< 2 Tarihi 29 >
1 Hezekiya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Abiya,’yar Zakariya.
Hezekiah became king when five and twenty years old, and twenty and nine years did he reign in Jerusalem. And his mother's name was Abiyah, the daughter of Zecharyahu.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda kakansa Dawuda ya yi.
And he did what is right in the eyes of the Lord, in accordance with all that David his father had done.
3 A wata na farkon a farkon shekarar mulkinsa, ya buɗe ƙofofin haikalin Ubangiji ya gyara su.
He it was that in the first year of his reign, in the first month, opened the doors of the house of the Lord, and repaired them.
4 Ya kawo firistoci da Lawiyawa, ya tattara su a filin da yake a gefen gabas
And he brought in the priests and the Levites, and gathered them together into the open place at the east;
5 ya kuma ce musu, “Ku saurare ni, Lawiyawa! Ku tsarkake kanku yanzu, ku kuma tsarkake haikalin Ubangiji Allah na kakanninku. Ku fid da ƙazanta daga wuri mai tsarki.
And he said unto them, Hear me, ye Levites, sanctify yourselves now, and sanctity the house of the Lord the God of your fathers, and carry forth the unclean thing out of the sanctuary.
6 Kakanninku ba su yi aminci ba; suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnmu, suka kuma yashe shi. Suka juya fuskokinsu daga mazaunin Ubangiji suka kuma juya masa baya.
For our fathers have dealt faithlessly, and have done what is evil in the eyes of the Lord our God, and have forsaken him; and they have turned away their faces from the habitation of the Lord, and turned their backs.
7 Suka kulle ƙofofin shirayi, suka kuma kashe fitilu. Ba su ƙone turare ko su miƙa hadayun ƙonawa a wuri mai tsarki ga Allah na Isra’ila ba.
They had also locked up the doors of the porch, and put out the lamps, and incense have they not burnt, and the burnt-offerings have they not offered in the sanctuary, unto the God of Israel.
8 Saboda haka, fushin Ubangiji ya fāɗo a kan Yahuda da Urushalima; ya mai da su abin tsoro da abin banrazana da kuma abin ba’a, kamar yadda kuke gani da idanunku.
Wherefore the wrath of the Lord is upon Judah and Jerusalem. and he hath rendered them to be a horror, an astonishment, and a hissing, as ye see with your eyes.
9 Abin da ya sa ke nan kakanninmu suka fāɗi ta takobi, kuma shi ya sa aka kai’ya’yanmu maza da’ya’yanmu mata da matanmu bauta.
And, lo, our fathers have fallen by the sword, and our sons, and our daughters, and our wives are in captivity because of this.
10 Yanzu ina niyya in yi alkawari da Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin fushinsa yă kauce daga gare mu.
Now it is in my heart to make a covenant for the Lord the God of Israel, that his fierce wrath may turn away from us.
11 ’Ya’yana maza, kada ku yi sakaci yanzu, gama Ubangiji ya zaɓe ku don ku tsaya a gabansa ku kuma yi masa hidima, don ku yi hidima a gabansa ku kuma ƙone turare.”
My sons, be not negligent now; for of you hath the Lord made choice to stand before him, to minister unto him, and that ye might be unto him ministers and those that burn incense.
12 Sai waɗannan Lawiyawa suka shiga aiki, daga Kohatawa Mahat ɗan Amasai da Yowel ɗan Azariya. Daga Kabilar Merari, Kish ɗan Abdi da Azariya ɗan Yahallelel. Daga Gershonawa, Yowa ɗan Zimma da Eden ɗan Yowa.
Then arose the Levites, Machath the son of 'Amassai, and Joel the son of 'Azaryahu, of the sons of the Kehathites; and of the sons of Merari, Kish the son of 'Abdi, and 'Azaryahu the son of Jehallelel; and of the Gershunites, Joach the son of Zimmah, and 'Eden the son of Joach:
13 Daga zuriyar Elizafan, Shimri da Yehiyel. Daga zuriyar Asaf, Zakariya da Mattaniya.
And of the sons of Elizaphan, Shimri, and Je'iel; and of the sons of Assaph, Zecharyahu and Matthanyahu;
14 Daga iyalin Heman, Yehiyel da Shimeyi. Daga zuriyar Yedutun, Shemahiya da Uzziyel.
And of the sons of Heman, Jechiel and Shim'i; and of the sons of Jeduthun, Shema'yah and 'Uzziel;
15 Da suka tattara’yan’uwansu suka kuma tsarkake kansu, sai suka shiga ciki suka tsarkake haikalin Ubangiji, kamar yadda sarki ya umarta, suna bin maganar Ubangiji.
And they gathered together their brethren, and they sanctified themselves, and came, according to the command of the king, by the words of the Lord, to cleanse the house of the Lord.
16 Firistoci suka shiga cikin wuri mai tsarki na Ubangiji suka tsarkake shi. Suka fitar da dukan abin da yake marar tsabta da suka samu a haikalin Ubangiji zuwa filin haikalin Ubangiji. Lawiyawa suka ɗauke su suka kai su Kwarin Kidron.
And the priests went into the inner part of the house of the Lord, to cleanse it; and they brought out every thing unclean which they found in the temple of the Lord into the court of the house of the Lord; and the Levites received it, to carry it out abroad unto the brook Kidron.
17 Suka fara tsarkakewar a rana ta farko na farkon wata, a rana ta takwas na watan kuwa suka kai shirayin Ubangiji. Karin kwana takwas kuma suka tsarkake haikalin Ubangiji kansa, suka gama a rana ta goma sha shida na farkon wata.
And they commenced on the first day of the first month to sanctify; and on the eighth day of the month they came to the porch of the Lord, and they sanctified the house of the Lord in eight days; and on the sixteenth day of the first month they made an end.
18 Sa’an nan suka tafi wurin Sarki Hezekiya suka faɗa masa, “Mun tsarkake haikalin Ubangiji gaba ɗaya, bagaden ƙone hadaya tare da dukan kayayyakinsa, da tebur don shirya tsarkaken burodi, tare da dukan kayayyakinsa.
Then went they in the inner part [of the palace] to king Hezekiah, and said, We have cleansed all the house of the Lord, and the altar of burnt-offering, and all its vessels, and the table of shewbread, and all its vessels.
19 Mun shirya muka kuma tsarkake dukan kayayyakin da Sarki Ahaz ya cire cikin rashin amincinsa yayinda yake sarki. Yanzu suna a gaban bagaden Ubangiji.”
Moreover all the vessels, which king Achaz had cast aside during his reign in his faithlessness, have we put in order and sanctified: and, behold, they are before the altar of the Lord.
20 Da sassafe kashegari Sarki Hezekiya ya tattara manyan birni wuri ɗaya, suka haura zuwa haikalin Ubangiji.
Then arose king Hezekiah early, and gathered together the princes of the city, and went up to the house of the Lord.
21 Suka kawo bijimai bakwai, raguna bakwai, bunsurai bakwai da kuma awaki mata bakwai a matsayin hadaya don zunubi domin masarauta, domin wuri mai tsarki da kuma domin Yahuda. Sarki ya umarce firistoci, zuriyar Haruna, su miƙa waɗannan a bagaden Ubangiji.
And they brought seven bullocks, and seven rams, and seven sheep, and seven he-goats, as a sin-offering for the kingdom, and for the sanctuary, and for Judah. And he ordered the sons of Aaron the priests to offer [them] on the altar of the Lord.
22 Saboda haka suka yayyanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin suka yayyafa a kan bagade. Suka kuma yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagaden. Haka kuma suka yanka’yan ragunan suka yayyafa jinin a bagaden.
So they slaughtered the bullocks, and the priests received the blood, and sprinkled it on the altar; and they slaughtered the rams, and they sprinkled the blood upon the altar; they also slaughtered the sheep, and they sprinkled the blood upon the altar.
23 Aka kawo awaki domin hadaya don zunubi a gaban sarki da taron, suka kuwa ɗibiya hannuwansu a kansu.
And they brought near the he-goats of the sin-offering before the king and the congregation; and they laid their hands upon them:
24 Sa’an nan firistoci suka yayyanka awakin suka miƙa jininsu a bagade domin hadaya don zunubi don kafara saboda dukan Isra’ila, domin sarki ya umarta a yi hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi domin dukan Isra’ila.
And the priests slaughtered them, and they made an expiation with their blood upon the altar, to make an atonement for all Israel; because for all the people, said the king, should be the burnt-offering and the sin-offering.
25 Sarki Hezekiya ya ajiye Lawiyawa a cikin haikalin Ubangiji tare da ganguna, garayu da molaye, yadda Dawuda da Gad mai duba na sarki da kuma annabi Natan suka tsara. Ubangiji ne ya umarta wannan ta wurin annabawansa.
And he stationed the Levites in the house of the Lord with cymbals, with psalteries, and with harps, according to the command of David, and of Gad the king's seer, and Nathan the prophet: because from the Lord was this commandment by means of his prophets.
26 Saboda haka Lawiyawa suka tsaya a shirye tare da kayan kiɗin Dawuda, firistoci kuma tare da ƙahoninsu.
And the Levites stood with the instruments of David, and the priests with the trumpets.
27 Hezekiya ya ba da umarni a miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagade. Yayinda aka fara miƙawa, ana rerawa ga Ubangiji, tare da bushe-bushe da kiɗe-kiɗen kayan waƙa na Dawuda sarkin Isra’ila.
And Hezekiah ordered to offer the burnt-offering on the altar. And when the burnt-offering began, the song of the Lord began [also] with the trumpets, and with the instruments of David the king of Israel.
28 Dukan taron suka durƙusa suka yi sujada, yayinda mawaƙa suke rerawa, ana kuma busa ƙahoni, dukan wannan ya ci gaba sai da aka gama miƙa hadaya ta ƙonawa.
And all the assembly prostrated themselves, and the song sounded, and the trumpeters blew; all this [continued] until the burnt-offering was completed.
29 Sa’ad da aka gama miƙawa, sai sarki da mutanen da suke tare da shi suka durƙusa suka yi sujada.
And when they had made an end of offering, the king and all that were present with him kneeled down and prostrated themselves.
30 Sarki Hezekiya da fadawansa suka umarci Lawiyawa su yabi Ubangiji da kalmomin Dawuda da na Asaf mai duba. Saboda haka suka rera yabai da murna, suka sunkuyar da kawunansu suka yi sujada.
And king Hezekiah and the princes then said to the Levites to sing praises unto the Lord with the words of David, and of Assaph the seer. And they sang praises with great joy, and they bowed their heads and prostrated themselves.
31 Sa’an nan Hezekiya ya ce, “Yanzu kun keɓe kanku ga Ubangiji. Ku zo ku kuma kawo hadayu da hadayun godiya zuwa ga haikalin Ubangiji.” Saboda haka taron suka kawo hadayu da hadayun godiya, da kuma dukan waɗanda suke da niyya suka kawo hadayun ƙonawa.
Then commenced Hezekiah, and said, Now have ye consecrated yourselves unto the Lord: come near and bring sacrifices and thanksgiving-offerings unto the house of the Lord. And the assembly brought in sacrifices and thanksgiving-offerings, and every one who was liberal of heart, burnt-offerings.
32 Yawan hadayun ƙonawan da taron suka kawo, bijimai saba’in ne, raguna ɗari da kuma bunsurai ɗari biyu, dukansu kuwa domin hadayun ƙonawa ga Ubangiji ne.
And the number of the burnt-offerings, which the assembly brought, was seventy bullocks, one hundred rams, [and] two hundred sheep: as a burnt-offering unto the Lord were all these.
33 Dabbobin da aka tsarkake a matsayi hadayu sun kai bijimai ɗari shida da tumaki da kuma awaki dubu uku.
And the hallowed sacrifices were six hundred oxen and three thousand sheep.
34 Firistoci fa, suka kāsa sosai don fiɗan dukan dabbobin da za a miƙa don hadayun ƙonawa; saboda haka’yan’uwansu Lawiyawa suka taimake su har aka gama aiki kafin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. Gama Lawiyawa sun fi firistoci himma wajen tsarkakewar kansu.
Only the priests were too few, so that they could not flay all the burnt-offerings: wherefore their brethren the Levites assisted them, till the work was ended, and until the other priests could sanctify themselves, for the Levites were of upright heart to sanctify themselves more than the priests.
35 Aka kasance da hadayun ƙonawa a yalwace, tare da kitsen hadayun salama da hadayun sha da suke tafe da hadayun ƙonawa. Saboda haka aka sāke kafa hidimar haikalin Ubangiji.
But there were also burnt-offerings in abundance, with the fat of the peace-offerings, and the drink-offerings for the burnt-offerings. So was [again] established the service of the house of the Lord.
36 Hezekiya da dukan mutane suka yi farin ciki game da abin da Allah ya yi wa mutanensa, domin ya faru farat ɗaya.
And Hezekiah rejoiced, with all the people, over that which God had prepared for the people; because the thing occurred suddenly.