< 2 Tarihi 29 >

1 Hezekiya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Abiya,’yar Zakariya.
Hezekiah began to reign being twenty-five years old; and he reigned twenty-nine years in Jerusalem; and his mother's name was Abijah, daughter of Zechariah.
2 Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, kamar dai yadda kakansa Dawuda ya yi.
And he did what was right in the sight of Jehovah, according to all that David his father had done.
3 A wata na farkon a farkon shekarar mulkinsa, ya buɗe ƙofofin haikalin Ubangiji ya gyara su.
He, in the first year of his reign, in the first month, opened the doors of the house of Jehovah, and repaired them.
4 Ya kawo firistoci da Lawiyawa, ya tattara su a filin da yake a gefen gabas
And he brought in the priests and the Levites, and gathered them into the open place eastward;
5 ya kuma ce musu, “Ku saurare ni, Lawiyawa! Ku tsarkake kanku yanzu, ku kuma tsarkake haikalin Ubangiji Allah na kakanninku. Ku fid da ƙazanta daga wuri mai tsarki.
and he said to them, Hear me, ye Levites: hallow yourselves now, and hallow the house of Jehovah the God of your fathers, and carry forth the filthiness out of the sanctuary.
6 Kakanninku ba su yi aminci ba; suka aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnmu, suka kuma yashe shi. Suka juya fuskokinsu daga mazaunin Ubangiji suka kuma juya masa baya.
For our fathers have transgressed, and done evil in the sight of Jehovah our God, and have forsaken him and turned away their faces from the habitation of Jehovah, and have turned their backs.
7 Suka kulle ƙofofin shirayi, suka kuma kashe fitilu. Ba su ƙone turare ko su miƙa hadayun ƙonawa a wuri mai tsarki ga Allah na Isra’ila ba.
Also they have shut up the doors of the porch, and put out the lamps, and have not burned incense nor offered up burnt-offerings in the sanctuary to the God of Israel.
8 Saboda haka, fushin Ubangiji ya fāɗo a kan Yahuda da Urushalima; ya mai da su abin tsoro da abin banrazana da kuma abin ba’a, kamar yadda kuke gani da idanunku.
Therefore the wrath of Jehovah has been upon Judah and Jerusalem, and he has delivered them to vexation, to desolation, and to hissing, as ye see with your eyes.
9 Abin da ya sa ke nan kakanninmu suka fāɗi ta takobi, kuma shi ya sa aka kai’ya’yanmu maza da’ya’yanmu mata da matanmu bauta.
And behold, our fathers have fallen by the sword, and our sons and our daughters and our wives are in captivity for this.
10 Yanzu ina niyya in yi alkawari da Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin fushinsa yă kauce daga gare mu.
Now it is in my heart to make a covenant with Jehovah the God of Israel, that his fierce anger may turn away from us.
11 ’Ya’yana maza, kada ku yi sakaci yanzu, gama Ubangiji ya zaɓe ku don ku tsaya a gabansa ku kuma yi masa hidima, don ku yi hidima a gabansa ku kuma ƙone turare.”
My sons, be not now negligent; for Jehovah has chosen you to stand before him, to do service unto him, and to be his ministers and incense-burners.
12 Sai waɗannan Lawiyawa suka shiga aiki, daga Kohatawa Mahat ɗan Amasai da Yowel ɗan Azariya. Daga Kabilar Merari, Kish ɗan Abdi da Azariya ɗan Yahallelel. Daga Gershonawa, Yowa ɗan Zimma da Eden ɗan Yowa.
Then the Levites rose up, Mahath the son of Amasai, and Joel the son of Azariah, of the sons of the Kohathites; and of the sons of Merari, Kish the son of Abdi, and Azariah the son of Jehalleleel; and of the Gershonites, Joah the son of Zimmah, and Eden the son of Joah;
13 Daga zuriyar Elizafan, Shimri da Yehiyel. Daga zuriyar Asaf, Zakariya da Mattaniya.
and of the sons of Elizaphan, Shimri and Jeiel; and of the sons of Asaph, Zechariah and Mattaniah;
14 Daga iyalin Heman, Yehiyel da Shimeyi. Daga zuriyar Yedutun, Shemahiya da Uzziyel.
and of the sons of Heman, Jehiel and Shimei; and of the sons of Jeduthun, Shemaiah and Uzziel.
15 Da suka tattara’yan’uwansu suka kuma tsarkake kansu, sai suka shiga ciki suka tsarkake haikalin Ubangiji, kamar yadda sarki ya umarta, suna bin maganar Ubangiji.
And they gathered their brethren, and hallowed themselves, and came, according to the commandment of the king by the words of Jehovah, to cleanse the house of Jehovah.
16 Firistoci suka shiga cikin wuri mai tsarki na Ubangiji suka tsarkake shi. Suka fitar da dukan abin da yake marar tsabta da suka samu a haikalin Ubangiji zuwa filin haikalin Ubangiji. Lawiyawa suka ɗauke su suka kai su Kwarin Kidron.
And the priests went into the inner part of the house of Jehovah to cleanse it, and carried forth all the uncleanness that they found in the temple of Jehovah, into the court of the house of Jehovah. And the Levites took it to carry it forth into the brook Kidron.
17 Suka fara tsarkakewar a rana ta farko na farkon wata, a rana ta takwas na watan kuwa suka kai shirayin Ubangiji. Karin kwana takwas kuma suka tsarkake haikalin Ubangiji kansa, suka gama a rana ta goma sha shida na farkon wata.
And they began on the first of the first month to hallow, and on the eighth day of the month they came to the porch of Jehovah; and they hallowed the house of Jehovah eight days; and on the sixteenth day of the first month they made an end.
18 Sa’an nan suka tafi wurin Sarki Hezekiya suka faɗa masa, “Mun tsarkake haikalin Ubangiji gaba ɗaya, bagaden ƙone hadaya tare da dukan kayayyakinsa, da tebur don shirya tsarkaken burodi, tare da dukan kayayyakinsa.
And they went in to king Hezekiah, and said, We have cleansed all the house of Jehovah, and the altar of burnt-offering with all its vessels, and the table of the [bread] to be set in rows, and all its vessels;
19 Mun shirya muka kuma tsarkake dukan kayayyakin da Sarki Ahaz ya cire cikin rashin amincinsa yayinda yake sarki. Yanzu suna a gaban bagaden Ubangiji.”
and all the vessels that king Ahaz in his reign cast away in his transgression have we prepared and hallowed, and behold, they are before the altar of Jehovah.
20 Da sassafe kashegari Sarki Hezekiya ya tattara manyan birni wuri ɗaya, suka haura zuwa haikalin Ubangiji.
And Hezekiah the king arose early, and gathered the princes of the city, and went up to the house of Jehovah.
21 Suka kawo bijimai bakwai, raguna bakwai, bunsurai bakwai da kuma awaki mata bakwai a matsayin hadaya don zunubi domin masarauta, domin wuri mai tsarki da kuma domin Yahuda. Sarki ya umarce firistoci, zuriyar Haruna, su miƙa waɗannan a bagaden Ubangiji.
And they brought seven bullocks, and seven rams, and seven lambs, and seven he-goats for a sin-offering for the kingdom, and for the sanctuary, and for Judah. And he commanded the priests the sons of Aaron to offer [them] upon the altar of Jehovah.
22 Saboda haka suka yayyanka bijiman, firistoci suka karɓi jinin suka yayyafa a kan bagade. Suka kuma yanka ragunan suka yayyafa jinin a bagaden. Haka kuma suka yanka’yan ragunan suka yayyafa jinin a bagaden.
And they slaughtered the bullocks, and the priests received the blood, and sprinkled it on the altar; and they slaughtered the rams, and sprinkled the blood on the altar; and they slaughtered the lambs, and sprinkled the blood on the altar.
23 Aka kawo awaki domin hadaya don zunubi a gaban sarki da taron, suka kuwa ɗibiya hannuwansu a kansu.
And they brought near the he-goats of the sin-offering before the king and the congregation; and they laid their hands upon them.
24 Sa’an nan firistoci suka yayyanka awakin suka miƙa jininsu a bagade domin hadaya don zunubi don kafara saboda dukan Isra’ila, domin sarki ya umarta a yi hadaya ta ƙonawa da hadaya don zunubi domin dukan Isra’ila.
And the priests slaughtered them, and they made purification for sin with their blood upon the altar, to make an atonement for all Israel; because for all Israel, said the king, is the burnt-offering and the sin-offering.
25 Sarki Hezekiya ya ajiye Lawiyawa a cikin haikalin Ubangiji tare da ganguna, garayu da molaye, yadda Dawuda da Gad mai duba na sarki da kuma annabi Natan suka tsara. Ubangiji ne ya umarta wannan ta wurin annabawansa.
And he set the Levites in the house of Jehovah with cymbals, with lutes, and with harps, according to the commandment of David, and of Gad the king's seer, and of Nathan the prophet; for the commandment was of Jehovah through his prophets.
26 Saboda haka Lawiyawa suka tsaya a shirye tare da kayan kiɗin Dawuda, firistoci kuma tare da ƙahoninsu.
And the Levites stood with the instruments of David, and the priests with the trumpets.
27 Hezekiya ya ba da umarni a miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagade. Yayinda aka fara miƙawa, ana rerawa ga Ubangiji, tare da bushe-bushe da kiɗe-kiɗen kayan waƙa na Dawuda sarkin Isra’ila.
And Hezekiah commanded to offer up the burnt-offering on the altar. And at the moment the burnt-offering began, the song of Jehovah began, and the trumpets, accompanied by the instruments of David king of Israel.
28 Dukan taron suka durƙusa suka yi sujada, yayinda mawaƙa suke rerawa, ana kuma busa ƙahoni, dukan wannan ya ci gaba sai da aka gama miƙa hadaya ta ƙonawa.
And all the congregation worshipped, and the singers sang, and the trumpeters sounded, all [the time] until the burnt-offering was finished.
29 Sa’ad da aka gama miƙawa, sai sarki da mutanen da suke tare da shi suka durƙusa suka yi sujada.
And when they had ended offering the burnt-offering, the king and all that were present with him bowed themselves and worshipped.
30 Sarki Hezekiya da fadawansa suka umarci Lawiyawa su yabi Ubangiji da kalmomin Dawuda da na Asaf mai duba. Saboda haka suka rera yabai da murna, suka sunkuyar da kawunansu suka yi sujada.
And king Hezekiah and the princes commanded the Levites to sing praise to Jehovah with the words of David, and of Asaph the seer. And they sang praises with gladness, and bowed their heads and worshipped.
31 Sa’an nan Hezekiya ya ce, “Yanzu kun keɓe kanku ga Ubangiji. Ku zo ku kuma kawo hadayu da hadayun godiya zuwa ga haikalin Ubangiji.” Saboda haka taron suka kawo hadayu da hadayun godiya, da kuma dukan waɗanda suke da niyya suka kawo hadayun ƙonawa.
And Hezekiah answered and said, Now ye have consecrated yourselves to Jehovah, come near and bring sacrifices and thank-offerings into the house of the Lord. And the congregation brought in sacrifices and thank-offerings; and as many as were of a willing heart, burnt-offerings.
32 Yawan hadayun ƙonawan da taron suka kawo, bijimai saba’in ne, raguna ɗari da kuma bunsurai ɗari biyu, dukansu kuwa domin hadayun ƙonawa ga Ubangiji ne.
And the number of the burnt-offerings, which the congregation brought, was seventy bullocks, a hundred rams, two hundred lambs: all these were for a burnt-offering to Jehovah.
33 Dabbobin da aka tsarkake a matsayi hadayu sun kai bijimai ɗari shida da tumaki da kuma awaki dubu uku.
And the consecrated things were six hundred oxen and three thousand sheep.
34 Firistoci fa, suka kāsa sosai don fiɗan dukan dabbobin da za a miƙa don hadayun ƙonawa; saboda haka’yan’uwansu Lawiyawa suka taimake su har aka gama aiki kafin sauran firistoci su sami damar tsarkake kansu. Gama Lawiyawa sun fi firistoci himma wajen tsarkakewar kansu.
Only the priests were too few, and they could not flay all the burnt-offerings; therefore their brethren the Levites helped them, until the work was ended, and until the priests had hallowed themselves; for the Levites were more upright in heart to hallow themselves than the priests.
35 Aka kasance da hadayun ƙonawa a yalwace, tare da kitsen hadayun salama da hadayun sha da suke tafe da hadayun ƙonawa. Saboda haka aka sāke kafa hidimar haikalin Ubangiji.
And also the burnt-offerings were in abundance, with the fat of the peace-offerings, and with the drink-offerings for the burnt-offering. And the service of the house of Jehovah was set in order.
36 Hezekiya da dukan mutane suka yi farin ciki game da abin da Allah ya yi wa mutanensa, domin ya faru farat ɗaya.
And Hezekiah rejoiced, and all the people, that God had prepared the people; for the thing was done suddenly.

< 2 Tarihi 29 >