry it forth to the Kidron ravine outside.
17 Suka fara tsarkakewar a rana ta farko na farkon wata, a rana ta takwas na watan kuwa suka kai shirayin Ubangiji. Karin kwana takwas kuma suka tsarkake haikalin Ubangiji kansa, suka gama a rana ta goma sha shida na farkon wata.
And they began, on the first of the first month, to hallow, —and, on the eighth day of the month, they came to the porch of Yahweh, so they hallowed the house of Yahweh in eight days, —and, on the sixteenth day of the first month, they finished.
18 Sa’an nan suka tafi wurin Sarki Hezekiya suka faɗa masa, “Mun tsarkake haikalin Ubangiji gaba ɗaya, bagaden ƙone hadaya tare da dukan kayayyakinsa, da tebur don shirya tsarkaken burodi, tare da dukan kayayyakinsa.
Then came they in unto Hezekiah the king, and said, We have purified all the house of Yahweh, —the altar of ascending-sacrifice, and all the utensils thereof, and the table for setting in array, and all the utensils thereof.
19 Mun shirya muka kuma tsarkake dukan kayayyakin da Sarki Ahaz ya cire cikin rashin amincinsa yayinda yake sarki. Yanzu suna a gaban bagaden Ubangiji.”
And, all the utensils which King Ahaz in his reign rejected when he acted unfaithfully, have we made ready and hallowed, —and, there they are, before the altar of Yahweh.
20 Da sassafe kashegari Sarki Hezekiya ya tattara manyan birni wuri ɗaya, suka haura zuwa haikalin Ubangiji.
So Hezekiah the king rose up early, and gathered together the rulers of the city, —and went up to the house of Yahweh.
21 Suka kawo bijimai bakwai, raguna bakwai, bunsurai bakwai da kuma awaki mata bakwai a matsayin hadaya don zunubi domin masarauta, domin wuri mai tsarki da kuma domin Yahuda. Sarki ya umarce firistoci, zuriyar Haruna, su miƙa waɗannan a bagaden Ubangiji.
And they brought in seven bullocks, and seven rams, and seven young sheep, and seven he-goats for bearing sin, for the kingdom and for the sanctuary and for Judah, —and he bade the sons of Aaron, the priests, cause them to ascend upon the altar of Yahweh.
22 Saboda haka suka yayyanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin suka yayyafa a kan bagade. Suka kuma yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagaden. Haka kuma suka yanka’yan ragunan suka yayyafa jinin a bagaden.
So they slaughtered the bullocks, and the priests received the blood, and dashed it against the altar, —and they slaughtered the rams, and dashed the blood against the altar, and slaughtered the young sheep, and dashed the blood against the altar.
23 Aka kawo awaki domin hadaya don zunubi a gaban sarki da taron, suka kuwa ɗibiya hannuwansu a kansu.
And they brought near the he-goats for bearing sin, before the king, and the convocation, —and they leaned their hands upon them;
24 Sa’an nan firistoci suka yayyanka awakin suka miƙa jininsu a bagade domin hadaya don zunubi don kafara saboda dukan Isra’ila, domin sarki ya umarta a yi hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi domin dukan Isra’ila.
and the priests slaughtered them, and sin-cleansed, with their blood, the altar, to put a propitiatory-covering over all Israel, -because, for all Israel, did the king appoint the ascending-sacrifice and the offering for bearing sin.
25 Sarki Hezekiya ya ajiye Lawiyawa a cikin haikalin Ubangiji tare da ganguna, garayu da molaye, yadda Dawuda da Gad mai duba na sarki da kuma annabi Natan suka tsara. Ubangiji ne ya umarta wannan ta wurin annabawansa.
And he caused the Levites to stand in the house of Yahweh, with cymbals and with harps and with lyres, by the commandment of David, and of Gad the seer of the king, and of Nathan the prophet, —for, by the hand of Yahweh, came the commandment by the hand of his prophets.
26 Saboda haka Lawiyawa suka tsaya a shirye tare da kayan kiɗin Dawuda, firistoci kuma tare da ƙahoninsu.
So the Levites took their stand, with the instruments of David, and the priests, with the trumpets.
27 Hezekiya ya ba da umarni a miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagade. Yayinda aka fara miƙawa, ana rerawa ga Ubangiji, tare da bushe-bushe da kiɗe-kiɗen kayan waƙa na Dawuda sarkin Isra’ila.
And Hezekiah gave word, to cause the ascending-sacrifice to go up on the altar, —and, when the ascending-sacrifice began, the singing unto Yahweh began, and the trumpets, even under the direction of the instruments of David, king of Israel.
28 Dukan taron suka durƙusa suka yi sujada, yayinda mawaƙa suke rerawa, ana kuma busa ƙahoni, dukan wannan ya ci gaba sai da aka gama miƙa hadaya ta ƙonawa.
And, all the convocation, were bowing themselves in prostration, and, the song, was resounding and the trumpets were blowing, -the whole, until the completing of the ascending-sacrifice.
29 Sa’ad da aka gama miƙawa, sai sarki da mutanen da suke tare da shi suka durƙusa suka yi sujada.
And, when the offering was complete, the king knelt down and all who were present with him, and bowed themselves in prostration.
30 Sarki Hezekiya da fadawansa suka umarci Lawiyawa su yabi Ubangiji da kalmomin Dawuda da na Asaf mai duba. Saboda haka suka rera yabai da murna, suka sunkuyar da kawunansu suka yi sujada.
And Hezekiah the king and the rulers gave word to the Levites, to offer praise unto Yahweh, in the words of David, and of Asaph the seer, —so they offered praise right joyfully, and bent their heads and bowed themselves in prostration.
31 Sa’an nan Hezekiya ya ce, “Yanzu kun keɓe kanku ga Ubangiji. Ku zo ku kuma kawo hadayu da hadayun godiya zuwa ga haikalin Ubangiji.” Saboda haka taron suka kawo hadayu da hadayun godiya, da kuma dukan waɗanda suke da niyya suka kawo hadayun ƙonawa.
Then responded Hezekiah and said—Now, have ye consecrated yourselves unto Yahweh. Draw near, and bring in sacrifices and thank-offerings unto the house of Yahweh, -So the convocation brought sacrifices and thank-offerings, and, everyone of a willing heart, [brought] ascending-sacrifices.
32 Yawan hadayun ƙonawan da taron suka kawo, bijimai saba’in ne, raguna ɗari da kuma bunsurai ɗari biyu, dukansu kuwa domin hadayun ƙonawa ga Ubangiji ne.
And it came to pass that, the number of ascending-sacrifices which the convocation brought, was—seventy bullocks, and a hundred rams, and two hundred young sheep, —as an ascending-sacrifice unto Yahweh, all these.
33 Dabbobin da aka tsarkake a matsayi hadayu sun kai bijimai ɗari shida da tumaki da kuma awaki dubu uku.
But, the hallowed beasts, were six hundred bullocks, and three thousand sheep.
34 Firistoci fa, suka kāsa sosai don fiɗan dukan dabbobin da za a miƙa don hadayun ƙonawa; saboda haka’yan’uwansu Lawiyawa suka taimake su har aka gama aiki kafin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. Gama Lawiyawa sun fi firistoci himma wajen tsarkakewar kansu.
Only, the priests, were too few, and were unable to flay all the ascending-sacrifices, —so their brethren the Levites strengthened them, until the work was complete and until the priests had hallowed themselves, for, the Levites, were more upright in heart to hallow themselves, than the priests.
35 Aka kasance da hadayun ƙonawa a yalwace, tare da kitsen hadayun salama da hadayun sha da suke tafe da hadayun ƙonawa. Saboda haka aka sāke kafa hidimar haikalin Ubangiji.
Moreover also, the ascending-sacrifices, were in abundance, with the fat portions of the peace-offerings, and with the drink-offerings to every ascending-sacrifice, -thus was established the service of the house of Yahweh.
36 Hezekiya da dukan mutane suka yi farin ciki game da abin da Allah ya yi wa mutanensa, domin ya faru farat ɗaya.
And Hezekiah rejoiced, and all the people, because God had established it for the people, —for, suddenly, had the thing come about.

< 2 Tarihi 29 >